< Yaƙub 5 >

1 Yanzu fa sai ku saurara, ku masu arziki, ku yi kuka da ihu, saboda azabar da take zuwa a kanku.
Og nu, I rige! græder og jamrer over de Ulykker, som komme over eder.
2 Arzikinku ya ruɓa, asu kuma sun cinye tufafinku.
Eders Rigdom er raadnet, og eders Klæder ere mølædte;
3 Zinariyarku da azurfarku sun yi tsatsa. Tsatsarsu kuwa za tă zama shaida a kanku, ta kuma ci namar jikinku kamar wuta. Kun ɓoye dukiya a kwanakin ƙarshe.
eders Guld og Sølv er rustet op, og deres Rust skal være til Vidnesbyrd imod eder og æde eders Kød som en Ild; I have samlet Skatte i de sidste Dage.
4 Ga shi! Zaluncin da kuka yi na hakkin ma’aikatan gonakinku yana ta ƙara. Kukan masu girbi ya kai kunnuwan Ubangiji Maɗaukaki.
Se, den Løn skriger, som I have forholdt Arbejderne, der høstede eders Marker, og Høstfolkenes Raab ere komne ind for den Herre Zebaoths Øren.
5 Kun yi rayuwar jin daɗi a duniya kuna ci kuna sha na ganin dama. Kun ciyar da kanku kun yi ƙiba don ranar yanka.
I levede i Vellevned paa Jorden og efter eders Lyster; I gjorde eders Hjerter til gode som paa en Slagtedag.
6 Kun hukunta kun kuma kashe mutane marasa laifi, waɗanda ba su yi gāba da ku ba.
I domfældte, I dræbte den retfærdige; han staar eder ikke imod.
7 Saboda haka’yan’uwa, sai ku yi haƙuri har dawowar Ubangiji. Ku dubi yadda manomi yakan jira gona ta ba da amfaninta mai kyau, da kuma yadda yake haƙurin jiran ruwan sama na damina da na kaka.
Derfor, værer taalmodige, Brødre! indtil Herrens Tilkommelse. Se, Bonden venter paa Jordens dyrebare Frugt og bier taalmodigt efter den, indtil den faar tidlig Regn og sildig Regn.
8 Haka ku ma, ku yi haƙuri, ku tsaya da ƙarfi, gama dawowar Ubangiji ya yi kusa.
Værer ogsaa I taalmodige, styrker eders Hjerter; thi Herrens Tilkommelse er nær.
9 ’Yan’uwa, kada ku yi gunaguni da juna, don kada a hukunta ku. Alƙalin yana tsaye a bakin ƙofa!
Sukker ikke imod hverandre, Brødre! for at I ikke skulle dømmes; se, Dommeren staar for Døren.
10 ’Yan’uwa, ku ɗauki annabawa da suka yi magana a cikin sunan Ubangiji, a matsayin gurbi na haƙuri a cikin shan wahala.
Brødre! tager Profeterne, som have talt i Herrens Navn, til Forbillede paa at lide ondt og være taalmodige.
11 Kamar yadda kuka sani, mukan ce da waɗanda suka jure, masu albarka ne. Kun ji daurewar Ayuba, kuka kuma ga abin da Ubangiji ya yi a ƙarshe. Ubangiji yana cike da tausayi da jinƙai.
Se, vi prise dem salige, som have holdt ud. I have hørt om Jobs Udholdenhed og vide Udfaldet fra Herren; thi Herren er saare medlidende og barmhjertig.
12 ’Yan’uwana, fiye da kome, kada ku yi rantsuwa ko da sama, ko da ƙasa ko da wani abu dabam. Bari “I” naku yă zama “I”. “A’a” naku kuma yă zama “A’a”, don kada a hukunta ku.
Men for alting, mine Brødre! sværger ikke, hverken ved Himmelen eller ved Jorden eller nogen anden Ed; men eders Ja være Ja, og Nej være Nej, for at I ikke skulle falde under Dom.
13 Akwai waninku da yake shan wahala? Ya kamata yă yi addu’a. Akwai wani mai murna? Sai yă rera waƙoƙin yabo.
Lider nogen iblandt eder ondt, han bede; er nogen vel til Mode, han synge Lovsang!
14 Akwai waninku da yake ciwo? Ya kamata yă kira dattawan ikkilisiya su yi masa addu’a, su kuma shafa masa mai cikin sunan Ubangiji.
Er nogen iblandt eder syg, han kalde Menighedens Ældste til sig, og de skulle bede over ham og salve ham med Olie i Herrens Navn.
15 Addu’ar da aka yi cikin bangaskiya, za tă warkar da marar lafiya, Ubangiji zai tashe shi. In ya yi zunubi kuwa za a gafarta masa.
Og Troens Bøn skal frelse den syge, og Herren skal oprejse ham, og har han gjort Synder, skulle de forlades ham.
16 Saboda haka, ku furta wa juna zunubanku, ku yi addu’a saboda juna, domin ku sami warkarwa. Addu’ar mai adalci tana da iko da kuma amfani.
Bekender derfor Synderne for hverandre og beder for hverandre, for at I maa blive helbredede; en retfærdigs Bøn formaar meget, naar den er alvorlig.
17 Iliya mutum ne kamar mu. Ya yi addu’a da gaske don kada a yi ruwan sama, ba a kuma yi ruwan sama a ƙasar ba har shekaru uku da rabi.
Elias var et Menneske, lige Vilkaar undergivet med os, og han bad en Bøn, at det ikke maatte regne; og det regnede ikke paa Jorden i tre Aar og seks Maaneder.
18 Ya sāke yin addu’a, sai sammai suka ba da ruwan sama, ƙasa kuma ta ba da amfaninta.
Og han bad atter, og Himmelen gav Regn, og Jorden bar sin Frugt.
19 ’Yan’uwana, in waninku ya kauce daga gaskiya, wani kuma ya komo da shi,
Mine Brødre! dersom nogen iblandt eder farer vild fra Sandheden, og nogen omvender ham,
20 sai yă tuna da wannan. Duk wanda ya komo da mai zunubi daga kaucewarsa, zai cece shi daga mutuwa, yă kuma rufe zunubai masu ɗumbun yawa.
han vide, at den, som omvender en Synder fra hans Vejs Vildfarelse, han frelser en Sjæl fra Døden og skjuler en Mangfoldighed af Synder.

< Yaƙub 5 >