< Yaƙub 5 >
1 Yanzu fa sai ku saurara, ku masu arziki, ku yi kuka da ihu, saboda azabar da take zuwa a kanku.
Come now, you who are rich, weep and howl over the miseries that are coming upon you.
2 Arzikinku ya ruɓa, asu kuma sun cinye tufafinku.
Your riches have rotted, and your garments are moth-eaten.
3 Zinariyarku da azurfarku sun yi tsatsa. Tsatsarsu kuwa za tă zama shaida a kanku, ta kuma ci namar jikinku kamar wuta. Kun ɓoye dukiya a kwanakin ƙarshe.
Your gold and silver have rusted, and their rust will be a testimony against you and will eat your flesh like fire. You have laid up treasure in the last days.
4 Ga shi! Zaluncin da kuka yi na hakkin ma’aikatan gonakinku yana ta ƙara. Kukan masu girbi ya kai kunnuwan Ubangiji Maɗaukaki.
Behold, the wages of the workers who harvested your fields, which you kept back by fraud, cry out, and the cries of the reapers have reached the ears of the Lord of hosts.
5 Kun yi rayuwar jin daɗi a duniya kuna ci kuna sha na ganin dama. Kun ciyar da kanku kun yi ƙiba don ranar yanka.
You have lived on the earth in luxury and self-indulgence. You have nourished your hearts as in a day of slaughter.
6 Kun hukunta kun kuma kashe mutane marasa laifi, waɗanda ba su yi gāba da ku ba.
You have condemned and murdered the righteous man; he does not resist you.
7 Saboda haka’yan’uwa, sai ku yi haƙuri har dawowar Ubangiji. Ku dubi yadda manomi yakan jira gona ta ba da amfaninta mai kyau, da kuma yadda yake haƙurin jiran ruwan sama na damina da na kaka.
Therefore be patient, brothers, until the coming of the Lord. Behold, the farmer waits for the precious fruit of the earth, being patient for it until it receives the early and latter rain.
8 Haka ku ma, ku yi haƙuri, ku tsaya da ƙarfi, gama dawowar Ubangiji ya yi kusa.
You also must be patient. Establish your hearts, for the coming of the Lord has drawn near.
9 ’Yan’uwa, kada ku yi gunaguni da juna, don kada a hukunta ku. Alƙalin yana tsaye a bakin ƙofa!
Do not complain against one another, brothers, so that you will not be judged. Behold, the Judge is standing at the door.
10 ’Yan’uwa, ku ɗauki annabawa da suka yi magana a cikin sunan Ubangiji, a matsayin gurbi na haƙuri a cikin shan wahala.
As an example of suffering and patience, my brothers, take the prophets who spoke in the name of the Lord.
11 Kamar yadda kuka sani, mukan ce da waɗanda suka jure, masu albarka ne. Kun ji daurewar Ayuba, kuka kuma ga abin da Ubangiji ya yi a ƙarshe. Ubangiji yana cike da tausayi da jinƙai.
Behold, we regard as blessed those who endure. You have heard of the endurance of Job. Now consider the purpose of the Lord, how he is full of compassion and mercy.
12 ’Yan’uwana, fiye da kome, kada ku yi rantsuwa ko da sama, ko da ƙasa ko da wani abu dabam. Bari “I” naku yă zama “I”. “A’a” naku kuma yă zama “A’a”, don kada a hukunta ku.
Above all, my brothers, do not swear, neither by heaven, nor by earth, nor by any other oath. But let your “Yes” be “Yes” and your “No” be “No,” so that you will not fall into hypocrisy.
13 Akwai waninku da yake shan wahala? Ya kamata yă yi addu’a. Akwai wani mai murna? Sai yă rera waƙoƙin yabo.
Is anyone among you suffering? He should pray. Is anyone of good cheer? He should sing praise.
14 Akwai waninku da yake ciwo? Ya kamata yă kira dattawan ikkilisiya su yi masa addu’a, su kuma shafa masa mai cikin sunan Ubangiji.
Is anyone among you sick? He should call for the elders of the church, and they should pray over him, anointing him with oil in the name of the Lord.
15 Addu’ar da aka yi cikin bangaskiya, za tă warkar da marar lafiya, Ubangiji zai tashe shi. In ya yi zunubi kuwa za a gafarta masa.
The prayer of faith will save the one who is sick, and the Lord will raise him up. And if he has committed sins, he will be forgiven.
16 Saboda haka, ku furta wa juna zunubanku, ku yi addu’a saboda juna, domin ku sami warkarwa. Addu’ar mai adalci tana da iko da kuma amfani.
Confess your trespasses to one another and pray for one another so that you may be healed. The prayer of a righteous person is very powerful and effective.
17 Iliya mutum ne kamar mu. Ya yi addu’a da gaske don kada a yi ruwan sama, ba a kuma yi ruwan sama a ƙasar ba har shekaru uku da rabi.
Elijah was a man with a nature like ours, and he prayed earnestly that it would not rain, and for three years and six months it did not rain on the land.
18 Ya sāke yin addu’a, sai sammai suka ba da ruwan sama, ƙasa kuma ta ba da amfaninta.
Then he prayed again, and the sky gave rain, and the land produced its fruit.
19 ’Yan’uwana, in waninku ya kauce daga gaskiya, wani kuma ya komo da shi,
Brothers, if anyone among you wanders from the truth and someone turns him back,
20 sai yă tuna da wannan. Duk wanda ya komo da mai zunubi daga kaucewarsa, zai cece shi daga mutuwa, yă kuma rufe zunubai masu ɗumbun yawa.
be assured that whoever turns a sinner back from the error of his way will save a soul from death and cover a multitude of sins.