< Ishaya 1 >
1 Wahayi game da Yahuda da Urushalima wanda Ishaya ɗan Amoz ya gani a zamanin da Uzziya, Yotam, Ahaz da Hezekiya, suka yi mulkin Yahuda.
Виді́ння Іса́ї, Амо́сового сина, яке він був бачив про Юдею та про Єрусалим за днів Уззії, Йотама, Ахаза та Єзекії, Юдиних царів.
2 Ku kasa kunne, ya sammai! Ki saurara, ya duniya! Gama Ubangiji ya yi magana, “Na yi renon’ya’ya, na kuma raya su, amma sun tayar mini.
Послухайте ви, небеса́, і ти, зе́мле, почуй, бо гово́рить Госпо́дь: Синів Собі ви́ховав й ви́кохав Я, а вони зняли́ бунт проти Мене!
3 Saniya ta san maigidanta, jaki ya san wurin sa wa dabbobi abinci maigidansa, amma Isra’ila ba su sani, mutanena ba su gane ba.”
Віл знає свого власника́, а осел — ясла пана свого, — а Ізраїль не знає Мене́, не зверта́є уваги наро́д Мій на Ме́не.
4 Kash, ya ke al’umma mai zunubi, mutane cike da laifi, tarin masu aikata mugunta,’ya’yan da aka miƙa wa lalaci! Sun yashe Ubangiji; sun rena Mai Tsarkin nan na Isra’ila suka juya masa baya.
О люду ти грішний, наро́де тяжко́ї провини, лиходійське насі́ння, сини-шкідники́, — ви покинули Господа, ви Святого Ізраїлевого поне́хтували, — обернулись наза́д!
5 Me ya sa za a ƙara yin muku dūka? Me ya sa kuka nace ga yin tayarwa? An yi wa dukan kanku rauni, zuciyarku duk tana ciwo.
У що́ будете биті ще, коли неслухня́ними далі ви бу́дете? Хвора ваша вся голова, і все серце боля́ще.
6 Daga tafin ƙafarku zuwa saman kanku ba lafiya, sai miyaku da ƙujewa da manyan gyambuna, ba a tsabtacce su ba ko a daure ko shafa musu magani.
Від підо́шви ноги й аж до голови́ нема ці́лого місця на ньому: рани й ґудзі, та свіжі пора́зи неви́чавлені, і не позав'я́зувані, і оливою не порозм'я́кшувані.
7 Ƙasarku ta zama kufai, an ƙone biranenku da wuta; baƙi suna ƙwace gonakinku a idanunku, ta zama kango kamar sa’ad da baƙi suka rushe ta.
Земля ваша спусто́шена, огнем спа́лені ваші міста́, поле ваше, — на ваших оча́х поїдають чужи́нці його, — з того всьо́го пустиня, немов з руйнува́ння чужи́нців!
8 An bar diyar Sihiyona kamar rumfar mai ƙumu a gonar inabi, kamar bukka a gonar kabewa, kamar birnin da aka kewaye da yaƙi.
І позоста́лась Сіо́нська дочка́, мов курі́нь в винограднику, мов шатро́ на ночлі́г в огірко́вому полі, як місто обло́жене.
9 Da ba a ce Ubangiji Maɗaukaki ya bar mana raguwar masu rai ba, da mun zama kamar Sodom, da mun zama kamar Gomorra.
Коли б був Господь Савао́т не лишив нам останку мало́го, ми були б як Содо́м, до Гомо́рри ми стали б подібні.
10 Ku saurari maganar Ubangiji, ku masu mulkin Sodom; ku kasa kunne ga dokar Allahnmu, ku mutanen Gomorra!
Послухайте сло́ва Господнього, содо́мські князі́, почуйте Зако́н Бога нашого, наро́де гомо́рський, —
11 Ubangiji ya ce, “Yawan hadayunku, mene ne suke a gare ni?” Ina da isashen hadayun ƙonawa, na raguna da na kitsen dabbobi masu ƙiba; ba na jin daɗin jinin bijimai da na tumaki da kuma na awaki.
на́що Мені многота́ ваших же́ртов? говорить Господь. Наси́тився Я цілопа́леннями баранів і жиром ситих теля́т, а крови биків та овець і козлів не жада́ю!
12 Sa’ad da kuka zo don ku bayyana a gabana, wa ya nemi wannan daga gare ku, da kuke kai da kawowa a filayen gidana?
Як прихо́дите ви, щоб явитися перед обличчям Моїм, хто жадає того з руки вашої, щоб топта́ли подві́р'я Мої?
13 Ku daina kawo hadayu marasa amfani! Turarenku abin ƙyama ne gare ni. Ina ƙin bukukkuwanku na Sabon Wata, da na ranakun Asabbaci, da taronku na addini, ba zan iya jure wa mugun taronku ba.
Не прино́сьте ви більше марно́тного да́ру, ваше кадило — оги́да для Мене воно; новомісяччя та ті суботи і скли́кання зборів, — не можу знести́ Я марно́ти цієї!
14 Bukukkuwanku na Sabon Wata da na tsarkakan ranaku na ƙi su. Sun zama mini kaya; na gaji da ɗaukansu.
Новомісяччя ваші й усі ваші свя́та — ненави́дить душа Моя їх: вони стали Мені тягаре́м, — Я зму́чений зно́сити їх.
15 Sa’ad da kuka ɗaga hannuwanku wajen yin addu’a, zan ɓoye fuskata daga gare ku; ko da kun miƙa addu’o’i masu yawa, ba zan kasa kunne ba. Hannuwanku sun cika da jini!
Коли ж руки свої простяга́єте, Я мру́жу від вас Свої очі! Навіть коли ви молитву примно́жуєте, Я не слухаю вас, — ваші руки напо́внені кро́в'ю.
16 Ku yi wanka ku kuma tsabtacce kanku. Ku kawar da mugayen ayyukanku daga gabana; Ku daina aikata mugunta.
Умийтесь, очистьте себе! Відкиньте зло ваших учи́нків із-перед оче́й Моїх, перестаньте чинити лихе́!
17 Ku koyi yin nagarta; ku nemi adalci. Ku ƙarfafa waɗanda aka zalunta. Ku ba wa marayu hakkinsu, ku taimaki gwauruwa.
Навчіться чинити добро, правосу́ддя жадайте, карайте грабі́жника, дайте суд сироті, за вдову заступа́йтесь!
18 Ubangiji ya ce, “Yanzu fa ku zo, bari mu dubi batun nan tare, Ko da zunubanku sun yi ja kamar garura, za su zama fari kamar ƙanƙara; ko da sun yi ja kamar mulufi, za su zama kamar ulu.
Прийдіть, і бу́демо правува́тися, — говорить Госпо́дь: коли ваші гріхи будуть як кармази́н, — стануть білі, мов сніг; якщо бу́дуть червоні, немов багряни́ця, — то стануть мов вовна вони!
19 In kuna da niyya kuna kuma yi mini biyayya, za ku ci abubuwa masu kyau daga ƙasar;
Як захочете ви та послухаєтесь, то бу́дете до́бра землі спожива́ти.
20 amma in kuka yi tsayayya kuka kuma yi tayarwa, za a kashe ku da takobi.” Ni Ubangiji na faɗa.
А коли ви відмо́витеся й неслухня́ними бу́дете, — меч пожере́ вас, бо уста Господні сказали оце!
21 Dubi yadda amintacciyar birni ta zama karuwa! Dā ta cika da yin gaskiya; dā masu adalci a can suke zama, amma yanzu sai masu kisankai kaɗai!
Як стало розпу́сницею вірне місто: було повне воно правосу́ддя, справедливість у нім пробува́ла, тепер же — розбійники!
22 Azurfarki ta zama jebu, an gauraye ruwan inabinki mafi kyau da ruwa.
Срі́бло твоє стало жу́желицею, твоє питво водою розпу́щене.
23 Masu mulkinki’yan tawaye ne, abokan ɓarayi; dukansu suna ƙaunar cin hanci suna bin kyautai. Ba sa taɓa tsare marayu a ɗakin shari’a; ba sa taimakon gwauruwa.
Князі́ твої впе́рті і дру́зі злоді́ям вони, хабара́ вони люблять усі та женуться за да́чкою, не судять вони сироти́, удо́вина справа до них не дохо́дить.
24 Saboda haka Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, Mai Iko nan na Isra’ila, ya furta, “Kai, zan sami hutu daga maƙiyana in kuma yi ramuwa a kan abokan gābana.
Тому́ то говорить Госпо́дь, Господь Савао́т, Си́льний Ізра́їлів: О, буду Я ті́шитися над Своїми супроти́вниками, і помщу́сь на Своїх ворога́х!
25 Zan juye hannuna a kanki; zan wanke ke sarai in fitar da dukan ƙazantarki.
І на тебе Я руку Свою оберну́, і твою жу́желицю немов лу́гом ви́топлю, і все твоє о́ливо повідкида́ю!
26 Zan maido da alƙalanki kamar yadda suke a dā can, mashawartanki kamar yadda suke da fari. Bayan haka za a ce da ke Birnin Masu Adalci, Amintacciyar Birni.”
І верну́ твоїх су́ддів, як перше було́, і твоїх радників, як напоча́тку. По цьо́му тебе будуть звати: місто справедливости, місто вірне!
27 Za a fanshi Sihiyona da adalci, masu tubanta kuma da aikin gaskiya.
Правосу́ддям Сіон буде ви́куплений, а той, хто наве́рнеться в нім, — справедли́вістю.
28 Amma za a karye’yan tawaye da masu zunubi, waɗanda suka rabu da Ubangiji kuma za su hallaka.
А зни́щення грішників та винуватців відбу́деться ра́зом, і ті, що покинули Го́спода, будуть пони́щені.
29 “Za ku ji kunya saboda masujadan ƙarƙashin itatuwan oak da kuka yi farin ciki; za a kunyata ku saboda lambun da kuka zaɓa.
І бу́дете ви посоро́млені за ті дуби́, що їх пожада́ли, і застида́єтеся за садки́, які ви́брали ви.
30 Za ku zama kamar itacen oak mai busasshen ganyaye, kamar lambu marar ruwa.
Бо станете ви, як той дуб, що листя всиха́є йому́, і як сад, що не має води.
31 Mutum mai ƙarfi zai zama kamar rama, aikinsa kuma kamar tartsatsin wuta; duka za su ƙone tare, ba kuwa wanda zai kashe wutar.”
I ста́неться сильний костри́цею, його ж ді́ло — за і́скру, і вони обоє попа́ляться ра́зом, — і не бу́де ніко́го, хто б те погаси́в!