< Irmiya 1 >

1 Kalmomin Irmiya ɗan Hilkiya, ɗaya daga cikin firistoci a Anatot a yankin Benyamin.
The words of Jeremiah, the son of Hilkiah of the priests who were in Anathoth in the land of Benjamin.
2 Maganar Ubangiji ta zo gare shi a shekara ta goma sha uku ta sarautar Yosiya ɗan Amon sarkin Yahuda,
The word of the Lord, which came to him in the days of Josiah, the son of Amon, king of Judah, in the thirteenth year of his reign,
3 da kuma a zamanin Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, har zuwa watan biyar na shekara goma sha ɗaya na Zedekiya ɗan Yosiya sarkin Yahuda, sa’ad da aka kai mutanen Urushalima zaman bauta.
and which came to him in the days of Jehoiakim, the son of Josiah, king of Judah, even until the completion of the eleventh year of Zedekiah, the son of Josiah, king of Judah, even until the transmigration of Jerusalem in the fifth month.
4 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And the word of the Lord came to me, saying:
5 “Kafin in siffanta ka a cikin ciki na san ka, kafin a haife ka, na keɓe ka; na naɗa ka ka zama annabi ga al’ummai.”
“Before I formed you in the womb, I knew you. And before you went forth from the womb, I sanctified you. And I made you a prophet to the nations.”
6 Sai na ce, “Kayya, Ubangiji Mai Iko Duka, ban iya magana ba; ni ɗan yaro ne kawai.”
And I said: “Alas, alas, alas, Lord God! Behold, I do not know how to speak, for I am a boy.”
7 Amma Ubangiji ya ce mini, “Kada ka ce, ‘Ni ɗan yaro ne kawai.’ Dole ka je wurin kowane mutumin da na aike ka ka kuma faɗa abin da na umarce ka.
And the Lord said to me: “Do not choose to say, ‘I am a boy.’ For you shall go forth to everyone to whom I will send you. And you shall speak all that I will command you.
8 Kada ka ji tsoronsu, gama ina tare da kai kuma zan kiyaye ka,” in ji Ubangiji.
You should not be afraid before their face. For I am with you, so that I may deliver you,” says the Lord.
9 Sai Ubangiji ya miƙa hannunsa ya taɓa bakina ya ce mini, “Yanzu na sa kalmomina a bakinka.
And the Lord put forth his hand, and he touched my mouth. And the Lord said to me: “Behold, I have placed my words in your mouth.
10 Duba, yau na naɗa ka a kan al’ummai da mulkoki don ka tumɓuke ka kuma rusar, ka hallaka ka kuma kakkaɓe, ka gina ka kuma shuka.”
Behold, today I have appointed you over nations and over kingdoms, so that you may root up, and pull down, and destroy, and scatter, and so that you may build and plant.”
11 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa, “Me ka gani, Irmiya?” Sai na amsa na ce, “Na ga reshen itacen almon.”
And the word of the Lord came to me, saying, “What do you see, Jeremiah?” And I said, “I see a staff, keeping watch.”
12 Ubangiji ya ce mini, “Daidai ne ka gani, gama ina lura in ga cewa maganata ta cika.”
And the Lord said to me: “You have seen well. For I will keep watch over my word, so that I may accomplish it.”
13 Maganar Ubangiji ta sāke zo mini cewa, “Me ka gani?” Na amsa na ce, “Na ga tukunya tana tafasa, tana juyewa daga arewa.”
And the word of the Lord came to me a second time, saying, “What do you see?” And I said, “I see a cooking pot upon a fire, and its face is before the face of the north.”
14 Ubangiji ya ce mini, “Daga arewa za a zubo masifa a kan dukan mazaunan ƙasar.
And the Lord said to me: “From the north, an evil will spread over all the inhabitants of the earth.
15 Ina shirin kiran dukan mutanen masarautar arewanci,” in ji Ubangiji. “Sarakunansu za su zo su kafa kursiyoyinsu a mashigin ƙofofin Urushalima; za su zo su kewaye dukan katangarta su kewaye dukan garuruwan Yahuda.
For behold, I will call together all the close associates of the kingdoms of the north, says the Lord. And they will arrive, and each one of them will place his throne at the entrance to the gates of Jerusalem, and over all its surrounding walls, and over all the cities of Judah.
16 Zan furta hukunci a kan mutanena saboda muguntarsu na yashe ni, suna ƙona turare ga waɗansu alloli suna kuma bauta wa abin da hannuwansu suka yi.
And I will speak my judgments with them, concerning all the wickedness of those who have forsaken me, and who have offered libations to strange gods, and who have adored the work of their own hands.
17 “Ka kintsa kanka! Ka tashi tsaye ka faɗa musu abin da na umarce ka. Kada su firgita ka, in ba haka ba zan firgita ka a gabansu.
Therefore, you should gird your waist, and rise up, and speak to them everything that I instruct you. You should not have dread before their face. For I will cause you to be unafraid of their countenance.
18 Yau na mai da kai birni mai katanga, ginshiƙin ƙarfe da bangon tagulla don ka tsaya gāba da dukan ƙasar, ya kuma yi gāba da sarakunan Yahuda da fadawan, da firistoci da kuma mutanenta.
For certainly, this day, I have made you like a fortified city, and an iron pillar, and a brass wall, over all the land, to the kings of Judah, to its leaders, and to the priests, and to the people of the land.
19 Za su yi yaƙi da kai amma ba za su ci nasara a kanka ba, gama ina tare da kai, zan kuma kiyaye ka,” in ji Ubangiji.
And they will make war against you, but they will not prevail. For I am with you, says the Lord, so that I may free you.”

< Irmiya 1 >