< Yaƙub 4 >

1 Me yake jawo faɗace-faɗace da gardandami a tsakaninku? Ashe, ba sha’awace-sha’awacenku da suke yaƙi a zukatanku ba ne?
Whence wars and whence fightings among you? are they not from hence—due to your pleasures which are taking the field in your members?
2 Kukan nemi abu ku rasa, sai ku yi kisa da ƙyashi. In kuka rasa abin da kuke nema sai ku shiga yin gardama da faɗa. Kukan rasa ne, domin ba ku roƙi Allah ba.
Ye covet—and have not, ye commit murder, and are jealous—and cannot obtain, —ye fight and war. Ye have not—because ye do not really ask,
3 Sa’ad da kuka roƙa, ba kwa samu, don kun roƙa da mugun nufi, don ku kashe abin da kuka samu a kan sha’awace-sha’awacenku.
Ye ask and receive not, because that, basely, ye ask, in order that, in your pleasures, ye may spend [it].
4 Ku mazinata, ba ku san cewa abokantaka da duniya gāba ce da Allah ba? Duk wanda ya zaɓa yă zama abokin duniya ya zama abokin gāban Allah ke nan.
Adulteresses! Know ye not that, the friendship of the world, is, enmity to God? Whosoever, therefore, is minded to be, a friend, of the world, an enemy of God, doth constitute himself.
5 Ko kuna tsammani a banza ne Nassi ya ce ruhun da ya sa yă zauna a cikinmu yana kishi sosai?
Or think ye that, in vain, the scripture speaketh? Is it, for envying, that the spirit which hath taken an abode within us doth crave?
6 Amma yakan ba mu alheri a yalwace. Shi ya sa Nassi ya ce, “Allah yana gāba da masu girman kai amma yakan ba da alheri ga masu tawali’u.”
Howbeit he giveth, greater, favour. Wherefore it saith—God, against the haughty, arrayeth himself, Whereas, unto the lowly, he giveth favour.
7 Saboda haka, ku miƙa kanku ga Allah. Ku yi tsayayya da Iblis, zai kuwa guje ku.
Range yourselves, therefore, under God, but withstand the adversary, and he will flee from you:
8 Ku matso kusa da Allah shi kuwa zai matso kusa da ku. Ku wanke hannuwanku, ku masu zunubi, ku kuma tsarkake zukatanku, ku masu zuciya biyu.
Draw near unto God, and he will draw near unto you. Cleanse hands, sinners! Chasten hearts, double souls!
9 Ku yi baƙin ciki, ku yi makoki ku kuma yi kuka. Ku mai da dariyarku ta zama makoki, farin cikinku kuma yă zama ɓacin zuciya.
Be miserable and lament and weep, let, your laughter, into lamentation, be turned, and, your joy, into dejection;
10 Ku ƙasƙantar da kanku a gaban Ubangiji, zai kuwa ɗaukaka ku.
Be made low in presence of the Lord, and he will lift you up.
11 ’Yan’uwa, kada ku ɓata wa juna suna. Duk wanda ya zargi ɗan’uwansa ko ya ɗora masa laifi, yana gāba da doka ne yana kuma yin mata shari’a ke nan. In kuwa ka ɗora wa shari’a laifi, kai ba mai binta ba ne, mai ɗora mata laifi ne.
Be not speaking one against another, brethren! He that speaketh against a brother, or judgeth his brother, speaketh against law, and judgeth law; Now, if, upon law, thou art passing judgment, thou art not a doer of law, but a judge!
12 Akwai Mai ba da doka da kuma Alƙali guda ɗaya tak, shi ne yake da ikon ceto da kuma hallakarwa. Amma kai, wane ne da za ka hukunta maƙwabcinka?
One, is Lawgiver and Judge—He who hath power to save and to destroy; but who art, thou, that judgest thy neighbour?
13 Yanzu fa sai ku saurara, ku da kuke cewa, “Yau ko gobe za mu je wannan ko wancan birni, mu yi shekara a can, mu yi kasuwanci, mu ci riba.”
Come now! ye that say—Today or To-morrow, we will journey unto this city here, and will spend there a year, and will trade and get gain, —
14 Alhali kuwa ba ku ma san abin da zai faru gobe ba. Wane iri ne ranku? Ku kamar hazo ne da yake bayyana na ɗan lokaci sa’an nan yă ɓace.
Men who are not versed in the morrow—of what sort your life [will be]; for ye are, a vapour—for a little, appearing, then, just disappearing!
15 A maimakon haka, ya kamata ku ce, “In Ubangiji ya yarda, muna kuma a raye, za mu yi wannan ko wancan.”
Instead of your saying—If, the Lord, be pleased, we shall both, live and do this or that;
16 Ga shi, kuna fariya da taƙama. Duk irin wannan taƙama mugun abu ne.
Whereas, now, are ye boasting in your pretensions: —All boasting like this, is, wicked,
17 Saboda haka, duk wanda ya san abu mai kyan da ya kamata yă yi, bai kuwa yi ba, ya yi zunubi ke nan.
To him, therefore, who knoweth how to be doing, a right thing, and is not doing it, it is, sin, unto him.

< Yaƙub 4 >