< Ishaya 1 >
1 Wahayi game da Yahuda da Urushalima wanda Ishaya ɗan Amoz ya gani a zamanin da Uzziya, Yotam, Ahaz da Hezekiya, suka yi mulkin Yahuda.
Judah siangpahrang Uziah, Jotham, Ahaz, Hezekiah tinaw a bawi awh navah, Amos capa Isaiah ni Judahnaw hoi Jerusalem kho hoi kâkuen lah a hmu e vision,
2 Ku kasa kunne, ya sammai! Ki saurara, ya duniya! Gama Ubangiji ya yi magana, “Na yi renon’ya’ya, na kuma raya su, amma sun tayar mini.
Cathut ni lawk a dei dawkvah, Oe kalvannaw, thai awh haw. Oe talai, hnâpakeng haw. Ka kawk e catounnaw ni Kai na taran awh toe.
3 Saniya ta san maigidanta, jaki ya san wurin sa wa dabbobi abinci maigidansa, amma Isra’ila ba su sani, mutanena ba su gane ba.”
Maito ni kakhoumkung a panue. La ni hai kakawkkung e dokko a panue. Isarelnaw ni Kai na panuek awh hoeh toe. Ka taminaw ni pouk panuek awh hoeh toe a ti.
4 Kash, ya ke al’umma mai zunubi, mutane cike da laifi, tarin masu aikata mugunta,’ya’yan da aka miƙa wa lalaci! Sun yashe Ubangiji; sun rena Mai Tsarkin nan na Isra’ila suka juya masa baya.
Miphun kathout, sak payonnae ka phawt e tamihu, kahawihoehe hno ka sak e catoun, rawknae canaw lah bo na o awh toung aw. BAWIPA hah na ceitakhai awh toe. Isarelnaw e kathounge Cathut hah na bari awh laipalah, hnamthun sin awh teh, na kamlang takhai awh toe.
5 Me ya sa za a ƙara yin muku dūka? Me ya sa kuka nace ga yin tayarwa? An yi wa dukan kanku rauni, zuciyarku duk tana ciwo.
Ahnimanaw hah bangtelamaw bout ka hem han vai. Bangtelamaw bout ka yue han vai. A lû teh hmâtan hoi king akawi, na lung hai tha khoeroe awm hoeh toe.
6 Daga tafin ƙafarku zuwa saman kanku ba lafiya, sai miyaku da ƙujewa da manyan gyambuna, ba a tsabtacce su ba ko a daure ko shafa musu magani.
Khoktabei koehoi lû koe totouh, damnae awmhoeh. Hmâtan hoi, a phing teh, a hnai ka lawi e seng lah ao. Hote hmânaw hah pâsu hoeh, kawm hoeh, satui hai hluk pouh hoeh rah.
7 Ƙasarku ta zama kufai, an ƙone biranenku da wuta; baƙi suna ƙwace gonakinku a idanunku, ta zama kango kamar sa’ad da baƙi suka rushe ta.
Nangmae ram teh tami kingkadi lah ao. Khonaw hai hmai a kak toe. Na talainaw hai ramlouknaw ni na hmaitung vah a ca awh vaiteh, taran ni a raphoe tangcoung e patetlah tami kingdi han.
8 An bar diyar Sihiyona kamar rumfar mai ƙumu a gonar inabi, kamar bukka a gonar kabewa, kamar birnin da aka kewaye da yaƙi.
Zion canu hai misur takha ringnae patetlah payin takha dawk e rim patetlah taran ni a kalup e kho patetlah ceitakhai lah ao.
9 Da ba a ce Ubangiji Maɗaukaki ya bar mana raguwar masu rai ba, da mun zama kamar Sodom, da mun zama kamar Gomorra.
Rasahu BAWIPA ni mamouh hanelah younca hai cawi sak hoehpawiteh, maimouh teh Sodom kho patetlah o awh teh, Gomorrah kho hoi kâvan awh.
10 Ku saurari maganar Ubangiji, ku masu mulkin Sodom; ku kasa kunne ga dokar Allahnmu, ku mutanen Gomorra!
Sodom kho ka uk e bawinaw, Cathut e lawk hah thai awh haw. Gomorrah khocanaw kaimae Cathut lawk hah hnâpakeng awh haw.
11 Ubangiji ya ce, “Yawan hadayunku, mene ne suke a gare ni?” Ina da isashen hadayun ƙonawa, na raguna da na kitsen dabbobi masu ƙiba; ba na jin daɗin jinin bijimai da na tumaki da kuma na awaki.
Cathut ni a dei e teh, nangmouh ni na thueng awh e satheinaw teh kai hoi bangtelamaw a kâkuet vaw. Thuengnae tu, ka phuekuek lah na paca e saring thawnaw hoi ka boum toe. Maito, tuca hoi hmaenaw e thi hah ka ngai hoeh.
12 Sa’ad da kuka zo don ku bayyana a gabana, wa ya nemi wannan daga gare ku, da kuke kai da kawowa a filayen gidana?
Ka hmalah minhmai patue han na tho awh navah, Kaie thongma coungroe hanlah apinimaw na patoun awh.
13 Ku daina kawo hadayu marasa amfani! Turarenku abin ƙyama ne gare ni. Ina ƙin bukukkuwanku na Sabon Wata, da na ranakun Asabbaci, da taronku na addini, ba zan iya jure wa mugun taronku ba.
Ayawmyin e pasoum hno hah bout thokhai awh hanh lawih. Hmai na sawi awh e hmuitui hah ka panuet. Thapa rei hnin, kamhluem hnin, kamkhueng hnin naw hai ka panuet. Hawihoehnae hoi kâkalawt e kathoung kamkhuengnae hah ka panguep thai hoeh.
14 Bukukkuwanku na Sabon Wata da na tsarkakan ranaku na ƙi su. Sun zama mini kaya; na gaji da ɗaukansu.
Ka muitha ni nangmae thapa rei hnin hoi nangmae pawinaw hah ka hmuhma. Kai katarawk e lah ao teh ka panguep lawi ngawt ka tawn toe.
15 Sa’ad da kuka ɗaga hannuwanku wajen yin addu’a, zan ɓoye fuskata daga gare ku; ko da kun miƙa addu’o’i masu yawa, ba zan kasa kunne ba. Hannuwanku sun cika da jini!
Nangmouh ni, na kut na kadai awh toteh, alouklah na kangvawi takhai awh han. Avai moikapap na ratoum awh nakunghai, ka thai mahoeh. Na kutnaw teh thi hoi akawi.
16 Ku yi wanka ku kuma tsabtacce kanku. Ku kawar da mugayen ayyukanku daga gabana; Ku daina aikata mugunta.
Kâpasu awh, kamthoung awh. Na payonnae hah ka hmaitung hoi takhoe awh. Kahawihoehe nuencang hah kâhat awh leih.
17 Ku koyi yin nagarta; ku nemi adalci. Ku ƙarfafa waɗanda aka zalunta. Ku ba wa marayu hakkinsu, ku taimaki gwauruwa.
Kahawi hno sak hanelah kamtu awh. Lannae hah tawng awh. Ka lawngkoi e hah palan awh. Naranaw hanelah kalan lah sak awh. Lahmainunaw hanelah kalan lah sak awh. Lahmainunaw hah pahren awh.
18 Ubangiji ya ce, “Yanzu fa ku zo, bari mu dubi batun nan tare, Ko da zunubanku sun yi ja kamar garura, za su zama fari kamar ƙanƙara; ko da sun yi ja kamar mulufi, za su zama kamar ulu.
BAWIPA ni a dei e teh, tho awh. Cungtalah pouk awh haw sei. Nangmae yonnae teh ka paling nakunghai tadamtui patetlah a pangaw han. Âthi patetlah ka paling nakunghai tumuen patetlah ao han.
19 In kuna da niyya kuna kuma yi mini biyayya, za ku ci abubuwa masu kyau daga ƙasar;
Nangmouh ni ngainae lahoi lawk na ngâi awh pawiteh, ram thung e hnokahawi e a pawnaw hah na ca awh han.
20 amma in kuka yi tsayayya kuka kuma yi tayarwa, za a kashe ku da takobi.” Ni Ubangiji na faɗa.
Hatei na taran awh pawiteh, tahloi hoi na due awh han telah BAWIPA e pahni ni a dei toe a ti.
21 Dubi yadda amintacciyar birni ta zama karuwa! Dā ta cika da yin gaskiya; dā masu adalci a can suke zama, amma yanzu sai masu kisankai kaɗai!
Yuemkamcu e kho teh bangtelamaw ka kâyawt e kho lah a kangcoung vaw. Ahmaloe teh, kângingnae hoi ka kawi e, a thung lannae ni hmuen a la e lah ao ei, atuteh tamikathetnaw ni hmuen lanae lah ao toe.
22 Azurfarki ta zama jebu, an gauraye ruwan inabinki mafi kyau da ruwa.
Na tangka hai a ei lah ao toe. Na misurtui hai tui hoi a kâkalawt toe.
23 Masu mulkinki’yan tawaye ne, abokan ɓarayi; dukansu suna ƙaunar cin hanci suna bin kyautai. Ba sa taɓa tsare marayu a ɗakin shari’a; ba sa taimakon gwauruwa.
Na khobawinaw teh, taran lah a thaw toe. Tamrunaw e hui lah ao awh toe. Hote bawinaw pueng ni tadawnghno a ngai awh teh, tawknae phu dueng a pâlei awh. Naranaw hah khenyawn awh hoeh. Lahmainunaw teh banglahai ngâi awh hoeh.
24 Saboda haka Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, Mai Iko nan na Isra’ila, ya furta, “Kai, zan sami hutu daga maƙiyana in kuma yi ramuwa a kan abokan gābana.
Hatdawkvah, Isarelnaw e Athakaawme, ransahu Bawipa Jehovah ni a dei e teh, Aya! Kai na ka taran e naw hah bat ka takhoe vaiteh, ka tarannaw koe moi ka pathung han.
25 Zan juye hannuna a kanki; zan wanke ke sarai in fitar da dukan ƙazantarki.
Nang hah na kuet vaiteh, a ei hoi khoeroe na thoungsak vaiteh, thounghoehnae pueng ka takhoe han.
26 Zan maido da alƙalanki kamar yadda suke a dā can, mashawartanki kamar yadda suke da fari. Bayan haka za a ce da ke Birnin Masu Adalci, Amintacciyar Birni.”
Lawkcengkungnaw hoi pouknae kapoekung naw hah, ahmaloe ka ta e patetlah bout ka ta han. Hathnukkhu lannae khopui, yuemkamcu e khopui ati awh han.
27 Za a fanshi Sihiyona da adalci, masu tubanta kuma da aikin gaskiya.
Zion teh kângingnae hoi thoseh, lannae hoi thoseh ratang lah ao han.
28 Amma za a karye’yan tawaye da masu zunubi, waɗanda suka rabu da Ubangiji kuma za su hallaka.
Kâtapoe e hoi ka yon e tami teh reirei raphoe lah ao han. Cathut ka cettakhai e teh hraba mueng ka yawng lah hmaisawi han.
29 “Za ku ji kunya saboda masujadan ƙarƙashin itatuwan oak da kuka yi farin ciki; za a kunyata ku saboda lambun da kuka zaɓa.
Na doun e kathenkungnaw hah na kayakkhai awh toung vaiteh, na kârawi e takha ni kângai lah a ru sak awh han. Minhmai mathoe na poe awh han.
30 Za ku zama kamar itacen oak mai busasshen ganyaye, kamar lambu marar ruwa.
Bangkongtetpawiteh, a hna kamyai e kathen kung hoi tui kahak e takha patetlah lah na o awh han.
31 Mutum mai ƙarfi zai zama kamar rama, aikinsa kuma kamar tartsatsin wuta; duka za su ƙone tare, ba kuwa wanda zai kashe wutar.”
Athakaawme taminaw teh ngun ei patetlah awm vaiteh, a tawksak e teh hmaitali patetlah ao han. Hottaroi teh reirei kang vaiteh, hote hmai hah apinihai padout mahoeh.