< Yaƙub 5 >

1 Yanzu fa sai ku saurara, ku masu arziki, ku yi kuka da ihu, saboda azabar da take zuwa a kanku.
Come, now, you rich men, weep, howl, on account of your miseries, which are coming upon you.
2 Arzikinku ya ruɓa, asu kuma sun cinye tufafinku.
Your riches are putrefied, and your garments are motheaten.
3 Zinariyarku da azurfarku sun yi tsatsa. Tsatsarsu kuwa za tă zama shaida a kanku, ta kuma ci namar jikinku kamar wuta. Kun ɓoye dukiya a kwanakin ƙarshe.
Your gold and silver are eaten with rust, and the rust of them will be a witness against you, and will eat your flesh as fire. You have heaped up treasure in the last days.
4 Ga shi! Zaluncin da kuka yi na hakkin ma’aikatan gonakinku yana ta ƙara. Kukan masu girbi ya kai kunnuwan Ubangiji Maɗaukaki.
Hark! the hire of the laborers who have reaped your field, which is fraudulently kept back by you, cries; and the cries of the reapers have entered into the ears of the Lord of hosts.
5 Kun yi rayuwar jin daɗi a duniya kuna ci kuna sha na ganin dama. Kun ciyar da kanku kun yi ƙiba don ranar yanka.
You have lived luxuriously on the earth, and been wanton; you have nourished your hearts as in a day of festivity.
6 Kun hukunta kun kuma kashe mutane marasa laifi, waɗanda ba su yi gāba da ku ba.
You have condemned--you have killed the Just One--he did not resist you.
7 Saboda haka’yan’uwa, sai ku yi haƙuri har dawowar Ubangiji. Ku dubi yadda manomi yakan jira gona ta ba da amfaninta mai kyau, da kuma yadda yake haƙurin jiran ruwan sama na damina da na kaka.
Behold the husbandman, who expects the valuable fruit of the earth, waits patiently for it, till it receive the early and later rain.
8 Haka ku ma, ku yi haƙuri, ku tsaya da ƙarfi, gama dawowar Ubangiji ya yi kusa.
Be you also patient--strengthen your hearts: for the coming of the Lord draws nigh.
9 ’Yan’uwa, kada ku yi gunaguni da juna, don kada a hukunta ku. Alƙalin yana tsaye a bakin ƙofa!
Repine not against one another, brethren, lest you be condemned: behold, the Judge stands before the door.
10 ’Yan’uwa, ku ɗauki annabawa da suka yi magana a cikin sunan Ubangiji, a matsayin gurbi na haƙuri a cikin shan wahala.
Take, my brethren, the prophets, who have spoken in the name of the Lord: for an example of suffering evil, and of patience.
11 Kamar yadda kuka sani, mukan ce da waɗanda suka jure, masu albarka ne. Kun ji daurewar Ayuba, kuka kuma ga abin da Ubangiji ya yi a ƙarshe. Ubangiji yana cike da tausayi da jinƙai.
Behold, we call them happy, who are patient. You have heard of the patience of Job, and you have seen the end of the Lord, that the Lord is very compassionate and merciful.
12 ’Yan’uwana, fiye da kome, kada ku yi rantsuwa ko da sama, ko da ƙasa ko da wani abu dabam. Bari “I” naku yă zama “I”. “A’a” naku kuma yă zama “A’a”, don kada a hukunta ku.
But, above all things, my brethren, swear not; neither by the heaven, or by the earth, nor by any other oath: but let your yes, be Yes, and your no, No; that you may not fall under condemnation.
13 Akwai waninku da yake shan wahala? Ya kamata yă yi addu’a. Akwai wani mai murna? Sai yă rera waƙoƙin yabo.
Does any one among you suffer evil? let him pray: is any one cheerful? let him sing psalms.
14 Akwai waninku da yake ciwo? Ya kamata yă kira dattawan ikkilisiya su yi masa addu’a, su kuma shafa masa mai cikin sunan Ubangiji.
Is any one sick, among you? let him send for the seniors of the congregation, and let them pray over him, having anointed him with oil, in the name of the Lord.
15 Addu’ar da aka yi cikin bangaskiya, za tă warkar da marar lafiya, Ubangiji zai tashe shi. In ya yi zunubi kuwa za a gafarta masa.
And the prayer of faith will save the sick person, and so the Lord will raise him up; and if he have committed sins, they shall be forgiven him.
16 Saboda haka, ku furta wa juna zunubanku, ku yi addu’a saboda juna, domin ku sami warkarwa. Addu’ar mai adalci tana da iko da kuma amfani.
Confess your faults, one to another, and pray for one another, that you may be healed. The inwrought prayer of the righteous man avails much.
17 Iliya mutum ne kamar mu. Ya yi addu’a da gaske don kada a yi ruwan sama, ba a kuma yi ruwan sama a ƙasar ba har shekaru uku da rabi.
Elias was a man frail and mortal like us, and he prayed fervently that it might not rain, and it did not rain on the land for three years and six months.
18 Ya sāke yin addu’a, sai sammai suka ba da ruwan sama, ƙasa kuma ta ba da amfaninta.
And again he prayed, and the heaven gave rain, and the land brought forth its fruit.
19 ’Yan’uwana, in waninku ya kauce daga gaskiya, wani kuma ya komo da shi,
Brethren, if any one among you be seduced from the truth, and any one turn him back;
20 sai yă tuna da wannan. Duk wanda ya komo da mai zunubi daga kaucewarsa, zai cece shi daga mutuwa, yă kuma rufe zunubai masu ɗumbun yawa.
let him know what he who converts a sinner from the error of his way, shall save a soul from death, and shall cover a multitude of sins.

< Yaƙub 5 >