< Yaƙub 1 >
1 Yaƙub, bawan Allah da kuma na Ubangiji Yesu Kiristi, Zuwa ga kabilan nan goma sha biyu, da suke warwartse a cikin al’ummai. Gaisuwa mai yawa.
James, a bondservant of God and of the Lord Jesus Christ: to the twelve tribes who are scattered over the world. All good wishes.
2 Ku ɗauki wannan da farin ciki mai tsabta,’yan’uwana, duk sa’ad da gwaje-gwaje na kowane iri suka zo muku,
Reckon it nothing but joy, my brethren, whenever you find yourselves hedged in by various trials.
3 domin kun san cewa gwajin bangaskiyarku yakan haifi daurewa.
Be assured that the testing of your faith leads to power of endurance.
4 Dole daurewa ta kammala aikinta don ku zama balagaggu da kuma cikakku, ba ku kuma rasa kome ba.
Only let endurance have perfect results so that you may become perfect and complete, deficient in nothing.
5 In waninku ya rasa hikima, ya kamata yă roƙi Allah, mai bayarwa hannu sake ga kowa ba tare da gori ba, za a kuwa ba shi.
And if any one of you is deficient in wisdom, let him ask God for it, who gives with open hand to all men, and without upbraiding; and it will be given him.
6 Amma sa’ad da ya roƙa, dole yă gaskata, ba tare da shakka ba, domin shi mai shakka, yana kama da raƙumar ruwan tekun da iska take kori tana kuma ɓuɓɓugowa.
But let him ask in faith and have no doubts; for he who has doubts is like the surge of the sea, driven by the wind and tossed into spray.
7 Kada irin wannan mutum yă yi tsammani zai sami wani abu daga Ubangiji;
A person of that sort must not expect to receive anything from the Lord--
8 shi mai zuciya biyu ne, marar tsai da zuciyarsa wuri ɗaya a cikin duk abin da yake yi.
such a one is a man of two minds, undecided in every step he takes.
9 Bari ɗan’uwan da yake cikin halin ƙasƙanci yă yi taƙama a matsayinsa na ɗaukaka.
Let a brother in humble life rejoice when raised to a higher position;
10 Amma wanda yake mai arziki, ya kamata yă yi taƙama a matsayinsa na ƙasƙanci, gama ba zai daɗe ba kamar furen jeji.
but a rich man should rejoice in being brought low, for like flowers among the herbage rich men will pass away.
11 Gama in rana ta fito ta yi zafi mai tsanani sai ta sa tsiro yă yanƙwane tsiro; furensa yă kakkaɓe, kyansa kuma yă lalace. Haka ma mai arziki zai shuɗe yayinda yake cikin harkarsa.
The sun rises with his scorching heat and dries up the herbage, so that its flowers drop off and the beauty of its appearance perishes, and in the same way rich men with all their prosperity will fade away.
12 Mai albarka ne mutumin da yake daurewa cikin gwaji, gama bayan ya yi nasara da gwajin, zai sami rawanin rai wanda Allah ya yi alkawari ga waɗanda suke ƙaunarsa.
Blessed is he who patiently endures trials; for when he has stood the test, he will gain the victor's crown--even the crown of Life--which the Lord has promised to those who love Him.
13 Sa’ad da aka jarrabci mutum, kada yă ce, “Allah ne yake jarrabtarsa.” Gama ba ya yiwuwa a jarrabci Allah da mugunta, shi kuma ba ya jarrabtar kowa;
Let no one say when passing through trial, "My temptation is from God;" for God is incapable of being tempted to do evil, and He Himself tempts no one.
14 amma akan jarrabce kowane mutum sa’ad da muguwar sha’awarsa ta janye shi ta kuma rinjaye shi.
But when a man is tempted, it is his own passions that carry him away and serve as a bait.
15 Sa’an nan, bayan da sha’awar ta yi ciki, takan haifi zunubi; zunubi kuwa, sa’ad da ya balaga yakan haifi mutuwa.
Then the passion conceives, and becomes the parent of sin; and sin, when fully matured, gives birth to death.
16 Kada a ruɗe ku,’yan’uwana ƙaunatattu.
Do not be deceived, my dearly-loved brethren.
17 Kowane abu mai kyau da kuma kowace cikakkiyar kyauta daga sama suke, sun sauko ne daga wurin Uban haskoki, wanda ba sauyawa ko wata alamar sākewa a gare shi faufau.
Every gift which is good, and every perfect boon, is from above, and comes down from the Father, who is the source of all Light. In Him there is no variation nor the slightest suggestion of change.
18 Ya zaɓa yă haife mu ta wurin kalmar gaskiya, domin mu zama’ya’yan fari na dukan abin da ya halitta.
In accordance with His will He made us His children through the Message of the truth, so that we might, in a sense, be the Firstfruits of the things which He has created.
19 ’Yan’uwana ƙaunatattu, ku lura da wannan. Ya kamata kowa yă kasance mai saurin saurara, ba mai saurin magana ba, ba kuma mai saurin fushi ba,
You know this, my dearly-loved brethren. But let every one be quick to hear, slow to speak, and slow to be angry.
20 gama fushin mutum ba ya kawo rayuwar adalcin da Allah yake so.
For a man's anger does not lead to action which God regards as righteous.
21 Saboda haka, ku rabu da ƙazamin hali da kuma kowace irin mugunta ku kuma yi na’am da maganar da aka shuka a cikinku da tawali’u, wadda za tă iya cetonku.
Ridding yourselves, therefore, of all that is vile and of the evil influences which prevail around you, welcome in a humble spirit the Message implanted within you, which is able to save your souls.
22 Kada ku zama masu ji kawai, ku ruɗi kanku. A maimakon haka ku zama masu yin abin da ta ce.
But prove yourselves obedient to the Message, and do not be mere hearers of it, imposing a delusion upon yourselves.
23 Duk wanda yake ji magana ne kawai, bai kuwa aikata abin da ta ce ba, yana kama da mutumin da ya kalli fuskarsa a madubi
For if any one listens but does not obey, he is like a man who carefully looks at his own face in a mirror.
24 bayan ya kalli kansa, sa’ad da ya tashi daga wurin, nan da nan sai yă manta da kamanninsa.
Although he has looked carefully at himself, he goes away, and has immediately forgotten the sort of man he is.
25 Amma duk mai duba cikakkiyar ƙa’idan nan ta’yanci, ya kuma nace a kanta, ya zama ba mai ji ne kawai yă mance ba, sai dai mai yi ne yă zartar, to wannan shi za a yi wa albarka a cikin abin da yake yi.
But he who looks closely into the perfect Law--the Law of freedom--and continues looking, he, being not a hearer who forgets, but an obedient doer, will as the result of his obedience be blessed.
26 In wani ya ɗauki kansa mai addini ne duk da haka bai ƙame harshensa ba, ruɗin kansa yake yi addininsa kuwa banza ne.
If a man thinks that he is scrupulously religious, although he is not curbing his tongue but is deceiving himself, his religious service is worthless.
27 Addinin da Allah Ubanmu ya yarda da shi a matsayin mai tsabta da kuma marar aibi shi ne, a kula da marayu da gwauraye cikin damuwoyinsu, a kuma kiyaye kai daga lalacin da duniya take sa wa.
The religious service which is pure and stainless in the sight of our God and Father is to visit fatherless children and widowed women in their time of trouble, and to keep one's own self unspotted from the world.