< Irmiya 1 >

1 Kalmomin Irmiya ɗan Hilkiya, ɗaya daga cikin firistoci a Anatot a yankin Benyamin.
The words of Jeremiah, the son of Hilkiah, one of the priests, who dwelt in Anathoth in the land of Benjamin;
2 Maganar Ubangiji ta zo gare shi a shekara ta goma sha uku ta sarautar Yosiya ɗan Amon sarkin Yahuda,
to whom the word of Jehovah came in the days of Josiah, the son of Amon, king of Judah, in the thirteenth year of his reign;
3 da kuma a zamanin Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, har zuwa watan biyar na shekara goma sha ɗaya na Zedekiya ɗan Yosiya sarkin Yahuda, sa’ad da aka kai mutanen Urushalima zaman bauta.
to whom it also came in the days of Jehoiakim, the son of Josiah, king of Judah, until the end of the eleventh year of Zedekiah, the son of Josiah, king of Judah, until the carrying away of Jerusalem into captivity in the fifth month.
4 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
The word of Jehovah came to me, saying:
5 “Kafin in siffanta ka a cikin ciki na san ka, kafin a haife ka, na keɓe ka; na naɗa ka ka zama annabi ga al’ummai.”
Before I formed thee in the womb, I knew thee; and before thou camest into the world, I chose thee; I appointed thee to be a prophet to the nations.
6 Sai na ce, “Kayya, Ubangiji Mai Iko Duka, ban iya magana ba; ni ɗan yaro ne kawai.”
Then said I, Alas, O Lord Jehovah! Behold, I am not able to speak; for I am a child.
7 Amma Ubangiji ya ce mini, “Kada ka ce, ‘Ni ɗan yaro ne kawai.’ Dole ka je wurin kowane mutumin da na aike ka ka kuma faɗa abin da na umarce ka.
But Jehovah said to me, Say not, I am a child; but go to whomever I send thee, and speak whatever I command thee!
8 Kada ka ji tsoronsu, gama ina tare da kai kuma zan kiyaye ka,” in ji Ubangiji.
Be not afraid of them! For I am with thee to help thee, saith Jehovah.
9 Sai Ubangiji ya miƙa hannunsa ya taɓa bakina ya ce mini, “Yanzu na sa kalmomina a bakinka.
Then Jehovah put forth his hand, and touched my mouth. Jehovah also said to me, Behold, I have put my words in thy mouth.
10 Duba, yau na naɗa ka a kan al’ummai da mulkoki don ka tumɓuke ka kuma rusar, ka hallaka ka kuma kakkaɓe, ka gina ka kuma shuka.”
Behold, I have set thee this day over nations and over kingdoms, to root out, and to pull down, and to destroy, and to overthrow; and to build, and to plant.
11 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa, “Me ka gani, Irmiya?” Sai na amsa na ce, “Na ga reshen itacen almon.”
Then the word of Jehovah came to me, saying, What seest thou, Jeremiah? And I said, I see a rod of almond-wood.
12 Ubangiji ya ce mini, “Daidai ne ka gani, gama ina lura in ga cewa maganata ta cika.”
And Jehovah said to me, Thou hast seen right; for I am watchful over my word to perform it.
13 Maganar Ubangiji ta sāke zo mini cewa, “Me ka gani?” Na amsa na ce, “Na ga tukunya tana tafasa, tana juyewa daga arewa.”
And the word of Jehovah came to me a second time, saying, What seest thou? And I said, I see a boiling pot, whose face is turned from the north.
14 Ubangiji ya ce mini, “Daga arewa za a zubo masifa a kan dukan mazaunan ƙasar.
And Jehovah said to me, From the north shall evil break forth upon all the inhabitants of the land.
15 Ina shirin kiran dukan mutanen masarautar arewanci,” in ji Ubangiji. “Sarakunansu za su zo su kafa kursiyoyinsu a mashigin ƙofofin Urushalima; za su zo su kewaye dukan katangarta su kewaye dukan garuruwan Yahuda.
For, behold, I will call all the tribes of the kingdoms of the north, saith Jehovah; and they shall come, and shall set every one his throne at the entrance of the gates of Jerusalem, and against all her walls around, and against all the cities of Judah.
16 Zan furta hukunci a kan mutanena saboda muguntarsu na yashe ni, suna ƙona turare ga waɗansu alloli suna kuma bauta wa abin da hannuwansu suka yi.
And I will pronounce my judgments against them for all their wickedness, in that they have forsaken me, and have burned incense to other gods, and worshipped the work of their own hands.
17 “Ka kintsa kanka! Ka tashi tsaye ka faɗa musu abin da na umarce ka. Kada su firgita ka, in ba haka ba zan firgita ka a gabansu.
Thou, therefore, gird up thy loins, and arise, and speak to them all that I command thee; be not afraid of them, lest I confound thee before them.
18 Yau na mai da kai birni mai katanga, ginshiƙin ƙarfe da bangon tagulla don ka tsaya gāba da dukan ƙasar, ya kuma yi gāba da sarakunan Yahuda da fadawan, da firistoci da kuma mutanenta.
For, behold, I make thee this day a fortified city, and a pillar of iron, and a wall of brass against all this land, against the kings of Judah, against the princes thereof, against the priests thereof, and against the people of the land.
19 Za su yi yaƙi da kai amma ba za su ci nasara a kanka ba, gama ina tare da kai, zan kuma kiyaye ka,” in ji Ubangiji.
They shall fight against thee, but they shall not prevail against thee; for I will be with thee, saith Jehovah, to help thee.

< Irmiya 1 >