< Yaƙub 5 >

1 Yanzu fa sai ku saurara, ku masu arziki, ku yi kuka da ihu, saboda azabar da take zuwa a kanku.
Come now, ye rich, weep mourning over your calamities which are coming on you.
2 Arzikinku ya ruɓa, asu kuma sun cinye tufafinku.
Your riches are corrupted, and your garments have become moth-eaten:
3 Zinariyarku da azurfarku sun yi tsatsa. Tsatsarsu kuwa za tă zama shaida a kanku, ta kuma ci namar jikinku kamar wuta. Kun ɓoye dukiya a kwanakin ƙarshe.
your gold and your silver are cankered; and their rust shall be for a witness against you, and eat your flesh like fire. You laid up treasures in the last days.
4 Ga shi! Zaluncin da kuka yi na hakkin ma’aikatan gonakinku yana ta ƙara. Kukan masu girbi ya kai kunnuwan Ubangiji Maɗaukaki.
Behold, the wages of the laborers having reaped your fields, which is fraudulently kept back by you, is crying out: and the voices of the reapers have come into the ears of the Lord of hosts.
5 Kun yi rayuwar jin daɗi a duniya kuna ci kuna sha na ganin dama. Kun ciyar da kanku kun yi ƙiba don ranar yanka.
Ye flourished upon the earth, and were wanton; you nourished your hearts in the day of slaughter.
6 Kun hukunta kun kuma kashe mutane marasa laifi, waɗanda ba su yi gāba da ku ba.
You condemned, you murdered the righteous; nothing antagonizes you.
7 Saboda haka’yan’uwa, sai ku yi haƙuri har dawowar Ubangiji. Ku dubi yadda manomi yakan jira gona ta ba da amfaninta mai kyau, da kuma yadda yake haƙurin jiran ruwan sama na damina da na kaka.
Therefore, O brethren, suffer long, until the coming of the Lord. Behold, the farmer receives the precious fruit of the earth, waiting for it, until he may receive the former and latter rain:
8 Haka ku ma, ku yi haƙuri, ku tsaya da ƙarfi, gama dawowar Ubangiji ya yi kusa.
you also suffer long; establish your hearts; because the coming of the Lord is nigh.
9 ’Yan’uwa, kada ku yi gunaguni da juna, don kada a hukunta ku. Alƙalin yana tsaye a bakin ƙofa!
Do not complain against one another, brethren, in order that you may not be judged: behold, the judge stands before the doors.
10 ’Yan’uwa, ku ɗauki annabawa da suka yi magana a cikin sunan Ubangiji, a matsayin gurbi na haƙuri a cikin shan wahala.
Brethren, receive the prophets who spoke in the name of the Lord as an example of suffering evil and longsuffering.
11 Kamar yadda kuka sani, mukan ce da waɗanda suka jure, masu albarka ne. Kun ji daurewar Ayuba, kuka kuma ga abin da Ubangiji ya yi a ƙarshe. Ubangiji yana cike da tausayi da jinƙai.
Behold, we pronounce them happy who have endured: you have heard the patience of Job, and have seen the end of the Lord, because the Lord is very merciful, and sympathetic.
12 ’Yan’uwana, fiye da kome, kada ku yi rantsuwa ko da sama, ko da ƙasa ko da wani abu dabam. Bari “I” naku yă zama “I”. “A’a” naku kuma yă zama “A’a”, don kada a hukunta ku.
But, my brethren, before all, swear not, neither by heaven, or by earth, or any other oath: but let your conversation be yes yes; and no no; lest you may fall under condemnation.
13 Akwai waninku da yake shan wahala? Ya kamata yă yi addu’a. Akwai wani mai murna? Sai yă rera waƙoƙin yabo.
Who is afflicted among you? let him pray. Who is merry? let him sing psalms.
14 Akwai waninku da yake ciwo? Ya kamata yă kira dattawan ikkilisiya su yi masa addu’a, su kuma shafa masa mai cikin sunan Ubangiji.
Is any one sick among you? let him call for the elders of the church; and let them pray over him, anointing him with oil in the name of the Lord.
15 Addu’ar da aka yi cikin bangaskiya, za tă warkar da marar lafiya, Ubangiji zai tashe shi. In ya yi zunubi kuwa za a gafarta masa.
Truly the prayer of faith shall save the sick, and the Lord will raise him up; if he may have committed sins, they shall be forgiven unto him.
16 Saboda haka, ku furta wa juna zunubanku, ku yi addu’a saboda juna, domin ku sami warkarwa. Addu’ar mai adalci tana da iko da kuma amfani.
Therefore confess your sins to one another, and pray for one another, in order that you may be healed: the inward working prayer of a righteous man avails much.
17 Iliya mutum ne kamar mu. Ya yi addu’a da gaske don kada a yi ruwan sama, ba a kuma yi ruwan sama a ƙasar ba har shekaru uku da rabi.
Elijah was a man of like suffering to us, and he prayed with prayer that it might not rain, and it rained not upon the earth during three years and six months;
18 Ya sāke yin addu’a, sai sammai suka ba da ruwan sama, ƙasa kuma ta ba da amfaninta.
and again he prayed, and the heaven gave rain, and the earth brought forth her fruit.
19 ’Yan’uwana, in waninku ya kauce daga gaskiya, wani kuma ya komo da shi,
My brethren, if any one among you may err from the truth, and one may turn him back;
20 sai yă tuna da wannan. Duk wanda ya komo da mai zunubi daga kaucewarsa, zai cece shi daga mutuwa, yă kuma rufe zunubai masu ɗumbun yawa.
let him know, that the one having turned a sinner from the error of his way shall save a soul from death, and hide a multitude of sins.

< Yaƙub 5 >