< Ishaya 1 >

1 Wahayi game da Yahuda da Urushalima wanda Ishaya ɗan Amoz ya gani a zamanin da Uzziya, Yotam, Ahaz da Hezekiya, suka yi mulkin Yahuda.
The visions of Isaiah, the son of Amoz, which he saw concerning Judah and Jerusalem, in the days of Uzziah, Jotham, Ahaz, and Hezekiah, kings of Judah.
2 Ku kasa kunne, ya sammai! Ki saurara, ya duniya! Gama Ubangiji ya yi magana, “Na yi renon’ya’ya, na kuma raya su, amma sun tayar mini.
Hear, O heavens, and give ear, O earth! For Jehovah speaketh: “I have nourished and brought up children, And they have rebelled against me.
3 Saniya ta san maigidanta, jaki ya san wurin sa wa dabbobi abinci maigidansa, amma Isra’ila ba su sani, mutanena ba su gane ba.”
The ox knoweth his owner, And the ass his master's crib; But Israel doth not know; My people do not consider.”
4 Kash, ya ke al’umma mai zunubi, mutane cike da laifi, tarin masu aikata mugunta,’ya’yan da aka miƙa wa lalaci! Sun yashe Ubangiji; sun rena Mai Tsarkin nan na Isra’ila suka juya masa baya.
Ah, sinful nation! a people laden with iniquity! A race of evil-doers! degenerate children! They have forsaken Jehovah; they have despised the Holy One of Israel; They have gone backward.
5 Me ya sa za a ƙara yin muku dūka? Me ya sa kuka nace ga yin tayarwa? An yi wa dukan kanku rauni, zuciyarku duk tana ciwo.
Where can ye be smitten again, Since ye renew your rebellion? The whole head is sick, and the whole heart faint;
6 Daga tafin ƙafarku zuwa saman kanku ba lafiya, sai miyaku da ƙujewa da manyan gyambuna, ba a tsabtacce su ba ko a daure ko shafa musu magani.
From the sole of the foot even to the head, there is no soundness in it; It is all bruises, and stripes, and flesh wounds, Neither pressed, nor bound up, nor softened with ointment.
7 Ƙasarku ta zama kufai, an ƙone biranenku da wuta; baƙi suna ƙwace gonakinku a idanunku, ta zama kango kamar sa’ad da baƙi suka rushe ta.
Your country is desolate; Your cities are burnt with fire; Your ground, strangers devour it before your eyes; It is become desolate, destroyed by an enemy.
8 An bar diyar Sihiyona kamar rumfar mai ƙumu a gonar inabi, kamar bukka a gonar kabewa, kamar birnin da aka kewaye da yaƙi.
And the daughter of Zion is left as a shed in a vineyard, As a hut in a garden of cucumbers, As a besieged city.
9 Da ba a ce Ubangiji Maɗaukaki ya bar mana raguwar masu rai ba, da mun zama kamar Sodom, da mun zama kamar Gomorra.
Had not Jehovah of hosts left us a small remnant, We had soon become as Sodom; We had been like to Gomorrah.
10 Ku saurari maganar Ubangiji, ku masu mulkin Sodom; ku kasa kunne ga dokar Allahnmu, ku mutanen Gomorra!
Hear ye the word of Jehovah, ye princes of Sodom! Give ear to the instruction of our God, ye people of Gomorrah!
11 Ubangiji ya ce, “Yawan hadayunku, mene ne suke a gare ni?” Ina da isashen hadayun ƙonawa, na raguna da na kitsen dabbobi masu ƙiba; ba na jin daɗin jinin bijimai da na tumaki da kuma na awaki.
What to me is the multitude of your sacrifices? saith Jehovah; I am satiated with burnt-offerings of rams, and the fat of fed beasts; In the blood of bullocks and of lambs and of goats I have no delight.
12 Sa’ad da kuka zo don ku bayyana a gabana, wa ya nemi wannan daga gare ku, da kuke kai da kawowa a filayen gidana?
When ye come to appear before me, Who hath required this of you, to tread my courts?
13 Ku daina kawo hadayu marasa amfani! Turarenku abin ƙyama ne gare ni. Ina ƙin bukukkuwanku na Sabon Wata, da na ranakun Asabbaci, da taronku na addini, ba zan iya jure wa mugun taronku ba.
Bring no more false oblations! Incense is an abomination to me, The new moon also, and the sabbath, and the calling of the assembly; Iniquity and festivals I cannot endure.
14 Bukukkuwanku na Sabon Wata da na tsarkakan ranaku na ƙi su. Sun zama mini kaya; na gaji da ɗaukansu.
Your new moons and your feasts my soul hateth; They are a burden to me; I am weary of bearing them.
15 Sa’ad da kuka ɗaga hannuwanku wajen yin addu’a, zan ɓoye fuskata daga gare ku; ko da kun miƙa addu’o’i masu yawa, ba zan kasa kunne ba. Hannuwanku sun cika da jini!
When ye spread forth your hands, I will hide mine eyes from you; Yea, when ye multiply prayers, I will not hear: Your hands are full of blood!
16 Ku yi wanka ku kuma tsabtacce kanku. Ku kawar da mugayen ayyukanku daga gabana; Ku daina aikata mugunta.
Wash you; make you clean; Put away your evil doings from before mine eyes;
17 Ku koyi yin nagarta; ku nemi adalci. Ku ƙarfafa waɗanda aka zalunta. Ku ba wa marayu hakkinsu, ku taimaki gwauruwa.
Cease to do evil; Learn to do well; Seek justice; relieve the oppressed; Defend the fatherless; plead for the widow!
18 Ubangiji ya ce, “Yanzu fa ku zo, bari mu dubi batun nan tare, Ko da zunubanku sun yi ja kamar garura, za su zama fari kamar ƙanƙara; ko da sun yi ja kamar mulufi, za su zama kamar ulu.
Come, now, and let us argue together, saith Jehovah. Though your sins be as scarlet, they shall be as white as snow; Though they be red as crimson, they shall be like wool.
19 In kuna da niyya kuna kuma yi mini biyayya, za ku ci abubuwa masu kyau daga ƙasar;
If ye be willing and obedient, Ye shall consume the good of the land.
20 amma in kuka yi tsayayya kuka kuma yi tayarwa, za a kashe ku da takobi.” Ni Ubangiji na faɗa.
But if ye refuse, and be rebellious, The sword shall consume you; For the mouth of Jehovah hath said it.
21 Dubi yadda amintacciyar birni ta zama karuwa! Dā ta cika da yin gaskiya; dā masu adalci a can suke zama, amma yanzu sai masu kisankai kaɗai!
How is the faithful city become a harlot, She that was full of equity! Once justice dwelt in her, but now murderers!
22 Azurfarki ta zama jebu, an gauraye ruwan inabinki mafi kyau da ruwa.
Thy silver is become dross; Thy wine is adulterated with water.
23 Masu mulkinki’yan tawaye ne, abokan ɓarayi; dukansu suna ƙaunar cin hanci suna bin kyautai. Ba sa taɓa tsare marayu a ɗakin shari’a; ba sa taimakon gwauruwa.
Thy princes are faithless, companions of thieves; Every one of them loveth gifts, and seeketh rewards; They render not justice to the fatherless, And the cause of the widow cometh not before them.
24 Saboda haka Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, Mai Iko nan na Isra’ila, ya furta, “Kai, zan sami hutu daga maƙiyana in kuma yi ramuwa a kan abokan gābana.
Wherefore, thus saith the Lord, Jehovah of hosts, the Mighty One of Israel: Ha! I will ease me of mine adversaries, And avenge me of mine enemies.
25 Zan juye hannuna a kanki; zan wanke ke sarai in fitar da dukan ƙazantarki.
And I will again turn my hand toward thee, And wholly purge away thy dross, And take away all thy alloy.
26 Zan maido da alƙalanki kamar yadda suke a dā can, mashawartanki kamar yadda suke da fari. Bayan haka za a ce da ke Birnin Masu Adalci, Amintacciyar Birni.”
And I will restore thee judges, as at the first, And counsellors, as at the beginning. Then shalt thou be called the city of righteousness, the faithful city.
27 Za a fanshi Sihiyona da adalci, masu tubanta kuma da aikin gaskiya.
Through justice shall Zion be delivered, And her reformed sons through righteousness.
28 Amma za a karye’yan tawaye da masu zunubi, waɗanda suka rabu da Ubangiji kuma za su hallaka.
But destruction shall fall at once on the rebels and sinners; Yea, they that forsake Jehovah shall be consumed.
29 “Za ku ji kunya saboda masujadan ƙarƙashin itatuwan oak da kuka yi farin ciki; za a kunyata ku saboda lambun da kuka zaɓa.
For ye shall be ashamed of the terebinths in which ye delighted; Ye shall blush for the gardens which ye loved;
30 Za ku zama kamar itacen oak mai busasshen ganyaye, kamar lambu marar ruwa.
And ye shall be as a terebinth-tree whose leaves are withered, And as a garden in which is no water.
31 Mutum mai ƙarfi zai zama kamar rama, aikinsa kuma kamar tartsatsin wuta; duka za su ƙone tare, ba kuwa wanda zai kashe wutar.”
The strong shall become tow, And his work a spark of fire; Both shall burn together, And none shall quench them.

< Ishaya 1 >