< Yaƙub 2 >

1 ’Yan’uwana, a matsayinmu cikin Ubangiji Yesu Kiristi maɗaukaki, kada ku nuna bambanci.
My brothers, stop holding the faith of our Lord Jesus Christ, the Glory, with partiality!
2 A ce wani ya shigo cikin taronku saye da zoben zinariya da riguna masu tsada, wani matalauci kuma saye da tsummoki shi ma ya shigo,
For if a man with a gold ring, in fine clothes, should enter your synagogue, and a poor man in filthy rags should also enter,
3 in kuka mai da hankali na musamman ga mutumin da yake da riguna masu tsadan nan kuka kuma ce, “Ga wurin zama mai kyau dominka,” amma kuka ce wa matalaucin nan, “Kai tsaya daga can,” ko kuwa, “Ka zauna a ƙasa kusa da ƙafafuna,”
and you pay special attention to the one wearing the fine clothes and say to him, “You sit in this special seat,” but to the poor one you say, “You stand there,” or “Sit here at my footstool,”
4 ashe, ba ku nuna bambanci a tsakaninku ke nan ba, kuka kuma zama alƙalai masu mugayen tunani?
have you not been separated among yourselves and become judges with malignant thoughts?
5 Ku saurara,’yan’uwana ƙaunatattu. Ashe, Allah bai zaɓi waɗanda suke matalauta a idon duniya don su zama masu wadata cikin bangaskiya, su kuma gāji mulkin da ya yi wa masu ƙaunarsa alkawari ba?
Listen, my beloved brothers. Has not God chosen the poor of the world to be rich in faith and heirs of the kingdom that He has promised to those loving Him?
6 Ga shi kun wulaƙanta matalauta. Ashe, ba masu arziki ne suke cutarku ba? Ba su ba ne suke jan ku zuwa kotu?
But you dishonored the poor one. Do not the rich oppress you and drag you into courts?
7 Ba su ba ne suke ɓata sunan nan mai martaba wanda aka san ku da shi ba?
Do they not blaspheme the noble name that was called upon you?
8 In fa kun kiyaye dokan nan ta mulki wadda take cikin Nassi mai cewa, “Ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka,” kun yi daidai.
If you really fulfill the royal law according to the Scripture, “You shall love your neighbor as yourself,” you do well;
9 Amma in kuka nuna bambanci, kun yi zunubi ke nan shari’a kuma ta same ku da laifi a matsayin masu karya doka.
but if you show partiality, you commit sin, being convicted by the law as transgressors.
10 Gama duk wanda ya kiyaye dukan doka amma ya yi tuntuɓe a kan abu ɗaya kaɗai, ya zama mai laifin karya dukansu ke nan.
For whoever will keep the whole law, yet stumble in one point, has become guilty of all.
11 Gama shi da ya ce, “Kada ka yi zina,” shi ne kuma ya ce, “Kada ka yi kisankai.” In kuwa ba ka zina amma kana kisankai, ka zama mai karya doka ke nan.
Because He who said, “Do not commit adultery,” also said, “Do not murder.” Now if you do not commit adultery, but you do murder, you have become a transgressor of the law.
12 Ku yi magana ku kuma yi aiki kamar waɗanda za a yi musu shari’a bisa ga doka mai ba da’yanci,
Speak and act as being those who are about to be judged by a law of liberty
13 gama za a yi wa duk wanda bai nuna jinƙai ba hukunci babu jinƙai. Jinƙai yakan yi nasara a kan hukunci!
(the judgment will be without mercy to the one not showing mercy). That law exalts mercy over judgment.
14 Wanda amfani ne,’yan’uwana, a ce wani yă ce yana da bangaskiya, amma ba shi da ayyuka? Anya, wannan bangaskiya za tă iya cetonsa kuwa?
What is the advantage, my brothers, if someone says he has faith but does not have works? That faith cannot save him, can it?
15 A ce wani ɗan’uwa ko’yar’uwa ba shi da riguna ko abincin yini,
If a brother or sister is actually naked, and is destitute of the daily food,
16 sai waninku yă ce masa, “Sauka lafiya, Allah ya ba da ci da sha da kuma sutura,” amma bai yi wani abu game da bukatunsa na jiki ba, ina amfani?
and someone among you says to them, “Go in peace, be warmed and filled,” but you (pl) do not give them the things needed for the body, what is the benefit?
17 Haka ma bangaskiya ita kaɗai, in ba tare da ayyuka ba, matacciya ce.
Thus also that faith, if it does not have works, is dead, being by itself.
18 Amma wani zai ce, “Kai kana da bangaskiya; ni kuma ina da ayyuka.” Ka nuna mini bangaskiyarka ba tare da ayyuka ba, ni kuma zan nuna maka bangaskiyata ta wurin abin da nake yi.
(But someone will say: “You have faith and I have works. Show me your faith by your works and I, by my works will show you my faith [what he believes].”
19 Ka gaskata cewa Allah ɗaya ne. To, da kyau! Ai, ko aljanu ma sun gaskata wannan, har da rawan jiki.
You believe that God is one. You do well. The demons also believe—and shudder!)
20 Kai wawa, kana son tabbaci cewa bangaskiya marar ayyuka banza ce?
But you need to know, you foolish fellow, that faith without works is dead!
21 Ashe, ba a mai da kakanmu Ibrahim mai adalci saboda abin da ya yi ba ne sa’ad da ya miƙa ɗansa Ishaku a bisa bagade?
Was not Abraham our father justified by works when he offered Isaac his son on the altar?
22 Ai, ka gani cewa bangaskiyarsa da ayyukansa sun yi aiki tare, bangaskiyarsa kuma ta zama cikakkiya ta wurin abin da ya yi.
You can see that faith was acting together with his works, and the faith was made complete by the works.
23 Aka kuma cika nassin nan da ya ce, “Ibrahim ya gaskata Allah, aka kuma lissafta wannan adalci ne gare shi,” aka kuma ce da shi abokin Allah.
And the Scripture was fulfilled which says, “So Abraham believed God, and it was accounted to him for righteousness.” And he was called ‘friend of God’.
24 Kun ga cewa ashe mutum zai sami kuɓuta ta wurin abin da ya yi ne ba ta wurin bangaskiya kaɗai ba.
You see then that a man is justified by works, and not by faith only.
25 Ta haka kuma ashe, Rahab karuwan nan ba a ɗauke ta mai adalci ce saboda abin da ta yi ba ne sa’ad da ta ba wa’yan leƙen asirin nan masauƙi ta kuma sallame su suka tafi ta wata hanya dabam?
Similarly, was not Rahab the prostitute also justified by works when she received the messengers and sent them out by a different way?
26 Kamar yadda jikin da babu ruhu matacce ne, haka ma bangaskiyar da babu ayyuka matacciya ce.
For just as the body without spirit is dead, so also faith without works is dead.

< Yaƙub 2 >