< Yaƙub 5 >

1 Yanzu fa sai ku saurara, ku masu arziki, ku yi kuka da ihu, saboda azabar da take zuwa a kanku.
Come, now, you rich men, weep and lament for your miseries that are coming upon you.
2 Arzikinku ya ruɓa, asu kuma sun cinye tufafinku.
Your wealth is corrupted, and your garments are moth-eaten:
3 Zinariyarku da azurfarku sun yi tsatsa. Tsatsarsu kuwa za tă zama shaida a kanku, ta kuma ci namar jikinku kamar wuta. Kun ɓoye dukiya a kwanakin ƙarshe.
your gold and your silver are covered with rust; and their rust will be a testimony against you, and will eat your flesh as fire. You have heaped up treasures in the last days.
4 Ga shi! Zaluncin da kuka yi na hakkin ma’aikatan gonakinku yana ta ƙara. Kukan masu girbi ya kai kunnuwan Ubangiji Maɗaukaki.
Behold, the hire of the laborers who have reaped your fields, which has been unjustly withheld by you, cries out: and the cries of those who have reaped, have entered into the ears of the Lord of hosts.
5 Kun yi rayuwar jin daɗi a duniya kuna ci kuna sha na ganin dama. Kun ciyar da kanku kun yi ƙiba don ranar yanka.
You have lived in pleasure on the earth, and been wanton; you have nourished your hearts, as in a day of slaughter.
6 Kun hukunta kun kuma kashe mutane marasa laifi, waɗanda ba su yi gāba da ku ba.
You have condemned and killed the Just One: and he does not set himself against you.
7 Saboda haka’yan’uwa, sai ku yi haƙuri har dawowar Ubangiji. Ku dubi yadda manomi yakan jira gona ta ba da amfaninta mai kyau, da kuma yadda yake haƙurin jiran ruwan sama na damina da na kaka.
Be patient, therefore, brethren, till the coming of the Lord. Behold, the farmer looks for the precious fruit of the earth, and waits patiently for it, till he receives the early and the latter rain.
8 Haka ku ma, ku yi haƙuri, ku tsaya da ƙarfi, gama dawowar Ubangiji ya yi kusa.
Be you also patient, establish your hearts: for the coming of the Lord draws near.
9 ’Yan’uwa, kada ku yi gunaguni da juna, don kada a hukunta ku. Alƙalin yana tsaye a bakin ƙofa!
Indulge not in complaints against one another, brethren, lest you be condemned: behold, the judge stands before the door.
10 ’Yan’uwa, ku ɗauki annabawa da suka yi magana a cikin sunan Ubangiji, a matsayin gurbi na haƙuri a cikin shan wahala.
Take, my brethren, the prophets who spoke in the name of the Lord, as an example of suffering evil, and of patience.
11 Kamar yadda kuka sani, mukan ce da waɗanda suka jure, masu albarka ne. Kun ji daurewar Ayuba, kuka kuma ga abin da Ubangiji ya yi a ƙarshe. Ubangiji yana cike da tausayi da jinƙai.
Behold, we count those happy who endure. You have heard of the patience of Job, and have seen the final dealing of the Lord, that the Lord is very compassionate and merciful.
12 ’Yan’uwana, fiye da kome, kada ku yi rantsuwa ko da sama, ko da ƙasa ko da wani abu dabam. Bari “I” naku yă zama “I”. “A’a” naku kuma yă zama “A’a”, don kada a hukunta ku.
But above all things, my brethren, swear not, either by heaven, or by the earth, or with any other oath: but let your yes, be yes, and your no, be no, lest you fall into condemnation.
13 Akwai waninku da yake shan wahala? Ya kamata yă yi addu’a. Akwai wani mai murna? Sai yă rera waƙoƙin yabo.
Is any one among you afflicted? let him pray. Is any one cheerful? let him sing praise.
14 Akwai waninku da yake ciwo? Ya kamata yă kira dattawan ikkilisiya su yi masa addu’a, su kuma shafa masa mai cikin sunan Ubangiji.
Is any one among you sick? let him call for the elders of the church, and let them pray over him, anointing him with oil, in the name of the Lord.
15 Addu’ar da aka yi cikin bangaskiya, za tă warkar da marar lafiya, Ubangiji zai tashe shi. In ya yi zunubi kuwa za a gafarta masa.
And the prayer of faith shall save the sick; and the Lord will raise him up. And if he has committed sins, they shall be forgiven him.
16 Saboda haka, ku furta wa juna zunubanku, ku yi addu’a saboda juna, domin ku sami warkarwa. Addu’ar mai adalci tana da iko da kuma amfani.
Confess your faults one to another, and pray for one another, that you may be restored to health: the fervent prayer of a righteous man avails much.
17 Iliya mutum ne kamar mu. Ya yi addu’a da gaske don kada a yi ruwan sama, ba a kuma yi ruwan sama a ƙasar ba har shekaru uku da rabi.
Elijah was a man with passions like our own; and he earnestly prayed that it might not rain; and it did not rain on the land for three years and six months.
18 Ya sāke yin addu’a, sai sammai suka ba da ruwan sama, ƙasa kuma ta ba da amfaninta.
And he prayed again; and the heavens gave rain, and the earth brought forth its fruit.
19 ’Yan’uwana, in waninku ya kauce daga gaskiya, wani kuma ya komo da shi,
Brethren, if any among you should err from the truth, and one should turn him back,
20 sai yă tuna da wannan. Duk wanda ya komo da mai zunubi daga kaucewarsa, zai cece shi daga mutuwa, yă kuma rufe zunubai masu ɗumbun yawa.
let him know that he who turns back a sinner from the error of his way, will save a soul from death, and cover a multitude of sins.

< Yaƙub 5 >