< Yaƙub 4 >
1 Me yake jawo faɗace-faɗace da gardandami a tsakaninku? Ashe, ba sha’awace-sha’awacenku da suke yaƙi a zukatanku ba ne?
Whence are wars and whence are fightings among you? Are they not hence, from your lusts that war in your members?
2 Kukan nemi abu ku rasa, sai ku yi kisa da ƙyashi. In kuka rasa abin da kuke nema sai ku shiga yin gardama da faɗa. Kukan rasa ne, domin ba ku roƙi Allah ba.
Ye lust, and have not; ye kill, and earnestly covet, and cannot obtain; ye fight and war. Ye have not, because ye ask not;
3 Sa’ad da kuka roƙa, ba kwa samu, don kun roƙa da mugun nufi, don ku kashe abin da kuka samu a kan sha’awace-sha’awacenku.
ye ask, and receive not, because ye ask amiss, that ye may consume it upon your lusts.
4 Ku mazinata, ba ku san cewa abokantaka da duniya gāba ce da Allah ba? Duk wanda ya zaɓa yă zama abokin duniya ya zama abokin gāban Allah ke nan.
Ye adulteresses, know ye not that the friendship of the world is enmity with God? Whoever therefore chooseth to be a friend of the world, becometh an enemy of God.
5 Ko kuna tsammani a banza ne Nassi ya ce ruhun da ya sa yă zauna a cikinmu yana kishi sosai?
Do ye think that the scripture saith in vain, “Zealously doth the Spirit, which made its abode in us, long for us”?
6 Amma yakan ba mu alheri a yalwace. Shi ya sa Nassi ya ce, “Allah yana gāba da masu girman kai amma yakan ba da alheri ga masu tawali’u.”
but he giveth more grace. Wherefore he saith, “God resisteth the proud, but giveth grace to the humble.”
7 Saboda haka, ku miƙa kanku ga Allah. Ku yi tsayayya da Iblis, zai kuwa guje ku.
Submit yourselves therefore to God; resist the Devil, and he will flee from you.
8 Ku matso kusa da Allah shi kuwa zai matso kusa da ku. Ku wanke hannuwanku, ku masu zunubi, ku kuma tsarkake zukatanku, ku masu zuciya biyu.
Draw nigh to God, and he will draw nigh to you. Cleanse your hands, ye sinners, and purify your hearts, ye double-minded.
9 Ku yi baƙin ciki, ku yi makoki ku kuma yi kuka. Ku mai da dariyarku ta zama makoki, farin cikinku kuma yă zama ɓacin zuciya.
Be afflicted, and mourn, and weep; let your laughter be turned into mourning, and your joy into heaviness.
10 Ku ƙasƙantar da kanku a gaban Ubangiji, zai kuwa ɗaukaka ku.
Humble yourselves in the sight of the Lord, and he will exalt you.
11 ’Yan’uwa, kada ku ɓata wa juna suna. Duk wanda ya zargi ɗan’uwansa ko ya ɗora masa laifi, yana gāba da doka ne yana kuma yin mata shari’a ke nan. In kuwa ka ɗora wa shari’a laifi, kai ba mai binta ba ne, mai ɗora mata laifi ne.
Speak not against one another, brethren; he that speaketh against his brother, or judgeth his brother, speaketh against the law, and judgeth the law; but if thou judge the law, thou art not a doer of the law, but a judge.
12 Akwai Mai ba da doka da kuma Alƙali guda ɗaya tak, shi ne yake da ikon ceto da kuma hallakarwa. Amma kai, wane ne da za ka hukunta maƙwabcinka?
One is the Lawgiver and Judge, he who is able to save, and to destroy; but who art thou, that judgest thy neighbor?
13 Yanzu fa sai ku saurara, ku da kuke cewa, “Yau ko gobe za mu je wannan ko wancan birni, mu yi shekara a can, mu yi kasuwanci, mu ci riba.”
Come now, ye that say, To-day and to-morrow we will go into such a city, and spend a year there and traffic, and get gain,
14 Alhali kuwa ba ku ma san abin da zai faru gobe ba. Wane iri ne ranku? Ku kamar hazo ne da yake bayyana na ɗan lokaci sa’an nan yă ɓace.
(whereas ye know not what will be on the morrow; for what is your life? Ye are even a vapor, that appeareth for a little time, and then vanisheth away; )
15 A maimakon haka, ya kamata ku ce, “In Ubangiji ya yarda, muna kuma a raye, za mu yi wannan ko wancan.”
instead of saying, If the Lord will, we shall both live and do this or that;
16 Ga shi, kuna fariya da taƙama. Duk irin wannan taƙama mugun abu ne.
but now ye glory in your boastings. All such glorying is evil.
17 Saboda haka, duk wanda ya san abu mai kyan da ya kamata yă yi, bai kuwa yi ba, ya yi zunubi ke nan.
Therefore to him that knoweth how to do good, and doeth it not, to him it is sin.