< Ishaya 9 >
1 Duk da haka, babu sauran baƙin ciki ga waɗanda suke shan azaba. Dā ya ƙasƙantar da ƙasar kabilan Zebulun da ƙasar Naftali, amma nan gaba zai girmama Galili na Al’ummai, ta hanyar teku wadda take ta Urdun.
In the earlier time, the land of Zebulun and the land of Naphtali were lifted up. But in the later time, the way of the sea beyond the Jordan, the Galilee of the Gentiles, was weighed down.
2 Mutanen da suke tafiya cikin duhu sun ga babban haske; a kan waɗanda suke zama a ƙasar inuwar mutuwa haske ya haskaka.
The people who walked in darkness have seen a great light. A light has risen for the inhabitants of the region of the shadow of death.
3 Ka fadada al’umma ka kuma ƙara farin cikinsu; suna farin ciki a gabanka yadda mutane sukan yi murna a lokacin girbi, kamar yadda mutane sukan yi farin ciki sa’ad da suke raba ganima.
You have increased the nation, but you have not increased the rejoicing. They will rejoice before you, like those who rejoice at the harvest, like the victorious exulting after capturing the prey, when they divide the spoils.
4 Gama kamar yadda yake a kwanakin da aka ci Midiyan da yaƙi, kuka ji tsoro nauyin da ya nawaita musu, sandar da yake a kafaɗunsu, sandar masu zaluncinsu.
For you have prevailed over the yoke of their burden, and over the rod of their shoulder, and over the scepter of their oppressor, as in the day of Midian.
5 Kowane takalmin jarumin da aka yi amfani da shi a yaƙi da kuma kowane rigar da ka naɗe cikin jini zai kasance an ƙone shi zai kuma zama abin hura wuta.
For every violent plunder with a tumult, and every garment mixed with blood, will be burned up and will become fuel for the fire.
6 Gama a gare mu an haifa mana yaro, a gare mu an ba da ɗa, gwamnati za tă kasance a kafaɗarsa. Za a ce da shi Mashawarci Mai Banmamaki, Allah Maɗaukaki Uban Madawwami, Sarkin Salama.
For unto us a child is born, and unto us a son is given. And leadership is placed upon his shoulder. And his name shall be called: wonderful Counselor, mighty God, father of the future age, Prince of Peace.
7 Game da girmar gwamnatinsa da salama babu iyaka. Zai gāji sarki Dawuda, yă yi mulki a matsayinsa, zai kafa mulkinsa a kan adalci da gaskiya, tun daga yanzu har zuwa ƙarshen zamani. Ubangiji Maɗaukaki ne ya yi niyyar aikata wannan duka.
His reign will be increased, and there will be no end to his peace. He will sit upon the throne of David and over his kingdom, to confirm and strengthen it, in judgment and justice, from now even unto eternity. The zeal of the Lord of hosts shall accomplish this.
8 Ubangiji ya aika da saƙon gāba da Yaƙub; zai auka wa Isra’ila.
The Lord sent a word to Jacob, and it fell upon Israel.
9 Dukan mutane za su san shi, Efraim da mazaunan Samariya, waɗanda suke magana da fariya suna kuma ɗaga kai,
And all the people of Ephraim will know it. And the inhabitants of Samaria will say it, in the arrogance and haughtiness of their heart:
10 “Tubalai sun zube a ƙasa, amma za mu sāke gina su da dutse; an sassare itatuwan ɓaure, amma za mu maya su da al’ul.”
“The bricks have fallen, but we will build with squared stones. They have cut down the sycamores, but we will replace them with cedars.”
11 Amma Ubangiji ya ƙarfafa maƙiyan Rezin gāba da su ya kuma ingiza abokan gāba.
And the Lord will raise up the enemies of Rezin over him, and he will turn his adversaries into a tumult:
12 Arameyawa daga gabas da Filistiyawa daga yamma sun cinye Isra’ila da buɗaɗɗen baki. Duk da haka, fushinsa bai huce ba, hannunsa har yanzu yana a miƙe.
the Syrians from the east and the Philistines from the west. And they will devour Israel with their whole mouth. After all this, his fury was not turned away; instead, his hand was still extended.
13 Amma mutanen ba su juyo wurin wanda ya buge su ba, balle su nemi Ubangiji Maɗaukaki.
And the people did not return to the One who struck them, and they did not seek the Lord of hosts.
14 Saboda haka Ubangiji zai yanke Isra’ila kai da wutsiya, da reshen dabino da iwa a rana guda;
And so, the Lord will disperse, away from Israel, the head and the tail, he who bows down and he who refrains, in one day.
15 dattawa da manyan mutane su ne kai, annabawa waɗanda suke koyar da ƙarairayi su ne wutsiya.
The long-lived and honorable, he is the head; and the prophet who teaches lies, he is the tail.
16 Waɗanda suke jagorar wannan mutane suna ɓad da su, su ne waɗanda ake jagora aka sa suka kauce.
And those who deceitfully praise this people, and those who are praised, will be thrown down violently.
17 Saboda haka Ubangiji ba zai ji daɗin matasa ba, ba kuwa zai ji tausayin marayu da gwauraye ba, gama kowa marar sanin Allah ne da kuma mugu, kowane baki yana faɗin mugayen maganganu. Duk da haka, fushinsa bai huce ba, hannunsa har yanzu yana a miƙe.
For this reason, the Lord will not rejoice over their youths. And he will not take pity on their orphans and widows. For each one is a hypocrite, and each one is wicked, and every mouth has spoken foolishness. After all this, his fury was not turned away; instead, his hand was still extended.
18 Tabbatacce mugunta tana ƙuna kamar wuta; tana cin ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya, ta sa wuta a jeji mai itatuwa masu yawa, don yă yi murtuke hayaƙi har zuwa sama.
For impiety has been kindled like a fire: it will devour brier and thorn, and it will burn in the dense forest, and it will be interwoven with the ascending smoke.
19 Ta wurin fushin Ubangiji Maɗaukaki ƙasar za tă ci wuta mutane kuma za su zama abin hura wutar, babu wanda zai ji tausayin ɗan’uwansa.
The earth has been shaken by the wrath of the Lord of hosts, and the people will become like fuel for the fire. A man will not spare his own brother.
20 A dama za su ci, amma su ci gaba da jin yunwa; a hagu za su ci, amma ba za su ƙoshi ba. Kowa zai mai da naman’ya’yansa abinci.
And he will turn toward the right, and he will be hungry. And he will eat toward the left, and he will not be satisfied. Each one will eat the flesh of his own arm: Manasseh Ephraim, and Ephraim Manasseh, and together they will be against Judah.
21 Manasse zai mai da Efraim abinci, Efraim kuma yă cinye Manasse; tare za su yi gāba da Yahuda. Duk da haka, fushinsa bai huce ba, hannunsa har yanzu yana a miƙe.
After all this, his fury was not turned away; instead, his hand was still extended.