< Ishaya 9 >

1 Duk da haka, babu sauran baƙin ciki ga waɗanda suke shan azaba. Dā ya ƙasƙantar da ƙasar kabilan Zebulun da ƙasar Naftali, amma nan gaba zai girmama Galili na Al’ummai, ta hanyar teku wadda take ta Urdun.
اما این تاریکی برای قوم خدا که در تنگی هستند تا ابد باقی نخواهد ماند. خدا سرزمین قبایل زبولون و نفتالی را در گذشته خوار و ذلیل ساخته بود، اما در آینده او تمام این سرزمین را از دریای مدیترانه گرفته تا آن سوی اردن و تا خود جلیل که بیگانگان در آن زندگی می‌کنند، مورد احترام قرار خواهد داد.
2 Mutanen da suke tafiya cikin duhu sun ga babban haske; a kan waɗanda suke zama a ƙasar inuwar mutuwa haske ya haskaka.
مردمانی که در تاریکی راه می‌روند، نوری عظیم خواهند دید، و بر آنان که در دیار ظلمت غلیظ ساکن بودند، نوری خواهد تابید.
3 Ka fadada al’umma ka kuma ƙara farin cikinsu; suna farin ciki a gabanka yadda mutane sukan yi murna a lokacin girbi, kamar yadda mutane sukan yi farin ciki sa’ad da suke raba ganima.
ای خداوند، تو خوشی قوم خود را افزودی و به ایشان شادمانی بخشیدی. آنها همچون کسانی که با شادی محصول را درو می‌کنند، و مانند آنانی که با خوشحالی غنایم را بین خود تقسیم می‌نمایند، در حضور تو شادمانی می‌کنند.
4 Gama kamar yadda yake a kwanakin da aka ci Midiyan da yaƙi, kuka ji tsoro nauyin da ya nawaita musu, sandar da yake a kafaɗunsu, sandar masu zaluncinsu.
زیرا تو یوغی را که بر گردن آنها بود شکستی و ایشان را از دست قوم تجاوزگر رهانیدی، همچنانکه در گذشته مدیانی‌ها را شکست داده، قومت را آزاد ساختی.
5 Kowane takalmin jarumin da aka yi amfani da shi a yaƙi da kuma kowane rigar da ka naɗe cikin jini zai kasance an ƙone shi zai kuma zama abin hura wuta.
تمام اسلحه‌ها و لباسهای جنگی که به خون آغشته‌اند خواهند سوخت و از بین خواهند رفت.
6 Gama a gare mu an haifa mana yaro, a gare mu an ba da ɗa, gwamnati za tă kasance a kafaɗarsa. Za a ce da shi Mashawarci Mai Banmamaki, Allah Maɗaukaki Uban Madawwami, Sarkin Salama.
زیرا فرزندی برای ما به دنیا آمده! پسری به ما بخشیده شده! او بر ما سلطنت خواهد کرد. نام او «عجیب»، «مشیر»، «خدای قدیر»، «پدر جاودانی» و «سرور سلامتی» خواهد بود.
7 Game da girmar gwamnatinsa da salama babu iyaka. Zai gāji sarki Dawuda, yă yi mulki a matsayinsa, zai kafa mulkinsa a kan adalci da gaskiya, tun daga yanzu har zuwa ƙarshen zamani. Ubangiji Maɗaukaki ne ya yi niyyar aikata wannan duka.
او بر تخت پادشاهی داوود خواهد نشست و بر سرزمین او تا ابد سلطنت خواهد کرد. پایهٔ حکومتش را بر عدل و انصاف استوار خواهد ساخت، و گسترش فرمانروایی صلح‌پرور او را انتهایی نخواهد بود. خداوند لشکرهای آسمان چنین اراده فرموده و این را انجام خواهد داد.
8 Ubangiji ya aika da saƙon gāba da Yaƙub; zai auka wa Isra’ila.
خداوند برضد خاندان یعقوب سخن گفته، او قوم اسرائیل را مجازات خواهد کرد،
9 Dukan mutane za su san shi, Efraim da mazaunan Samariya, waɗanda suke magana da fariya suna kuma ɗaga kai,
و تمام قوم که در سامره و سایر شهرها هستند خواهند فهمید که او این کار را کرده است؛ زیرا این قوم مغرور شده‌اند و می‌گویند:
10 “Tubalai sun zube a ƙasa, amma za mu sāke gina su da dutse; an sassare itatuwan ɓaure, amma za mu maya su da al’ul.”
«هر چند خشتهای خانه‌های ما ریخته، ولی با سنگها آنها را بازسازی خواهیم کرد. هر چند درختان انجیر ما بریده شده‌اند، اما به جای آنها درختان سرو خواهیم کاشت.»
11 Amma Ubangiji ya ƙarfafa maƙiyan Rezin gāba da su ya kuma ingiza abokan gāba.
خداوند دشمنان اسرائیل را علیه او برانگیخته است.
12 Arameyawa daga gabas da Filistiyawa daga yamma sun cinye Isra’ila da buɗaɗɗen baki. Duk da haka, fushinsa bai huce ba, hannunsa har yanzu yana a miƙe.
او سوری‌ها را از شرق و فلسطینی‌ها را از غرب فرستاده تا اسرائیل را ببلعند. با این حال، خشم خداوند فروکش نکرده و دست او همچنان برای مجازات دراز است.
13 Amma mutanen ba su juyo wurin wanda ya buge su ba, balle su nemi Ubangiji Maɗaukaki.
اما اسرائیل توبه نمی‌کند و به سوی خداوند لشکرهای آسمان برنمی‌گردد.
14 Saboda haka Ubangiji zai yanke Isra’ila kai da wutsiya, da reshen dabino da iwa a rana guda;
بنابراین، خداوند در یک روز مردم اسرائیل و رهبرانشان را مجازات خواهد کرد و سر و دم این قوم را خواهد برید!
15 dattawa da manyan mutane su ne kai, annabawa waɗanda suke koyar da ƙarairayi su ne wutsiya.
ریش‌سفیدان و اشراف اسرائیل سر قوم هستند و انبیای کاذبش دم آن.
16 Waɗanda suke jagorar wannan mutane suna ɓad da su, su ne waɗanda ake jagora aka sa suka kauce.
اینها که هادیان قوم هستند قوم را به گمراهی و نابودی کشانده‌اند.
17 Saboda haka Ubangiji ba zai ji daɗin matasa ba, ba kuwa zai ji tausayin marayu da gwauraye ba, gama kowa marar sanin Allah ne da kuma mugu, kowane baki yana faɗin mugayen maganganu. Duk da haka, fushinsa bai huce ba, hannunsa har yanzu yana a miƙe.
خداوند جوانانشان را مجازات خواهد کرد و حتی بر بیوه‌زنان و یتیمانشان نیز رحم نخواهد نمود، زیرا همهٔ ایشان خدانشناس و شرور و دروغگو هستند. به این سبب است که هنوز خشم خدا فروکش نکرده و دست او برای مجازات ایشان دراز است.
18 Tabbatacce mugunta tana ƙuna kamar wuta; tana cin ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya, ta sa wuta a jeji mai itatuwa masu yawa, don yă yi murtuke hayaƙi har zuwa sama.
شرارت این قوم باعث شده غضب خداوند لشکرهای آسمان افروخته گردد و مانند آتشی که خار و خس را می‌سوزاند و تمام جنگل را فرا می‌گیرد و دود غلیظی به آسمان می‌فرستد، همه را بسوزاند. مردم مانند هیزم می‌سوزند و حتی برادر به برادر کمک نمی‌کند.
19 Ta wurin fushin Ubangiji Maɗaukaki ƙasar za tă ci wuta mutane kuma za su zama abin hura wutar, babu wanda zai ji tausayin ɗan’uwansa.
20 A dama za su ci, amma su ci gaba da jin yunwa; a hagu za su ci, amma ba za su ƙoshi ba. Kowa zai mai da naman’ya’yansa abinci.
لقمه را از دست یکدیگر می‌قاپند و می‌خورند اما سیر نمی‌شوند. از شدت گرسنگی حتی بچه‌های خودشان را نیز می‌خورند!
21 Manasse zai mai da Efraim abinci, Efraim kuma yă cinye Manasse; tare za su yi gāba da Yahuda. Duk da haka, fushinsa bai huce ba, hannunsa har yanzu yana a miƙe.
قبیلهٔ منسی و قبیلهٔ افرایم بر ضد یکدیگر، و هر دو بر ضد یهودا برخاسته‌اند. ولی با وجود این خشم خداوند فروکش نمی‌کند و دست او هنوز برای مجازات ایشان دراز است.

< Ishaya 9 >