< Ishaya 1 >

1 Wahayi game da Yahuda da Urushalima wanda Ishaya ɗan Amoz ya gani a zamanin da Uzziya, Yotam, Ahaz da Hezekiya, suka yi mulkin Yahuda.
Vision d'Ésaïe, fils d'Amoz, concernant Juda et Jérusalem, au temps d'Ozias, de Jotham, d'Achaz et d'Ézéchias, rois de Juda.
2 Ku kasa kunne, ya sammai! Ki saurara, ya duniya! Gama Ubangiji ya yi magana, “Na yi renon’ya’ya, na kuma raya su, amma sun tayar mini.
Écoutez, cieux, et écoute, terre, car Yahvé a parlé: « J'ai nourri et élevé des enfants et ils se sont rebellés contre moi.
3 Saniya ta san maigidanta, jaki ya san wurin sa wa dabbobi abinci maigidansa, amma Isra’ila ba su sani, mutanena ba su gane ba.”
Le bœuf connaît son propriétaire, et l'âne la crèche de son maître; mais Israël ne le sait pas. Mon peuple n'en tient pas compte. »
4 Kash, ya ke al’umma mai zunubi, mutane cike da laifi, tarin masu aikata mugunta,’ya’yan da aka miƙa wa lalaci! Sun yashe Ubangiji; sun rena Mai Tsarkin nan na Isra’ila suka juya masa baya.
Ah nation pécheresse, un peuple chargé d'iniquité, la progéniture des méchants, les enfants qui font des affaires corrompues! Ils ont abandonné Yahvé. Ils ont méprisé le Saint d'Israël. Ils sont éloignés et arriérés.
5 Me ya sa za a ƙara yin muku dūka? Me ya sa kuka nace ga yin tayarwa? An yi wa dukan kanku rauni, zuciyarku duk tana ciwo.
Pourquoi devriez-vous être plus battu, que vous vous révoltez de plus en plus? La tête entière est malade, et le cœur entier s'évanouit.
6 Daga tafin ƙafarku zuwa saman kanku ba lafiya, sai miyaku da ƙujewa da manyan gyambuna, ba a tsabtacce su ba ko a daure ko shafa musu magani.
De la plante du pied à la tête, il n'y a pas de solidité, mais les blessures, les zébrures et les plaies ouvertes. Elles n'ont pas été refermées, pansées, ou apaisées avec de l'huile.
7 Ƙasarku ta zama kufai, an ƙone biranenku da wuta; baƙi suna ƙwace gonakinku a idanunku, ta zama kango kamar sa’ad da baƙi suka rushe ta.
Ton pays est dévasté. Vos villes sont brûlées par le feu. Les étrangers dévorent votre terre en votre présence et elle est désolée, comme renversé par des étrangers.
8 An bar diyar Sihiyona kamar rumfar mai ƙumu a gonar inabi, kamar bukka a gonar kabewa, kamar birnin da aka kewaye da yaƙi.
La fille de Sion est abandonnée comme un abri dans une vigne, comme une cabane dans un champ de melons, comme une ville assiégée.
9 Da ba a ce Ubangiji Maɗaukaki ya bar mana raguwar masu rai ba, da mun zama kamar Sodom, da mun zama kamar Gomorra.
A moins que Yahvé des armées ne nous ait laissé un tout petit reste, nous aurions été comme Sodome. Nous aurions été comme Gomorrah.
10 Ku saurari maganar Ubangiji, ku masu mulkin Sodom; ku kasa kunne ga dokar Allahnmu, ku mutanen Gomorra!
Écoutez la parole de Yahvé, chefs de Sodome! Écoutez la loi de notre Dieu, peuple de Gomorrhe!
11 Ubangiji ya ce, “Yawan hadayunku, mene ne suke a gare ni?” Ina da isashen hadayun ƙonawa, na raguna da na kitsen dabbobi masu ƙiba; ba na jin daɗin jinin bijimai da na tumaki da kuma na awaki.
« Quelle est la multitude de vos sacrifices pour moi? », dit Yahvé. « J'en ai assez des holocaustes de béliers... et la graisse des animaux nourris. Je ne me délecte pas du sang des taureaux, ou d'agneaux, ou de chèvres mâles.
12 Sa’ad da kuka zo don ku bayyana a gabana, wa ya nemi wannan daga gare ku, da kuke kai da kawowa a filayen gidana?
Quand tu viendras comparaître devant moi, qui a exigé cela de ta main, pour piétiner mes cours?
13 Ku daina kawo hadayu marasa amfani! Turarenku abin ƙyama ne gare ni. Ina ƙin bukukkuwanku na Sabon Wata, da na ranakun Asabbaci, da taronku na addini, ba zan iya jure wa mugun taronku ba.
N'apportez plus d'offrandes vaines. L'encens est une abomination pour moi. Nouvelles lunes, sabbats, et convocations... Je ne supporte pas les assemblées maléfiques.
14 Bukukkuwanku na Sabon Wata da na tsarkakan ranaku na ƙi su. Sun zama mini kaya; na gaji da ɗaukansu.
Mon âme déteste vos nouvelles lunes et vos fêtes fixes. Ils sont un fardeau pour moi. Je suis fatigué de les supporter.
15 Sa’ad da kuka ɗaga hannuwanku wajen yin addu’a, zan ɓoye fuskata daga gare ku; ko da kun miƙa addu’o’i masu yawa, ba zan kasa kunne ba. Hannuwanku sun cika da jini!
Quand tu étends tes mains, je te cache mes yeux. Oui, quand tu fais beaucoup de prières, je n'entends pas. Vos mains sont pleines de sang.
16 Ku yi wanka ku kuma tsabtacce kanku. Ku kawar da mugayen ayyukanku daga gabana; Ku daina aikata mugunta.
Lavez-vous. Rendez vous propres. Ôtez de devant mes yeux la méchanceté de vos actes. Cessez de faire le mal.
17 Ku koyi yin nagarta; ku nemi adalci. Ku ƙarfafa waɗanda aka zalunta. Ku ba wa marayu hakkinsu, ku taimaki gwauruwa.
Apprenez à bien faire. Cherchez la justice. Soulager les opprimés. Défendez les orphelins. Plaidez pour la veuve. »
18 Ubangiji ya ce, “Yanzu fa ku zo, bari mu dubi batun nan tare, Ko da zunubanku sun yi ja kamar garura, za su zama fari kamar ƙanƙara; ko da sun yi ja kamar mulufi, za su zama kamar ulu.
« Viens maintenant, et raisonnons ensemble », dit l'Éternel: « Si vos péchés sont comme l'écarlate, ils deviendront blancs comme la neige. Même s'ils sont rouges comme la cramoisie, ils seront comme la laine.
19 In kuna da niyya kuna kuma yi mini biyayya, za ku ci abubuwa masu kyau daga ƙasar;
Si vous êtes volontaires et obéissants, vous mangerez le bien de la terre;
20 amma in kuka yi tsayayya kuka kuma yi tayarwa, za a kashe ku da takobi.” Ni Ubangiji na faɗa.
mais si vous refusez et vous rebellez, vous serez dévorés par l'épée; car la bouche de Yahvé l'a dit. »
21 Dubi yadda amintacciyar birni ta zama karuwa! Dā ta cika da yin gaskiya; dā masu adalci a can suke zama, amma yanzu sai masu kisankai kaɗai!
Comment la ville fidèle est devenue une prostituée! Elle était pleine de justice. La droiture s'est logée en elle, mais maintenant il y a des meurtriers.
22 Azurfarki ta zama jebu, an gauraye ruwan inabinki mafi kyau da ruwa.
Votre argent est devenu de la poussière, votre vin mélangé à de l'eau.
23 Masu mulkinki’yan tawaye ne, abokan ɓarayi; dukansu suna ƙaunar cin hanci suna bin kyautai. Ba sa taɓa tsare marayu a ɗakin shari’a; ba sa taimakon gwauruwa.
Tes princes sont rebelles et compagnons de voleurs. Tout le monde aime les pots-de-vin et suit les récompenses. Ils ne défendent pas les orphelins, la cause de la veuve ne leur revient pas non plus.
24 Saboda haka Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, Mai Iko nan na Isra’ila, ya furta, “Kai, zan sami hutu daga maƙiyana in kuma yi ramuwa a kan abokan gābana.
C'est pourquoi l'Éternel, le Yahvé des Armées, le Puissant d'Israël, dit: « Ah, je vais être soulagé de mes adversaires, et me venger de mes ennemis.
25 Zan juye hannuna a kanki; zan wanke ke sarai in fitar da dukan ƙazantarki.
Je tournerai ma main vers toi, purgez complètement vos scories, et emportera tout ton étain.
26 Zan maido da alƙalanki kamar yadda suke a dā can, mashawartanki kamar yadda suke da fari. Bayan haka za a ce da ke Birnin Masu Adalci, Amintacciyar Birni.”
Je rétablirai vos juges comme au début, et vos conseillers comme au début. Ensuite, on t'appellera « la cité de la justice », une ville fidèle.
27 Za a fanshi Sihiyona da adalci, masu tubanta kuma da aikin gaskiya.
Sion sera rachetée avec justice, et ses convertis avec droiture.
28 Amma za a karye’yan tawaye da masu zunubi, waɗanda suka rabu da Ubangiji kuma za su hallaka.
Mais la destruction des transgresseurs et des pécheurs sera commune, et ceux qui abandonnent Yahvé seront consumés.
29 “Za ku ji kunya saboda masujadan ƙarƙashin itatuwan oak da kuka yi farin ciki; za a kunyata ku saboda lambun da kuka zaɓa.
Car ils auront honte des chênes que tu as désirés, et tu seras confondu pour les jardins que tu as choisis.
30 Za ku zama kamar itacen oak mai busasshen ganyaye, kamar lambu marar ruwa.
Car vous serez comme un chêne dont la feuille se fane, et comme un jardin qui n'a pas d'eau.
31 Mutum mai ƙarfi zai zama kamar rama, aikinsa kuma kamar tartsatsin wuta; duka za su ƙone tare, ba kuwa wanda zai kashe wutar.”
Les forts seront comme de l'amadou, et son travail comme une étincelle. Ils brûleront tous les deux ensemble, et personne ne les éteindra. »

< Ishaya 1 >