< Ishaya 9 >

1 Duk da haka, babu sauran baƙin ciki ga waɗanda suke shan azaba. Dā ya ƙasƙantar da ƙasar kabilan Zebulun da ƙasar Naftali, amma nan gaba zai girmama Galili na Al’ummai, ta hanyar teku wadda take ta Urdun.
Bet tumsība nepaliks, kur (tagad) bēdas; pirmajā laikā Viņš kaunā licis Zebulona zemi un Naftalus zemi, bet pastara laikā Viņš cels godā jūrmalu, AizJardāni un pagānu Galileju.
2 Mutanen da suke tafiya cikin duhu sun ga babban haske; a kan waɗanda suke zama a ƙasar inuwar mutuwa haske ya haskaka.
Tie ļaudis, kas staigā tumsībā, redz lielu gaišumu; kas dzīvo nāves ēnas zemē, pār tiem spīd spožums.
3 Ka fadada al’umma ka kuma ƙara farin cikinsu; suna farin ciki a gabanka yadda mutane sukan yi murna a lokacin girbi, kamar yadda mutane sukan yi farin ciki sa’ad da suke raba ganima.
To tautu Tu esi vairojis; lielu prieku Tu tai esi devis; tie priecāsies Tavā priekšā, tā kā priecājās pļaujamā laikā, tā kā līksmojās laupījumu dalot.
4 Gama kamar yadda yake a kwanakin da aka ci Midiyan da yaƙi, kuka ji tsoro nauyin da ya nawaita musu, sandar da yake a kafaɗunsu, sandar masu zaluncinsu.
Jo viņu nastas jūgu un viņu muguras rīksti un viņu dzinēja dzenuli Tu esi salauzis kā Midijana laikā.
5 Kowane takalmin jarumin da aka yi amfani da shi a yaƙi da kuma kowane rigar da ka naɗe cikin jini zai kasance an ƙone shi zai kuma zama abin hura wuta.
Jo kurpes, autas uz kara troksni, un drēbes, apgānītas asinīm, taps sadedzinātas un no uguns aprītas.
6 Gama a gare mu an haifa mana yaro, a gare mu an ba da ɗa, gwamnati za tă kasance a kafaɗarsa. Za a ce da shi Mashawarci Mai Banmamaki, Allah Maɗaukaki Uban Madawwami, Sarkin Salama.
Jo viens bērns mums dzimis, viens dēls mums dots, un valdība ir uz Viņa kamieša; un Viņa vārds top saukts: Brīnums, Padoma devējs, Varenais Dievs, Mūžīgais tēvs, Miera lielkungs.
7 Game da girmar gwamnatinsa da salama babu iyaka. Zai gāji sarki Dawuda, yă yi mulki a matsayinsa, zai kafa mulkinsa a kan adalci da gaskiya, tun daga yanzu har zuwa ƙarshen zamani. Ubangiji Maɗaukaki ne ya yi niyyar aikata wannan duka.
Lai valdība top vairota, un mieram nav gala uz Dāvida goda krēsla un Viņa valstībā, ka Viņš to sataisa un stiprina ar tiesu un taisnību no šī laika mūžīgi. To darīs Tā Kunga Cebaot karstums.
8 Ubangiji ya aika da saƙon gāba da Yaƙub; zai auka wa Isra’ila.
Tas Kungs vienu vārdu ir sūtījis pie Jēkaba, un tas ir nolaidies pie Israēla.
9 Dukan mutane za su san shi, Efraim da mazaunan Samariya, waɗanda suke magana da fariya suna kuma ɗaga kai,
Un visi ļaudis to samanīs, Efraīms un Samarijas iedzīvotāji, kas lielībā un sirds lepnībā saka:
10 “Tubalai sun zube a ƙasa, amma za mu sāke gina su da dutse; an sassare itatuwan ɓaure, amma za mu maya su da al’ul.”
Ķieģeļi gruvuši, bet ar cirstiem akmeņiem atkal uztaisīsim, meža vīģu koki ir nocirsti, bet viņu vietā stādīsim ciedru kokus.
11 Amma Ubangiji ya ƙarfafa maƙiyan Rezin gāba da su ya kuma ingiza abokan gāba.
Jo Tas Kungs paaugstina Recina pretiniekus pār viņu un saskubina viņa ienaidniekus,
12 Arameyawa daga gabas da Filistiyawa daga yamma sun cinye Isra’ila da buɗaɗɗen baki. Duk da haka, fushinsa bai huce ba, hannunsa har yanzu yana a miƙe.
Sīriešus no rītiem un Fīlistus no vakariem, ka tie Israēli ēd pilnā mutē. Ar visu to Viņa dusmība nenovēršas, un Viņa roka vēl ir izstiepta.
13 Amma mutanen ba su juyo wurin wanda ya buge su ba, balle su nemi Ubangiji Maɗaukaki.
Bet tie ļaudis negriežas pie Tā, kas tos sit, un nemeklē To Kungu Cebaot.
14 Saboda haka Ubangiji zai yanke Isra’ila kai da wutsiya, da reshen dabino da iwa a rana guda;
Tādēļ Tas Kungs nocirtīs no Israēla galvu un asti, zaru un celmu vienā dienā.
15 dattawa da manyan mutane su ne kai, annabawa waɗanda suke koyar da ƙarairayi su ne wutsiya.
Vecaji un augstie ir tā galva, bet pravietis, kas melus māca, tā aste.
16 Waɗanda suke jagorar wannan mutane suna ɓad da su, su ne waɗanda ake jagora aka sa suka kauce.
Jo šo ļaužu vadoņi ir viltnieki, un kas no tiem top vadīti, tie iet bojā.
17 Saboda haka Ubangiji ba zai ji daɗin matasa ba, ba kuwa zai ji tausayin marayu da gwauraye ba, gama kowa marar sanin Allah ne da kuma mugu, kowane baki yana faɗin mugayen maganganu. Duk da haka, fushinsa bai huce ba, hannunsa har yanzu yana a miƙe.
Tādēļ Tas Kungs par viņu jaunekļiem nepriecāsies un neapžēlosies par viņu bāriņiem un atraitnēm, jo tie visi ir blēži un ļaundari, un ikviena mute runā blēņas. Ar visu to Viņa dusmība nenovēršas, un Viņa roka vēl ir izstiepta.
18 Tabbatacce mugunta tana ƙuna kamar wuta; tana cin ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya, ta sa wuta a jeji mai itatuwa masu yawa, don yă yi murtuke hayaƙi har zuwa sama.
Jo bezdievība deg kā uguns un aprij ērkšķus un dadžus un aizdedzina mežu biezumus un augsti dūmi paceļas gaisā.
19 Ta wurin fushin Ubangiji Maɗaukaki ƙasar za tă ci wuta mutane kuma za su zama abin hura wutar, babu wanda zai ji tausayin ɗan’uwansa.
Jo caur Tā Kunga Cebaot bardzību zeme kvēlo, un ļaudis ir kā uguns barība, un viens otru nežēlo.
20 A dama za su ci, amma su ci gaba da jin yunwa; a hagu za su ci, amma ba za su ƙoshi ba. Kowa zai mai da naman’ya’yansa abinci.
Pa labo roku rij, un tomēr ir izsalkuši, un pa kreiso roku ēd, un tomēr nav paēduši, ikkatrs ēd sava elkoņa miesu,
21 Manasse zai mai da Efraim abinci, Efraim kuma yă cinye Manasse; tare za su yi gāba da Yahuda. Duk da haka, fushinsa bai huce ba, hannunsa har yanzu yana a miƙe.
Manasus Efraīmu, un Efraīms Manasu, un abi kopā pret Jūdu. Ar visu to Viņa dusmība nenovēršas, un Viņa roka vēl ir izstiepta.

< Ishaya 9 >