< Yaƙub 1 >
1 Yaƙub, bawan Allah da kuma na Ubangiji Yesu Kiristi, Zuwa ga kabilan nan goma sha biyu, da suke warwartse a cikin al’ummai. Gaisuwa mai yawa.
UJakobe, inceku kaNkulunkulu leyeNkosi uJesu Kristu, kuzo izizwe ezilitshumi lambili ezisekuhlakazekeni, ngiyabingelela.
2 Ku ɗauki wannan da farin ciki mai tsabta,’yan’uwana, duk sa’ad da gwaje-gwaje na kowane iri suka zo muku,
Kubaleni ukuthi kuyintokozo yonke, bazalwane bami, nxa liwela ezilingweni ezizinhlobonhlobo,
3 domin kun san cewa gwajin bangaskiyarku yakan haifi daurewa.
lisazi ukuthi ukuhlolwa kokholo lwenu kuveza ukubekezela;
4 Dole daurewa ta kammala aikinta don ku zama balagaggu da kuma cikakku, ba ku kuma rasa kome ba.
kodwa ukubekezela kakube lomsebenzi opheleleyo, ukuze libe ngabapheleleyo liphelelisiwe, lingasileli ngalutho.
5 In waninku ya rasa hikima, ya kamata yă roƙi Allah, mai bayarwa hannu sake ga kowa ba tare da gori ba, za a kuwa ba shi.
Njalo uba kukhona kini oswele inhlakanipho, kacele kuNkulunkulu ophanayo ngesihle kubo bonke, futhi engasoli, njalo uzayinikwa.
6 Amma sa’ad da ya roƙa, dole yă gaskata, ba tare da shakka ba, domin shi mai shakka, yana kama da raƙumar ruwan tekun da iska take kori tana kuma ɓuɓɓugowa.
Kodwa kacele ekholweni engathandabuzi ngalutho; ngoba othandabuzayo unjengegagasi lolwandle eliqhutshwa ngumoya lizuliswe.
7 Kada irin wannan mutum yă yi tsammani zai sami wani abu daga Ubangiji;
Ngoba lowomuntu kangacabangi ukuthi uzazuza ulutho eNkosini.
8 shi mai zuciya biyu ne, marar tsai da zuciyarsa wuri ɗaya a cikin duk abin da yake yi.
Indoda enhliziyombili iyaphenduphenduka endleleni zayo zonke.
9 Bari ɗan’uwan da yake cikin halin ƙasƙanci yă yi taƙama a matsayinsa na ɗaukaka.
Lomzalwane ophansi kazincome ekuphakameni kwakhe;
10 Amma wanda yake mai arziki, ya kamata yă yi taƙama a matsayinsa na ƙasƙanci, gama ba zai daɗe ba kamar furen jeji.
kodwa onothileyo ekuthotshisweni kwakhe; ngoba njengeluba lotshani uzadlula.
11 Gama in rana ta fito ta yi zafi mai tsanani sai ta sa tsiro yă yanƙwane tsiro; furensa yă kakkaɓe, kyansa kuma yă lalace. Haka ma mai arziki zai shuɗe yayinda yake cikin harkarsa.
Ngoba ilanga liphuma lilokutshisa, libunise utshani, leluba labo liwohloke, lobuhle bokubonakala kwalo bunyamalale; ngokunjalo lesinothi sizanyamalala ezindleleni zaso.
12 Mai albarka ne mutumin da yake daurewa cikin gwaji, gama bayan ya yi nasara da gwajin, zai sami rawanin rai wanda Allah ya yi alkawari ga waɗanda suke ƙaunarsa.
Ubusisiwe umuntu obekezelela isilingo; ngoba esehloliwe uzakwemukela umqhele wempilo, iNkosi eyawuthembisa kwabayithandayo.
13 Sa’ad da aka jarrabci mutum, kada yă ce, “Allah ne yake jarrabtarsa.” Gama ba ya yiwuwa a jarrabci Allah da mugunta, shi kuma ba ya jarrabtar kowa;
Kakulamuntu olingwayo omele athi: Ngilingwa nguNkulunkulu; ngoba uNkulunkulu kalasilingo sokubi, laye uqobo kalingi muntu.
14 amma akan jarrabce kowane mutum sa’ad da muguwar sha’awarsa ta janye shi ta kuma rinjaye shi.
Kodwa ngulowo lalowo uyalingwa, lapho eyengwa ngezakhe inkanuko, ehugwa;
15 Sa’an nan, bayan da sha’awar ta yi ciki, takan haifi zunubi; zunubi kuwa, sa’ad da ya balaga yakan haifi mutuwa.
kuthi lapho inkanuko isikhulelwe ibelethe isono; lesono lapho sesiphelele sizala ukufa.
16 Kada a ruɗe ku,’yan’uwana ƙaunatattu.
Lingakhohliswa, bazalwane bami abathandekayo.
17 Kowane abu mai kyau da kuma kowace cikakkiyar kyauta daga sama suke, sun sauko ne daga wurin Uban haskoki, wanda ba sauyawa ko wata alamar sākewa a gare shi faufau.
Sonke isipho esihle laso sonke isipho esipheleleyo sivela phezulu, sehla sivela kuYise wezibane, okungekho kuye ukuguquka, kumbe isithunzi sokuphenduka.
18 Ya zaɓa yă haife mu ta wurin kalmar gaskiya, domin mu zama’ya’yan fari na dukan abin da ya halitta.
Ngokuthanda kwakhe wasizala ngelizwi leqiniso, ukuze sibe njengezithelo zokuqala zezidalwa zakhe.
19 ’Yan’uwana ƙaunatattu, ku lura da wannan. Ya kamata kowa yă kasance mai saurin saurara, ba mai saurin magana ba, ba kuma mai saurin fushi ba,
Ngakho, bazalwane bami abathandekayo, wonke umuntu umele aphangise ukuzwa, aphuze ukukhuluma, aphuze ukuthukuthela;
20 gama fushin mutum ba ya kawo rayuwar adalcin da Allah yake so.
ngoba ukuthukuthela kwendoda kakwenzi ukulunga kukaNkulunkulu.
21 Saboda haka, ku rabu da ƙazamin hali da kuma kowace irin mugunta ku kuma yi na’am da maganar da aka shuka a cikinku da tawali’u, wadda za tă iya cetonku.
Ngakho selihlubule amanyala wonke lokwanda kakhulu kobubi, lemukele ngobumnene ilizwi eligxunyekiweyo, elilamandla okusindisa imiphefumulo yenu.
22 Kada ku zama masu ji kawai, ku ruɗi kanku. A maimakon haka ku zama masu yin abin da ta ce.
Kodwa banini ngabenzi belizwi, lingabi ngabezwayo kuphela, lizikhohlisa lina ngokwenu.
23 Duk wanda yake ji magana ne kawai, bai kuwa aikata abin da ta ce ba, yana kama da mutumin da ya kalli fuskarsa a madubi
Ngoba uba umuntu engumuzwi welizwi futhi engesimenzi, yena ufanana lendoda ebuka ubuso bayo bemvelo esibukweni;
24 bayan ya kalli kansa, sa’ad da ya tashi daga wurin, nan da nan sai yă manta da kamanninsa.
ngoba iyazibuka, ibisisuka, ibisihle ikhohlwa ukuthi ibinjani.
25 Amma duk mai duba cikakkiyar ƙa’idan nan ta’yanci, ya kuma nace a kanta, ya zama ba mai ji ne kawai yă mance ba, sai dai mai yi ne yă zartar, to wannan shi za a yi wa albarka a cikin abin da yake yi.
Kodwa lowo okhangelisisa emlayweni opheleleyo, lowo owenkululeko, abesebambelela kuwo, yena engesimuzwi okhohlwayo kodwa engumenzi womsebenzi, lo uzakuba ngobusisiweyo ekwenzeni kwakhe.
26 In wani ya ɗauki kansa mai addini ne duk da haka bai ƙame harshensa ba, ruɗin kansa yake yi addininsa kuwa banza ne.
Uba umuntu phakathi kwenu esithi uyakholwa, uba engalufaki itomu ulimi lwakhe, kodwa akhohlise inhliziyo yakhe, ukukholwa kwalowo kuyize.
27 Addinin da Allah Ubanmu ya yarda da shi a matsayin mai tsabta da kuma marar aibi shi ne, a kula da marayu da gwauraye cikin damuwoyinsu, a kuma kiyaye kai daga lalacin da duniya take sa wa.
Ukukholwa okuhlanzekileyo lokungangcoliswanga phambi kukaNkulunkulu ngitsho uBaba yilokhu, ukuhambela izintandane labafelokazi ekuhluphekeni kwabo, lokuzilondoloza engelasici kokomhlaba.