< Yaƙub 4 >

1 Me yake jawo faɗace-faɗace da gardandami a tsakaninku? Ashe, ba sha’awace-sha’awacenku da suke yaƙi a zukatanku ba ne?
D’où viennent les guerres et les luttes parmi vous? N’est-ce pas de vos passions qui combattent dans vos membres?
2 Kukan nemi abu ku rasa, sai ku yi kisa da ƙyashi. In kuka rasa abin da kuke nema sai ku shiga yin gardama da faɗa. Kukan rasa ne, domin ba ku roƙi Allah ba.
Vous convoitez, et vous n’avez pas; vous êtes meurtriers, vous êtes jaloux, et vous n’arrivez pas à obtenir; vous êtes dans un état de lutte et de guerre; et vous n’obtenez pas, parce que vous ne demandez pas;
3 Sa’ad da kuka roƙa, ba kwa samu, don kun roƙa da mugun nufi, don ku kashe abin da kuka samu a kan sha’awace-sha’awacenku.
vous demandez, et vous ne recevez pas, parce que vous demandez mal, avec l’intention de satisfaire vos passions.
4 Ku mazinata, ba ku san cewa abokantaka da duniya gāba ce da Allah ba? Duk wanda ya zaɓa yă zama abokin duniya ya zama abokin gāban Allah ke nan.
Adultères, ne savez-vous pas que l’amitié du monde c’est l’inimitié contre Dieu? Quiconque veut être ami du monde se rend ennemi de Dieu.
5 Ko kuna tsammani a banza ne Nassi ya ce ruhun da ya sa yă zauna a cikinmu yana kishi sosai?
Ou bien pensez-vous que l’Ecriture dise en vain: « C’est jusqu’à la jalousie que vous aime l’Esprit qu’il a mis en vous? »
6 Amma yakan ba mu alheri a yalwace. Shi ya sa Nassi ya ce, “Allah yana gāba da masu girman kai amma yakan ba da alheri ga masu tawali’u.”
Mais il donne une grâce d’autant plus grande, selon ce que dit l’Ecriture: « Dieu résiste aux orgueilleux, et il accorde sa grâce aux humbles. »
7 Saboda haka, ku miƙa kanku ga Allah. Ku yi tsayayya da Iblis, zai kuwa guje ku.
Soumettez-vous donc à Dieu; résistez au diable, et il s’enfuira de vous.
8 Ku matso kusa da Allah shi kuwa zai matso kusa da ku. Ku wanke hannuwanku, ku masu zunubi, ku kuma tsarkake zukatanku, ku masu zuciya biyu.
Approchez-vous de Dieu, et il s’approchera de vous. Nettoyez vos mains, pécheurs; purifiez vos cœurs, hommes à l’âme double.
9 Ku yi baƙin ciki, ku yi makoki ku kuma yi kuka. Ku mai da dariyarku ta zama makoki, farin cikinku kuma yă zama ɓacin zuciya.
Sentez votre misère; prenez le deuil, et pleurez: que votre rire se change en pleurs, et votre joie en tristesse.
10 Ku ƙasƙantar da kanku a gaban Ubangiji, zai kuwa ɗaukaka ku.
Humiliez-vous devant le Seigneur, et il vous élèvera.
11 ’Yan’uwa, kada ku ɓata wa juna suna. Duk wanda ya zargi ɗan’uwansa ko ya ɗora masa laifi, yana gāba da doka ne yana kuma yin mata shari’a ke nan. In kuwa ka ɗora wa shari’a laifi, kai ba mai binta ba ne, mai ɗora mata laifi ne.
Frères, ne dites pas de mal les uns des autres. Celui qui parle mal de son frère ou qui juge son frère, parle mal de la loi et juge la loi. Or, si tu juges la loi, tu n’es plus un observateur de la loi, mais tu t’en fais juge.
12 Akwai Mai ba da doka da kuma Alƙali guda ɗaya tak, shi ne yake da ikon ceto da kuma hallakarwa. Amma kai, wane ne da za ka hukunta maƙwabcinka?
Il n’y a qu’un seul législateur et qu’un seul juge, celui qui a la puissance de sauver et de perdre.
13 Yanzu fa sai ku saurara, ku da kuke cewa, “Yau ko gobe za mu je wannan ko wancan birni, mu yi shekara a can, mu yi kasuwanci, mu ci riba.”
Mais qui es-tu, toi qui juges le prochain? Eh bien donc vous qui dites: « Aujourd’hui ou demain nous irons dans telle ville, nous y séjournerons une année, nous trafiquerons, et nous ferons des profits »,
14 Alhali kuwa ba ku ma san abin da zai faru gobe ba. Wane iri ne ranku? Ku kamar hazo ne da yake bayyana na ɗan lokaci sa’an nan yă ɓace.
— vous qui ne savez pas ce qui arrivera demain; —
15 A maimakon haka, ya kamata ku ce, “In Ubangiji ya yarda, muna kuma a raye, za mu yi wannan ko wancan.”
car qu’est-ce que votre vie? Vous êtes une vapeur qui paraît un instant et s’évanouit ensuite: — au lieu de dire: « Si le Seigneur le veut », ou: « Si nous sommes en vie, nous ferons ceci ou cela. »
16 Ga shi, kuna fariya da taƙama. Duk irin wannan taƙama mugun abu ne.
Mais maintenant vous vous vantez dans votre présomption. Toute jactance de cette sorte est mauvaise.
17 Saboda haka, duk wanda ya san abu mai kyan da ya kamata yă yi, bai kuwa yi ba, ya yi zunubi ke nan.
Celui donc qui sait faire ce qui est bien et qui ne le fait pas, commet un péché.

< Yaƙub 4 >