< Irmiya 1 >
1 Kalmomin Irmiya ɗan Hilkiya, ɗaya daga cikin firistoci a Anatot a yankin Benyamin.
These are the words of Jeremiah son of Hilkiah, one of the priests at Anathoth in the land of Benjamin.
2 Maganar Ubangiji ta zo gare shi a shekara ta goma sha uku ta sarautar Yosiya ɗan Amon sarkin Yahuda,
The word of Yahweh came to him in the days of Josiah son of Amon, king of Judah, in the thirteenth year of his reign.
3 da kuma a zamanin Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, har zuwa watan biyar na shekara goma sha ɗaya na Zedekiya ɗan Yosiya sarkin Yahuda, sa’ad da aka kai mutanen Urushalima zaman bauta.
It also came in the days of Jehoiakim son of Josiah, king of Judah, until the fifth month of the eleventh year of Zedekiah son of Josiah, king of Judah, when the people of Jerusalem were taken away as prisoners.
4 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
The word of Yahweh came to me, saying,
5 “Kafin in siffanta ka a cikin ciki na san ka, kafin a haife ka, na keɓe ka; na naɗa ka ka zama annabi ga al’ummai.”
“Before I formed you in the womb, I chose you; before you came out from the womb I set you apart; I made you a prophet to the nations.”
6 Sai na ce, “Kayya, Ubangiji Mai Iko Duka, ban iya magana ba; ni ɗan yaro ne kawai.”
“Ah, Lord Yahweh!” I said, “I do not know how to speak, for I am too young.”
7 Amma Ubangiji ya ce mini, “Kada ka ce, ‘Ni ɗan yaro ne kawai.’ Dole ka je wurin kowane mutumin da na aike ka ka kuma faɗa abin da na umarce ka.
But Yahweh said to me, “Do not say, 'I am too young.' You must go everywhere I send you, and you must say whatever I command you!
8 Kada ka ji tsoronsu, gama ina tare da kai kuma zan kiyaye ka,” in ji Ubangiji.
Do not be afraid of them, for I am with you to rescue you—this is Yahweh's declaration.”
9 Sai Ubangiji ya miƙa hannunsa ya taɓa bakina ya ce mini, “Yanzu na sa kalmomina a bakinka.
Then Yahweh reached out with his hand, touched my mouth, and said to me, “Now, I have placed my word in your mouth.
10 Duba, yau na naɗa ka a kan al’ummai da mulkoki don ka tumɓuke ka kuma rusar, ka hallaka ka kuma kakkaɓe, ka gina ka kuma shuka.”
I am appointing you today over nations and over kingdoms, to uproot and break down, to destroy and overthrow, to build and plant.”
11 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa, “Me ka gani, Irmiya?” Sai na amsa na ce, “Na ga reshen itacen almon.”
The word of Yahweh came to me, saying, “What do you see, Jeremiah?” I said, “I see an almond branch.”
12 Ubangiji ya ce mini, “Daidai ne ka gani, gama ina lura in ga cewa maganata ta cika.”
Yahweh said to me, “You have seen well, for I am watching over my word to carry it out.”
13 Maganar Ubangiji ta sāke zo mini cewa, “Me ka gani?” Na amsa na ce, “Na ga tukunya tana tafasa, tana juyewa daga arewa.”
The word of Yahweh came to me a second time, saying, “What do you see?” I said, “I see a heated pot, whose surface is churning, tipping away from the north.”
14 Ubangiji ya ce mini, “Daga arewa za a zubo masifa a kan dukan mazaunan ƙasar.
Yahweh said to me, “Disaster will be opened up out of the north on all who live in this land.
15 Ina shirin kiran dukan mutanen masarautar arewanci,” in ji Ubangiji. “Sarakunansu za su zo su kafa kursiyoyinsu a mashigin ƙofofin Urushalima; za su zo su kewaye dukan katangarta su kewaye dukan garuruwan Yahuda.
For I am calling all the tribes of the northern kingdoms, declares Yahweh. They will come, and everyone will set his throne at the entrance of the gates of Jerusalem, against all the walls that surround it, and against all the cities of Judah.
16 Zan furta hukunci a kan mutanena saboda muguntarsu na yashe ni, suna ƙona turare ga waɗansu alloli suna kuma bauta wa abin da hannuwansu suka yi.
I will pronounce sentence against them for all their evil in forsaking me, in burning incense to other gods, and in worshiping what they made with their own hands.
17 “Ka kintsa kanka! Ka tashi tsaye ka faɗa musu abin da na umarce ka. Kada su firgita ka, in ba haka ba zan firgita ka a gabansu.
Get yourself ready! Stand up and say to them whatever I command you. Do not be shattered before them, or I will shatter you before them!
18 Yau na mai da kai birni mai katanga, ginshiƙin ƙarfe da bangon tagulla don ka tsaya gāba da dukan ƙasar, ya kuma yi gāba da sarakunan Yahuda da fadawan, da firistoci da kuma mutanenta.
Behold! Today I have made you a fortified city, an iron pillar, and bronze walls against the whole land—against the kings of Judah, its officials, its priests, and the people of the land.
19 Za su yi yaƙi da kai amma ba za su ci nasara a kanka ba, gama ina tare da kai, zan kuma kiyaye ka,” in ji Ubangiji.
They will fight against you, but they will not defeat you, for I will be with you to rescue you—this is Yahweh's declaration.”