< Ishaya 1 >

1 Wahayi game da Yahuda da Urushalima wanda Ishaya ɗan Amoz ya gani a zamanin da Uzziya, Yotam, Ahaz da Hezekiya, suka yi mulkin Yahuda.
La vision d'Esaïe, fils d'Amots, laquelle il a vue touchant Juda et Jérusalem, aux jours de Hozias, de Jotham, d'Achas, et d'Ezéchias, Rois de Juda.
2 Ku kasa kunne, ya sammai! Ki saurara, ya duniya! Gama Ubangiji ya yi magana, “Na yi renon’ya’ya, na kuma raya su, amma sun tayar mini.
Cieux écoutez, et toi Terre prête l'oreille, car l'Eternel a parlé, [disant]; j'ai nourri des enfants, je les ai élevés, mais ils se sont rebellés contre moi.
3 Saniya ta san maigidanta, jaki ya san wurin sa wa dabbobi abinci maigidansa, amma Isra’ila ba su sani, mutanena ba su gane ba.”
Le bœuf connaît son possesseur, et l'âne la crèche de son maître; [mais] Israël n'a point de connaissance, mon peuple n'a point d'intelligence.
4 Kash, ya ke al’umma mai zunubi, mutane cike da laifi, tarin masu aikata mugunta,’ya’yan da aka miƙa wa lalaci! Sun yashe Ubangiji; sun rena Mai Tsarkin nan na Isra’ila suka juya masa baya.
Ha! nation pécheresse, peuple chargé d'iniquité, race de gens malins, enfants qui ne font que se corrompre; ils ont abandonné l'Eternel, ils ont irrité par leur mépris le Saint d'Israël, ils se sont retirés en arrière.
5 Me ya sa za a ƙara yin muku dūka? Me ya sa kuka nace ga yin tayarwa? An yi wa dukan kanku rauni, zuciyarku duk tana ciwo.
Pourquoi seriez-vous encore battus? vous ajouterez la révolte; toute tête est en douleur, et tout cœur est languissant.
6 Daga tafin ƙafarku zuwa saman kanku ba lafiya, sai miyaku da ƙujewa da manyan gyambuna, ba a tsabtacce su ba ko a daure ko shafa musu magani.
Depuis la plante du pied jusqu'à la tête il n'y a rien d'entier en lui; il [n'y a que] blessure, meurtrissure, et plaie pourrie, qui n'ont point été nettoyées, ni bandées, et dont aucune n'a été adoucie d'huile.
7 Ƙasarku ta zama kufai, an ƙone biranenku da wuta; baƙi suna ƙwace gonakinku a idanunku, ta zama kango kamar sa’ad da baƙi suka rushe ta.
Votre pays n'est que désolation, et vos villes sont en feu; les étrangers dévorent votre terre en votre présence, et cette désolation est comme un bouleversement fait par des étrangers.
8 An bar diyar Sihiyona kamar rumfar mai ƙumu a gonar inabi, kamar bukka a gonar kabewa, kamar birnin da aka kewaye da yaƙi.
Car la fille de Sion restera comme une cabane dans une vigne; comme une loge dans un champ de concombres; comme une ville serrée de près.
9 Da ba a ce Ubangiji Maɗaukaki ya bar mana raguwar masu rai ba, da mun zama kamar Sodom, da mun zama kamar Gomorra.
Si l'Eternel des armées ne nous eût laissé des gens de reste, qui sont même bien peu, nous eussions été comme Sodome, nous eussions été semblables à Gomorrhe.
10 Ku saurari maganar Ubangiji, ku masu mulkin Sodom; ku kasa kunne ga dokar Allahnmu, ku mutanen Gomorra!
Ecoutez la parole de l'Eternel, Conducteurs de Sodome, prêtez l'oreille à la Loi de notre Dieu, peuple de Gomorrhe!
11 Ubangiji ya ce, “Yawan hadayunku, mene ne suke a gare ni?” Ina da isashen hadayun ƙonawa, na raguna da na kitsen dabbobi masu ƙiba; ba na jin daɗin jinin bijimai da na tumaki da kuma na awaki.
Qu'ai-je à faire, dit l'Eternel, de la multitude de vos sacrifices? je suis rassasié d'holocaustes de moutons, et de la graisse de bêtes grasses, je ne prends point de plaisir au sang des taureaux, ni des agneaux, ni des boucs.
12 Sa’ad da kuka zo don ku bayyana a gabana, wa ya nemi wannan daga gare ku, da kuke kai da kawowa a filayen gidana?
Quand vous entrez pour vous présenter devant ma face; qui a requis cela de vos mains, que vous fouliez de [vos pieds] mes parvis?
13 Ku daina kawo hadayu marasa amfani! Turarenku abin ƙyama ne gare ni. Ina ƙin bukukkuwanku na Sabon Wata, da na ranakun Asabbaci, da taronku na addini, ba zan iya jure wa mugun taronku ba.
Ne continuez plus à m'apporter des oblations de néant; le parfum m'est en abomination; quant aux nouvelles Lunes, et aux Sabbats, et à la publication de [vos] convocations, je n'en puis [plus] supporter l'ennui, ni de [vos] assemblées solennelles.
14 Bukukkuwanku na Sabon Wata da na tsarkakan ranaku na ƙi su. Sun zama mini kaya; na gaji da ɗaukansu.
Mon âme hait vos nouvelles Lunes, et vos fêtes solennelles; elles me sont fâcheuses, je suis las de les supporter.
15 Sa’ad da kuka ɗaga hannuwanku wajen yin addu’a, zan ɓoye fuskata daga gare ku; ko da kun miƙa addu’o’i masu yawa, ba zan kasa kunne ba. Hannuwanku sun cika da jini!
C'est pourquoi quand vous étendrez vos mains, je cacherai mes yeux de vous, et quand vous multiplierez vos prières, je ne les exaucerai point; vos mains sont pleines de sang.
16 Ku yi wanka ku kuma tsabtacce kanku. Ku kawar da mugayen ayyukanku daga gabana; Ku daina aikata mugunta.
Lavez-vous, nettoyez-vous, ôtez de devant mes yeux la malice de vos actions; cessez de mal faire.
17 Ku koyi yin nagarta; ku nemi adalci. Ku ƙarfafa waɗanda aka zalunta. Ku ba wa marayu hakkinsu, ku taimaki gwauruwa.
Apprenez à bien faire; recherchez la droiture; redressez celui qui est foulé, faites justice à l'orphelin, défendez la cause de la veuve.
18 Ubangiji ya ce, “Yanzu fa ku zo, bari mu dubi batun nan tare, Ko da zunubanku sun yi ja kamar garura, za su zama fari kamar ƙanƙara; ko da sun yi ja kamar mulufi, za su zama kamar ulu.
Venez maintenant, dit l'Eternel, et débattons nos droits; quand vos péchés seraient comme le cramoisi, ils seront blanchis comme la neige; et quand ils seraient rouges comme le vermillon, ils seront [blanchis] comme la laine.
19 In kuna da niyya kuna kuma yi mini biyayya, za ku ci abubuwa masu kyau daga ƙasar;
Si vous obéissez volontairement, vous mangerez le meilleur du pays.
20 amma in kuka yi tsayayya kuka kuma yi tayarwa, za a kashe ku da takobi.” Ni Ubangiji na faɗa.
Mais si vous refusez [d'obéir], et si vous êtes rebelles, vous serez consumés par l'épée; car la bouche de l'Eternel a parlé.
21 Dubi yadda amintacciyar birni ta zama karuwa! Dā ta cika da yin gaskiya; dā masu adalci a can suke zama, amma yanzu sai masu kisankai kaɗai!
Comment s'est prostituée la cité fidèle? elle était pleine de droiture, et la justice logeait en elle, mais maintenant elle est pleine de meurtriers.
22 Azurfarki ta zama jebu, an gauraye ruwan inabinki mafi kyau da ruwa.
Ton argent est devenu de l'écume, et ton breuvage est mêlé d'eau.
23 Masu mulkinki’yan tawaye ne, abokan ɓarayi; dukansu suna ƙaunar cin hanci suna bin kyautai. Ba sa taɓa tsare marayu a ɗakin shari’a; ba sa taimakon gwauruwa.
Les Principaux de ton peuple sont revêches, et compagnons de larrons; chacun d'eux aime les présents, ils courent après les récompenses; ils ne font point droit à l'orphelin, et la cause de la veuve ne vient point devant eux.
24 Saboda haka Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, Mai Iko nan na Isra’ila, ya furta, “Kai, zan sami hutu daga maƙiyana in kuma yi ramuwa a kan abokan gābana.
C'est pourquoi le Seigneur, l'Eternel des armées, le Puissant d'Israël dit; Ha! je me satisferai [en punissant] mes adversaires, et je me vengerai de mes ennemis.
25 Zan juye hannuna a kanki; zan wanke ke sarai in fitar da dukan ƙazantarki.
Et je remettrai ma main sur toi, et je refondrai au net ton écume, et j'ôterai tout ton étain.
26 Zan maido da alƙalanki kamar yadda suke a dā can, mashawartanki kamar yadda suke da fari. Bayan haka za a ce da ke Birnin Masu Adalci, Amintacciyar Birni.”
Mais je rétablirai tes Juges, tels qu'[ils étaient] la première fois, et tes Conseillers, tels que du commencement; et après cela on t'appellera, Cité de justice, ville fidèle.
27 Za a fanshi Sihiyona da adalci, masu tubanta kuma da aikin gaskiya.
Sion sera rachetée par le jugement, et ceux qui y retourneront [seront rachetés] par la justice.
28 Amma za a karye’yan tawaye da masu zunubi, waɗanda suka rabu da Ubangiji kuma za su hallaka.
Mais les rebelles, et les pécheurs seront froissés ensemble; et ceux qui ont abandonné l'Eternel, seront consumés.
29 “Za ku ji kunya saboda masujadan ƙarƙashin itatuwan oak da kuka yi farin ciki; za a kunyata ku saboda lambun da kuka zaɓa.
Car on sera honteux à cause des chênes que vous avez désirés; et vous rougirez à cause des jardins que vous avez choisis.
30 Za ku zama kamar itacen oak mai busasshen ganyaye, kamar lambu marar ruwa.
Car vous serez comme le chêne dont la feuille tombe, et comme le jardin qui n'a point d'eau.
31 Mutum mai ƙarfi zai zama kamar rama, aikinsa kuma kamar tartsatsin wuta; duka za su ƙone tare, ba kuwa wanda zai kashe wutar.”
Et le fort sera de l'étoupe, et son œuvre une étincelle; et tous deux brûleront ensemble, et il n'y aura personne qui éteigne [le feu].

< Ishaya 1 >