< Ishaya 1 >

1 Wahayi game da Yahuda da Urushalima wanda Ishaya ɗan Amoz ya gani a zamanin da Uzziya, Yotam, Ahaz da Hezekiya, suka yi mulkin Yahuda.
The vision of Isaiah son of Amoz, that he saw concerning Judah and Jerusalem, in the days of Uzziah, Jotham, Ahaz, and Hezekiah, kings of Judah.
2 Ku kasa kunne, ya sammai! Ki saurara, ya duniya! Gama Ubangiji ya yi magana, “Na yi renon’ya’ya, na kuma raya su, amma sun tayar mini.
Hear, heavens, and give ear, earth; for Yahweh has spoken: “I have nourished and brought up children, but they have rebelled against me.
3 Saniya ta san maigidanta, jaki ya san wurin sa wa dabbobi abinci maigidansa, amma Isra’ila ba su sani, mutanena ba su gane ba.”
The ox knows his owner, and the donkey his master's feeding trough, but Israel does not know, Israel does not understand.”
4 Kash, ya ke al’umma mai zunubi, mutane cike da laifi, tarin masu aikata mugunta,’ya’yan da aka miƙa wa lalaci! Sun yashe Ubangiji; sun rena Mai Tsarkin nan na Isra’ila suka juya masa baya.
Woe! Nation, sinners, a people weighed down with iniquity, offspring of evildoers, sons who act corruptly! They have abandoned Yahweh, they have despised the Holy One of Israel, they have estranged themselves from him.
5 Me ya sa za a ƙara yin muku dūka? Me ya sa kuka nace ga yin tayarwa? An yi wa dukan kanku rauni, zuciyarku duk tana ciwo.
Why are you still being beaten? Why do you rebel more and more? The whole head is sick, the whole heart is weak.
6 Daga tafin ƙafarku zuwa saman kanku ba lafiya, sai miyaku da ƙujewa da manyan gyambuna, ba a tsabtacce su ba ko a daure ko shafa musu magani.
From the sole of the foot to the head there is no part unharmed; only wounds, and bruises, and fresh open wounds; they have not been closed, cleansed, bandaged, nor treated with oil.
7 Ƙasarku ta zama kufai, an ƙone biranenku da wuta; baƙi suna ƙwace gonakinku a idanunku, ta zama kango kamar sa’ad da baƙi suka rushe ta.
Your country is ruined; your cities are burned; your fields—in your presence, strangers are destroying them— abandoned devastation, overthrown by strangers.
8 An bar diyar Sihiyona kamar rumfar mai ƙumu a gonar inabi, kamar bukka a gonar kabewa, kamar birnin da aka kewaye da yaƙi.
The daughter of Zion is left like a hut in a vineyard, like a shed in a garden of cucumbers, like a besieged city.
9 Da ba a ce Ubangiji Maɗaukaki ya bar mana raguwar masu rai ba, da mun zama kamar Sodom, da mun zama kamar Gomorra.
If Yahweh of hosts had not left for us a small remnant, we would have been like Sodom, we would have been like Gomorrah.
10 Ku saurari maganar Ubangiji, ku masu mulkin Sodom; ku kasa kunne ga dokar Allahnmu, ku mutanen Gomorra!
Hear the word of Yahweh, you rulers of Sodom; listen to the law of our God, you people of Gomorrah:
11 Ubangiji ya ce, “Yawan hadayunku, mene ne suke a gare ni?” Ina da isashen hadayun ƙonawa, na raguna da na kitsen dabbobi masu ƙiba; ba na jin daɗin jinin bijimai da na tumaki da kuma na awaki.
“What is the multitude of your sacrifices to me?” says Yahweh. “I have had enough of the burnt offerings of rams, and the fat of fatted beasts; and in the blood of bulls, lambs, or goats I do not delight.
12 Sa’ad da kuka zo don ku bayyana a gabana, wa ya nemi wannan daga gare ku, da kuke kai da kawowa a filayen gidana?
When you come to appear before me, who has required this of you, to trample my courts?
13 Ku daina kawo hadayu marasa amfani! Turarenku abin ƙyama ne gare ni. Ina ƙin bukukkuwanku na Sabon Wata, da na ranakun Asabbaci, da taronku na addini, ba zan iya jure wa mugun taronku ba.
Bring no more meaningless offerings; incense is an abomination to me; your new moon and Sabbath assemblies—I cannot tolerate these wicked assemblies.
14 Bukukkuwanku na Sabon Wata da na tsarkakan ranaku na ƙi su. Sun zama mini kaya; na gaji da ɗaukansu.
I hate your new moons and your appointed feasts; they are a burden to me; I am tired of enduring them.
15 Sa’ad da kuka ɗaga hannuwanku wajen yin addu’a, zan ɓoye fuskata daga gare ku; ko da kun miƙa addu’o’i masu yawa, ba zan kasa kunne ba. Hannuwanku sun cika da jini!
So when you spread out your hands in prayer, I hide my eyes from you; even though you offer many prayers, I will not listen; your hands are full of blood.
16 Ku yi wanka ku kuma tsabtacce kanku. Ku kawar da mugayen ayyukanku daga gabana; Ku daina aikata mugunta.
Wash, cleanse yourselves; remove the evil of your deeds from my sight; stop being evil;
17 Ku koyi yin nagarta; ku nemi adalci. Ku ƙarfafa waɗanda aka zalunta. Ku ba wa marayu hakkinsu, ku taimaki gwauruwa.
learn to do good; seek justice, make straight the oppression, give justice to the fatherless, defend the widow.”
18 Ubangiji ya ce, “Yanzu fa ku zo, bari mu dubi batun nan tare, Ko da zunubanku sun yi ja kamar garura, za su zama fari kamar ƙanƙara; ko da sun yi ja kamar mulufi, za su zama kamar ulu.
“Come now, and let us reason together,” says Yahweh; “though your sins are like scarlet, they will be white like snow; though they are red like crimson, they will be like wool.
19 In kuna da niyya kuna kuma yi mini biyayya, za ku ci abubuwa masu kyau daga ƙasar;
If you are willing and obedient, you will eat the good of the land,
20 amma in kuka yi tsayayya kuka kuma yi tayarwa, za a kashe ku da takobi.” Ni Ubangiji na faɗa.
but if you refuse and rebel, the sword will devour you,” for the mouth of Yahweh has spoken it.
21 Dubi yadda amintacciyar birni ta zama karuwa! Dā ta cika da yin gaskiya; dā masu adalci a can suke zama, amma yanzu sai masu kisankai kaɗai!
How the faithful city has become a prostitute! She who was full of justice—she was full of righteousness, but now she is full of murderers.
22 Azurfarki ta zama jebu, an gauraye ruwan inabinki mafi kyau da ruwa.
Your silver has become impure, your wine mixed with water.
23 Masu mulkinki’yan tawaye ne, abokan ɓarayi; dukansu suna ƙaunar cin hanci suna bin kyautai. Ba sa taɓa tsare marayu a ɗakin shari’a; ba sa taimakon gwauruwa.
Your princes are rebels and companions of thieves; everyone loves bribes and runs after payoffs. They do not defend the fatherless, nor does the widow's legal plea come before them.
24 Saboda haka Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, Mai Iko nan na Isra’ila, ya furta, “Kai, zan sami hutu daga maƙiyana in kuma yi ramuwa a kan abokan gābana.
Therefore this is the declaration of the Lord Yahweh of hosts, the Mighty One of Israel: “Woe to them! I will take vengeance against my adversaries, and avenge myself against my enemies;
25 Zan juye hannuna a kanki; zan wanke ke sarai in fitar da dukan ƙazantarki.
I will turn my hand against you, refine away your dross as with lye, and take away all your dross.
26 Zan maido da alƙalanki kamar yadda suke a dā can, mashawartanki kamar yadda suke da fari. Bayan haka za a ce da ke Birnin Masu Adalci, Amintacciyar Birni.”
I will restore your judges as at the first, and your counselors as at the beginning; after that you will be called the city of righteousness, a faithful town.”
27 Za a fanshi Sihiyona da adalci, masu tubanta kuma da aikin gaskiya.
Zion will be redeemed by justice, and her repentant ones by righteousness.
28 Amma za a karye’yan tawaye da masu zunubi, waɗanda suka rabu da Ubangiji kuma za su hallaka.
Rebels and sinners will be crushed together, and those who abandon Yahweh will be done away with.
29 “Za ku ji kunya saboda masujadan ƙarƙashin itatuwan oak da kuka yi farin ciki; za a kunyata ku saboda lambun da kuka zaɓa.
“For you will be ashamed of the sacred oak trees that you desired, and you will be embarrassed by the gardens that you have chosen.
30 Za ku zama kamar itacen oak mai busasshen ganyaye, kamar lambu marar ruwa.
For you will be like an oak whose leaf fades, and like a garden that has no water.
31 Mutum mai ƙarfi zai zama kamar rama, aikinsa kuma kamar tartsatsin wuta; duka za su ƙone tare, ba kuwa wanda zai kashe wutar.”
The strong man will be like tinder, and his work like a spark; they will both burn together, and no one will quench them.”

< Ishaya 1 >