< Ishaya 1 >
1 Wahayi game da Yahuda da Urushalima wanda Ishaya ɗan Amoz ya gani a zamanin da Uzziya, Yotam, Ahaz da Hezekiya, suka yi mulkin Yahuda.
Esajas's, Amoz's Søns, Syn, hvilket han saa om Juda og Jerusalem i de Dage, da Usias, Jotham, Akas, Ezekias, vare Konger i Juda.
2 Ku kasa kunne, ya sammai! Ki saurara, ya duniya! Gama Ubangiji ya yi magana, “Na yi renon’ya’ya, na kuma raya su, amma sun tayar mini.
Hører, I Himle! og du Jord! mærk, thi Herren har talt; jeg har opdraget Børn og opfostret dem, men de have gjort Overtrædelse imod mig.
3 Saniya ta san maigidanta, jaki ya san wurin sa wa dabbobi abinci maigidansa, amma Isra’ila ba su sani, mutanena ba su gane ba.”
En Okse kender sin Ejermand og et Asen sin Herres Krybbe; Israel kender intet, mit Folk forstaar intet.
4 Kash, ya ke al’umma mai zunubi, mutane cike da laifi, tarin masu aikata mugunta,’ya’yan da aka miƙa wa lalaci! Sun yashe Ubangiji; sun rena Mai Tsarkin nan na Isra’ila suka juya masa baya.
Ve et syndigt Folk, et Folk med svar Misgerning, en Slægt af onde, vanartede Børn! De forlode Herren, de opirrede den Hellige i Israel, de ere vegne tilbage.
5 Me ya sa za a ƙara yin muku dūka? Me ya sa kuka nace ga yin tayarwa? An yi wa dukan kanku rauni, zuciyarku duk tana ciwo.
Hvorfor ville I lade eder slaa ydermere? hvorfor ville I forøge eders Afvigelse? hvert Hoved er sygt, og hvert Hjerte er mat.
6 Daga tafin ƙafarku zuwa saman kanku ba lafiya, sai miyaku da ƙujewa da manyan gyambuna, ba a tsabtacce su ba ko a daure ko shafa musu magani.
Fra Fodsaale og indtil Hovedet er intet helt paa det: Saar og Skrammer og friske Hug! de ere ikke trykkede ud og ikke forbundne og ikke lindrede med Olie.
7 Ƙasarku ta zama kufai, an ƙone biranenku da wuta; baƙi suna ƙwace gonakinku a idanunku, ta zama kango kamar sa’ad da baƙi suka rushe ta.
Eders Land er en Ørk, eders Stæder ere opbrændte med Ild; fremmede fortære eders Land for eders Øjne, og der er en Ørk, som naar fremmede have væltet op og ned.
8 An bar diyar Sihiyona kamar rumfar mai ƙumu a gonar inabi, kamar bukka a gonar kabewa, kamar birnin da aka kewaye da yaƙi.
Og Zions Datter er bleven tilovers som en Hytte i en Vingaard, som et Natteskjul i en Græskarhave, som en frelst Stad.
9 Da ba a ce Ubangiji Maɗaukaki ya bar mana raguwar masu rai ba, da mun zama kamar Sodom, da mun zama kamar Gomorra.
Dersom ikke den Herre Zebaoth havde ladet os en liden Levning tilbage, havde vi været som Sodoma, været lige med Gomorra.
10 Ku saurari maganar Ubangiji, ku masu mulkin Sodom; ku kasa kunne ga dokar Allahnmu, ku mutanen Gomorra!
I Sodomas Fyrster! hører Herrens Ord; I Gomorras Folk! mærker paa vor Guds Lov!
11 Ubangiji ya ce, “Yawan hadayunku, mene ne suke a gare ni?” Ina da isashen hadayun ƙonawa, na raguna da na kitsen dabbobi masu ƙiba; ba na jin daɗin jinin bijimai da na tumaki da kuma na awaki.
Hvad skal jeg med eders mangfoldige Ofre? siger Herren; jeg er mæt af Brændofre af Vædre og af det fedede Kvægs Fedme, og jeg har ingen Lyst til Blod af Okser og Lam og Bukke.
12 Sa’ad da kuka zo don ku bayyana a gabana, wa ya nemi wannan daga gare ku, da kuke kai da kawowa a filayen gidana?
Naar I komme for at ses for mit Ansigt, hvo har krævet dette af eder, at I skulle nedtræde mine Forgaarde?
13 Ku daina kawo hadayu marasa amfani! Turarenku abin ƙyama ne gare ni. Ina ƙin bukukkuwanku na Sabon Wata, da na ranakun Asabbaci, da taronku na addini, ba zan iya jure wa mugun taronku ba.
Bærer ikke mere forfængeligt Madoffer frem, det er mig en vederstyggelig Røgelse; Nymaaneder og Sabbater og Højtids Forsamlinger —! jeg fordrager ikke Uret og Højtid.
14 Bukukkuwanku na Sabon Wata da na tsarkakan ranaku na ƙi su. Sun zama mini kaya; na gaji da ɗaukansu.
Min Sjæl hader eders Nymaaneder og eders Højtider; de ere blevne mig til Byrde; jeg er træt af at taale dem.
15 Sa’ad da kuka ɗaga hannuwanku wajen yin addu’a, zan ɓoye fuskata daga gare ku; ko da kun miƙa addu’o’i masu yawa, ba zan kasa kunne ba. Hannuwanku sun cika da jini!
Og naar I udbrede eders Hænder, skjuler jeg mine Øjne for eder; hvor meget I end bede, hører jeg dog ikke; eders Hænder ere fulde af Blod.
16 Ku yi wanka ku kuma tsabtacce kanku. Ku kawar da mugayen ayyukanku daga gabana; Ku daina aikata mugunta.
Toer eder, renser eder, borttager eders Idrætters Ondskab fra mine Øjne, lader af at gøre ilde!
17 Ku koyi yin nagarta; ku nemi adalci. Ku ƙarfafa waɗanda aka zalunta. Ku ba wa marayu hakkinsu, ku taimaki gwauruwa.
Lærer at gøre godt, søger Ret, leder den vanartede paa rette Vej, skaffer den faderløse Ret, udfører Enkens Sag!
18 Ubangiji ya ce, “Yanzu fa ku zo, bari mu dubi batun nan tare, Ko da zunubanku sun yi ja kamar garura, za su zama fari kamar ƙanƙara; ko da sun yi ja kamar mulufi, za su zama kamar ulu.
Kommer dog, og lader os gaa i Rette med hinanden, siger Herren. Dersom eders Synder end vare som Karmesin, da skulle de blive hvide som Sne; om de end vare røde som Skarlagen, skulle de blive som Uld.
19 In kuna da niyya kuna kuma yi mini biyayya, za ku ci abubuwa masu kyau daga ƙasar;
Dersom I ere villige og lydige, skulle I æde Landets Gode.
20 amma in kuka yi tsayayya kuka kuma yi tayarwa, za a kashe ku da takobi.” Ni Ubangiji na faɗa.
Men dersom I vægre eder og ere genstridige, skulle I fortæres af Sværd; thi Herrens Mund har talt det.
21 Dubi yadda amintacciyar birni ta zama karuwa! Dā ta cika da yin gaskiya; dā masu adalci a can suke zama, amma yanzu sai masu kisankai kaɗai!
Hvorledes er den trofaste Stad bleven til en Hore? den var fuld af Ret; Retfærdighed havde hjemme i den, men nu er der Mordere.
22 Azurfarki ta zama jebu, an gauraye ruwan inabinki mafi kyau da ruwa.
Dit Sølv er blevet til Slagger, din Drik er spædet med Vand.
23 Masu mulkinki’yan tawaye ne, abokan ɓarayi; dukansu suna ƙaunar cin hanci suna bin kyautai. Ba sa taɓa tsare marayu a ɗakin shari’a; ba sa taimakon gwauruwa.
Dine Fyrster ere Oprørere og Tyvenes Stalbrødre, de elske alle Skænk og jage efter Gaver; de ville ikke skaffe den faderløse Ret, og Enkens Sag maa ikke komme for dem.
24 Saboda haka Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, Mai Iko nan na Isra’ila, ya furta, “Kai, zan sami hutu daga maƙiyana in kuma yi ramuwa a kan abokan gābana.
Derfor siger Herren, den Herre Zebaoth, den Mægtige i Israel: Ve! jeg vil mætte min Vrede paa mine Modstandere og hævne mig paa mine Fjender.
25 Zan juye hannuna a kanki; zan wanke ke sarai in fitar da dukan ƙazantarki.
Og jeg vil atter vende min Haand imod dig og udsmelte dine Slagger som med Ludsalt og borttage alt dit Tin.
26 Zan maido da alƙalanki kamar yadda suke a dā can, mashawartanki kamar yadda suke da fari. Bayan haka za a ce da ke Birnin Masu Adalci, Amintacciyar Birni.”
Og jeg vil give dig Dommere igen som i Førstningen og Raadsherrer som i Begyndelsen; derefter skal du kaldes Retfærdigheds Stad, en trofast By.
27 Za a fanshi Sihiyona da adalci, masu tubanta kuma da aikin gaskiya.
Zion skal forløses ved Ret og de omvendte i den ved Retfærdighed.
28 Amma za a karye’yan tawaye da masu zunubi, waɗanda suka rabu da Ubangiji kuma za su hallaka.
Hen Overtrædere og Syndere skulle knuses til Hobe, og de, som forlade Herren, skulle omkomme.
29 “Za ku ji kunya saboda masujadan ƙarƙashin itatuwan oak da kuka yi farin ciki; za a kunyata ku saboda lambun da kuka zaɓa.
Thi de skulle blive til Skamme for de Terebinters Skyld, som I havde Lyst tilog I skulle beskæmmes for de Havers Skyld, som vare eders Glæde.
30 Za ku zama kamar itacen oak mai busasshen ganyaye, kamar lambu marar ruwa.
Thi I skulle blive som en Terebinte, der fælder sit Blad, og som en Have, hvori der ikke er Vand.
31 Mutum mai ƙarfi zai zama kamar rama, aikinsa kuma kamar tartsatsin wuta; duka za su ƙone tare, ba kuwa wanda zai kashe wutar.”
Og den stærke skal blive til Blaar og hans Gerning til en Gnist; og de skulle begge brænde med hinanden, og der skal ingen være, som slukker.