< Yaƙub 3 >
1 Kada yawancinku su so ɗaukan kansu a matsayin malamai,’yan’uwana, domin kun san cewa mu da muke koyarwa za a yi mana shari’a mafi tsanani.
hE mama bhrAtaraH, zikSakairasmAbhi rgurutaradaNPO lapsyata iti jnjAtvA yUyam anEkE zikSakA mA bhavata|
2 Dukanmu mukan yi tuntuɓe a hanyoyi dabam-dabam. In wani bai taɓa yin kuskure a cikin maganarsa ba, shi cikakke ne, yana kuma iya ƙame dukan jikinsa.
yataH sarvvE vayaM bahuviSayESu skhalAmaH, yaH kazcid vAkyE na skhalati sa siddhapuruSaH kRtsnaM vazIkarttuM samarthazcAsti|
3 Sa’ad da muka sa linzamai a bakunan dawakai don mu sa su yi mana biyayya, mukan iya bin da dabbar gaba ɗaya.
pazyata vayam azvAn vazIkarttuM tESAM vaktrESu khalInAn nidhAya tESAM kRtsnaM zarIram anuvarttayAmaH|
4 Ko kuwa misali, mu dubi jiragen ruwa, mana. Ko da yake suna da girma ƙwarai kuma iska mai ƙarfi ce take tura su, ana tuƙa su da ɗan ƙaramin sandan ƙarfe ne zuwa duk inda mai tuƙin jirgin yake so.
pazyata yE pOtA atIva bRhadAkArAH pracaNPavAtaizca cAlitAstE'pi karNadhArasya manO'bhimatAd atikSudrENa karNEna vAnjchitaM sthAnaM pratyanuvarttantE|
5 Haka ma harshe yake, ga shi ɗan ƙanƙanin gaɓar jiki ne, amma sai manyan fariya. Ku dubi yadda ɗan ƙaramin ƙyastu yake ƙuna wa babban jeji wuta mana.
tadvad rasanApi kSudratarAggaM santI darpavAkyAni bhASatE| pazya kIdRgmahAraNyaM dahyatE 'lpEna vahninA|
6 Harshe ma wuta ne! A cikin duk gaɓoɓinmu, harshe shi ne tushen kowace irin mugunta, mai ɓata mutum gaba ɗaya, mai zuga zuciyar mutum ta tafasa, shi kuwa jahannama ce take zuga shi. (Geenna )
rasanApi bhavEd vahniradharmmarUpapiSTapE| asmadaggESu rasanA tAdRzaM santiSThati sA kRtsnaM dEhaM kalagkayati sRSTirathasya cakraM prajvalayati narakAnalEna jvalati ca| (Geenna )
7 Kowace irin dabba, tsuntsu, masu ja da ciki da kuma halittun da suke cikin teku an sarrafa su kuma mutum ne ya sarrafa,
pazupakSyurOgajalacarANAM sarvvESAM svabhAvO damayituM zakyatE mAnuSikasvabhAvEna damayAnjcakrE ca|
8 amma ba mutumin da zai iya ya sarrafa harshe. Mugu ne marar hutu, cike da dafi mai kisa.
kintu mAnavAnAM kEnApi jihvA damayituM na zakyatE sA na nivAryyam aniSTaM halAhalaviSENa pUrNA ca|
9 Da harshe mukan yabi Ubangijinmu da kuma Ubanmu, da shi kuma muke la’antar mutane, waɗanda aka halitta a kamannin Allah.
tayA vayaM pitaram IzvaraM dhanyaM vadAmaH, tayA cEzvarasya sAdRzyE sRSTAn mAnavAn zapAmaH|
10 Daga wannan baki guda yabo da la’ana suke fitowa.’Yan’uwana, wannan bai kamata yă zama haka ba.
EkasmAd vadanAd dhanyavAdazApau nirgacchataH| hE mama bhrAtaraH, EtAdRzaM na karttavyaM|
11 Ruwa mai kyau da kuma ruwan gishiri zai iya fito daga maɓulɓula ɗaya?
prasravaNaH kim EkasmAt chidrAt miSTaM tiktanjca tOyaM nirgamayati?
12 ’Yan’uwana, itacen ɓaure yana iya haifar’ya’yan zaitun, ko kuma itacen inabi yă haifi’ya’yan ɓaure? Haka ma, maɓulɓular ruwan gishiri ba zai iya ba da ruwa mai kyau ba.
hE mama bhrAtaraH, uPumbarataruH kiM jitaphalAni drAkSAlatA vA kim uPumbaraphalAni phalituM zaknOti? tadvad EkaH prasravaNO lavaNamiSTE tOyE nirgamayituM na zaknOti|
13 Wane ne mai hikima da fahimta a cikinku? Bari yă nuna ta ta wurin rayuwarsa mai kyau, ta wurin ayyukan da aka yi cikin tawali’un da suke fitowa daga hikima.
yuSmAkaM madhyE jnjAnI subOdhazca ka AstE? tasya karmmANi jnjAnamUlakamRdutAyuktAnIti sadAcArAt sa pramANayatu|
14 Amma in kuna cike da mugun kishi da kuma sonkai a cikin zukatanku, kada ku yi taƙama game da wannan, ko ku danne gaskiya.
kintu yuSmadantaHkaraNamadhyE yadi tiktErSyA vivAdEcchA ca vidyatE tarhi satyamatasya viruddhaM na zlAghadhvaM nacAnRtaM kathayata|
15 Irin wannan “hikima” ba daga sama ta sauko ba, ta duniya ce, ta rashin ruhaniya, ta Iblis kuma.
tAdRzaM jnjAnam UrddhvAd AgataM nahi kintu pArthivaM zarIri bhautikanjca|
16 Gama inda akwai kishi da sonkai, a can za a tarar da hargitsi da kowane irin mugun aiki.
yatO hEtOrIrSyA vivAdEcchA ca yatra vEdyEtE tatraiva kalahaH sarvvaM duSkRtanjca vidyatE|
17 Amma hikimar da ta zo daga sama da fari tana da tsabta gaba ɗaya; sa’an nan mai ƙaunar salama ce, mai sanin ya kamata, mai biyayya, cike da jinƙai da aiki mai kyau, marar nuna bambanci, sahihiya kuma.
kintUrddhvAd AgataM yat jnjAnaM tat prathamaM zuci tataH paraM zAntaM kSAntam AzusandhEyaM dayAdisatphalaiH paripUrNam asandigdhaM niSkapaTanjca bhavati|
18 Masu salama da suke shuki cikin salama sukan girbe adalci.
zAntyAcAribhiH zAntyA dharmmaphalaM rOpyatE|