< Yaƙub 5 >

1 Yanzu fa sai ku saurara, ku masu arziki, ku yi kuka da ihu, saboda azabar da take zuwa a kanku.
Dejte torej, bogatini, jokajte javkajoč o bedah, katere vam pridejo;
2 Arzikinku ya ruɓa, asu kuma sun cinye tufafinku.
Bogastvo vaše je iztrohnelo, in oblačila vaša so moli snedli;
3 Zinariyarku da azurfarku sun yi tsatsa. Tsatsarsu kuwa za tă zama shaida a kanku, ta kuma ci namar jikinku kamar wuta. Kun ɓoye dukiya a kwanakin ƙarshe.
Zlato vaše in srebro je zrujavelo, in njih ruja bode v pričanje vam, in žrla meso vaše kakor ogenj; zaklade ste zbirali v zadnjih dnevih.
4 Ga shi! Zaluncin da kuka yi na hakkin ma’aikatan gonakinku yana ta ƙara. Kukan masu girbi ya kai kunnuwan Ubangiji Maɗaukaki.
Glej, plačilo delalcev, kateri so kosili polja vaša, ki ste ga jim utrgali, kriči; in vpitje ženjic prišlo je do ušes Gospoda Sabaot.
5 Kun yi rayuwar jin daɗi a duniya kuna ci kuna sha na ganin dama. Kun ciyar da kanku kun yi ƙiba don ranar yanka.
V požréšnosti ste na zemlji živeli in razkošnosti; srca svoja ste redili kakor o dnevi klanja.
6 Kun hukunta kun kuma kashe mutane marasa laifi, waɗanda ba su yi gāba da ku ba.
Obsodili, ubili ste pravičnega; ne ustavlja se vam!
7 Saboda haka’yan’uwa, sai ku yi haƙuri har dawowar Ubangiji. Ku dubi yadda manomi yakan jira gona ta ba da amfaninta mai kyau, da kuma yadda yake haƙurin jiran ruwan sama na damina da na kaka.
Bodite torej potrpežljivi, bratje, do prihoda Gospodovega. Glej, ratar pričakuje drazega sadú zemljé, potrpežljiv zanj, da dobi dež zgodnji in kasni;
8 Haka ku ma, ku yi haƙuri, ku tsaya da ƙarfi, gama dawowar Ubangiji ya yi kusa.
Bodite potrpežljivi tudi vi, pokrepčajte srca svoja, ker prihod Gospodov se je približal.
9 ’Yan’uwa, kada ku yi gunaguni da juna, don kada a hukunta ku. Alƙalin yana tsaye a bakin ƙofa!
Ne zdihujte drug zoper druzega, bratje, da ne bodete obsojeni; glej, sodnik stoji pred vrati!
10 ’Yan’uwa, ku ɗauki annabawa da suka yi magana a cikin sunan Ubangiji, a matsayin gurbi na haƙuri a cikin shan wahala.
Za zgled vzemite trpljenja in potrpežljivosti, bratje, preroke, kateri so govorili v imenu Gospodovem.
11 Kamar yadda kuka sani, mukan ce da waɗanda suka jure, masu albarka ne. Kun ji daurewar Ayuba, kuka kuma ga abin da Ubangiji ya yi a ƙarshe. Ubangiji yana cike da tausayi da jinƙai.
Glej, blagrujemo stanovitne; o stanovitnosti Jobovi ste čuli, in konec Gospodov ste videli; ker usmiljen je Gospod in milosrčen.
12 ’Yan’uwana, fiye da kome, kada ku yi rantsuwa ko da sama, ko da ƙasa ko da wani abu dabam. Bari “I” naku yă zama “I”. “A’a” naku kuma yă zama “A’a”, don kada a hukunta ku.
Pred vsem pa, bratje moji, ne prisezajte; ne pri nebu, ne pri zemlji, ne kake druge prisege; bodi pa vaše; dá, dá, in ne, ne! da ne padete pod sodbo.
13 Akwai waninku da yake shan wahala? Ya kamata yă yi addu’a. Akwai wani mai murna? Sai yă rera waƙoƙin yabo.
Trpi li kdo med vami? moli naj; je li kdo dobre volje? prepeva naj.
14 Akwai waninku da yake ciwo? Ya kamata yă kira dattawan ikkilisiya su yi masa addu’a, su kuma shafa masa mai cikin sunan Ubangiji.
Je-li kdo bolan med vami? pokliče naj k sebi starejšine občine, in molijo naj nad njim, ter pomazilijo ga z oljem v imenu Gospodovem;
15 Addu’ar da aka yi cikin bangaskiya, za tă warkar da marar lafiya, Ubangiji zai tashe shi. In ya yi zunubi kuwa za a gafarta masa.
In molitev vere bode pomagala bolniku, in ozdravil ga bode Gospod; in ako je storil grehe, odpustilo se mu bode.
16 Saboda haka, ku furta wa juna zunubanku, ku yi addu’a saboda juna, domin ku sami warkarwa. Addu’ar mai adalci tana da iko da kuma amfani.
Izpovedujte si med seboj grehe, in molite zase med seboj, da bodete ozdravljeni! Mnogo more krepka molitev pravičnega.
17 Iliya mutum ne kamar mu. Ya yi addu’a da gaske don kada a yi ruwan sama, ba a kuma yi ruwan sama a ƙasar ba har shekaru uku da rabi.
Elija je bil človek enakočuten z nami in v molitvi je molil, naj ne dežuje, in deževalo ni na zemlji tri leta in mesece tri;
18 Ya sāke yin addu’a, sai sammai suka ba da ruwan sama, ƙasa kuma ta ba da amfaninta.
In zopet je molil, in nebo je dalo dežja, in zemlja je rodila sad svoj.
19 ’Yan’uwana, in waninku ya kauce daga gaskiya, wani kuma ya komo da shi,
Bratje, ako kdo med vami zabrede od resnice in ga kdo nazaj pripelje,
20 sai yă tuna da wannan. Duk wanda ya komo da mai zunubi daga kaucewarsa, zai cece shi daga mutuwa, yă kuma rufe zunubai masu ɗumbun yawa.
Vedi, da kdor nazaj pripelje grešnika s krive poti, rešil bode dušo njegovo smrti, in pokril grehov obilost.

< Yaƙub 5 >