< Ishaya 9 >

1 Duk da haka, babu sauran baƙin ciki ga waɗanda suke shan azaba. Dā ya ƙasƙantar da ƙasar kabilan Zebulun da ƙasar Naftali, amma nan gaba zai girmama Galili na Al’ummai, ta hanyar teku wadda take ta Urdun.
A však ne tak obklíčí mrákota té země, kteráž ssoužena bude, jako když se ponejprv nepřítel dotkl země Zabulon a země Neftalím, ani jako potom, když více obtíží, naproti moři, při Jordánu Galilei lidnou.
2 Mutanen da suke tafiya cikin duhu sun ga babban haske; a kan waɗanda suke zama a ƙasar inuwar mutuwa haske ya haskaka.
Nebo lid tento chodě v temnostech, uzří světlo veliké, a bydlícím v zemi stínu smrti světlo zastkví se.
3 Ka fadada al’umma ka kuma ƙara farin cikinsu; suna farin ciki a gabanka yadda mutane sukan yi murna a lokacin girbi, kamar yadda mutane sukan yi farin ciki sa’ad da suke raba ganima.
Rozmnožil jsi tento národ, ale nezveličils veselé. A však veseliti se budou před tebou, tak jako se veselí ve žni, jako se radují, když dělí kořisti,
4 Gama kamar yadda yake a kwanakin da aka ci Midiyan da yaƙi, kuka ji tsoro nauyin da ya nawaita musu, sandar da yake a kafaɗunsu, sandar masu zaluncinsu.
Když jho břemene jeho a prut ramene jeho, hůl násilníka jeho polámeš, jako za dnů Madianských,
5 Kowane takalmin jarumin da aka yi amfani da shi a yaƙi da kuma kowane rigar da ka naɗe cikin jini zai kasance an ƙone shi zai kuma zama abin hura wuta.
Kdyžto všickni bojovníci předěšeni, a roucha ve krvi zbrocena, ano což hořeti mohlo, i ohněm spáleno.
6 Gama a gare mu an haifa mana yaro, a gare mu an ba da ɗa, gwamnati za tă kasance a kafaɗarsa. Za a ce da shi Mashawarci Mai Banmamaki, Allah Maɗaukaki Uban Madawwami, Sarkin Salama.
Nebo dítě narodilo se nám, syn dán jest nám, i bude knížetství na rameni jeho, a nazváno bude jméno jeho: Předivný, Rádce, Bůh silný, Rek udatný, Otec věčnosti, Kníže pokoje.
7 Game da girmar gwamnatinsa da salama babu iyaka. Zai gāji sarki Dawuda, yă yi mulki a matsayinsa, zai kafa mulkinsa a kan adalci da gaskiya, tun daga yanzu har zuwa ƙarshen zamani. Ubangiji Maɗaukaki ne ya yi niyyar aikata wannan duka.
K rozmnožování pak toho knížetství a pokoje, jemuž nebude konce, sedne na stolici Davidově, a na království jeho, až je i v řád uvede, a utvrdí v soudu a v spravedlnosti, od tohoto času až na věky. Horlivost Hospodina zástupů to učiní.
8 Ubangiji ya aika da saƙon gāba da Yaƙub; zai auka wa Isra’ila.
Slovo poslal Pán Jákobovi, a padlo v Izraeli.
9 Dukan mutane za su san shi, Efraim da mazaunan Samariya, waɗanda suke magana da fariya suna kuma ɗaga kai,
A zvíť všecken lid, Efraim, i obyvatelé Samařští, kteříž v pýše a vysokomyslnosti srdce říkají:
10 “Tubalai sun zube a ƙasa, amma za mu sāke gina su da dutse; an sassare itatuwan ɓaure, amma za mu maya su da al’ul.”
Padly cihly, ale my tesaným kamenem stavěti budeme; planí fíkové podťati jsou, a my to v cedry směníme.
11 Amma Ubangiji ya ƙarfafa maƙiyan Rezin gāba da su ya kuma ingiza abokan gāba.
Ale zvýší Hospodin protivníky Rezinovy nad něj, a nepřátely jeho svolá,
12 Arameyawa daga gabas da Filistiyawa daga yamma sun cinye Isra’ila da buɗaɗɗen baki. Duk da haka, fushinsa bai huce ba, hannunsa har yanzu yana a miƙe.
Syrské po předu, a Filistinské po zadu. I budou žráti Izraele celými ústy, aniž ve všem tom odvrátí se prchlivost jeho, ale ruka jeho předce bude vztažená.
13 Amma mutanen ba su juyo wurin wanda ya buge su ba, balle su nemi Ubangiji Maɗaukaki.
Protože se lid ten nenavrací k tomu, kterýž jej bije, a Hospodina zástupů nehledají,
14 Saboda haka Ubangiji zai yanke Isra’ila kai da wutsiya, da reshen dabino da iwa a rana guda;
Protož odetne Hospodin od Izraele hlavu i ocas, ratolest i sítí jednoho dne.
15 dattawa da manyan mutane su ne kai, annabawa waɗanda suke koyar da ƙarairayi su ne wutsiya.
(Stařec a vzácný člověk, onť jest hlava, prorok pak, kterýž učí lži, onť jest ocas.)
16 Waɗanda suke jagorar wannan mutane suna ɓad da su, su ne waɗanda ake jagora aka sa suka kauce.
Nebo vůdcové lidu tohoto jsou svůdcové, a kteříž se jim vésti dadí, zhynuli.
17 Saboda haka Ubangiji ba zai ji daɗin matasa ba, ba kuwa zai ji tausayin marayu da gwauraye ba, gama kowa marar sanin Allah ne da kuma mugu, kowane baki yana faɗin mugayen maganganu. Duk da haka, fushinsa bai huce ba, hannunsa har yanzu yana a miƙe.
Protož z mládenců jeho nepotěší se Pán, a nad sirotky a vdovami jeho neslituje se; nebo všickni jsou pokrytci a zločinci, a každá ústa mluví nešlechetnost. Aniž ve všem tom odvrátí se prchlivost jeho, ale předce ruka jeho bude vztažená.
18 Tabbatacce mugunta tana ƙuna kamar wuta; tana cin ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya, ta sa wuta a jeji mai itatuwa masu yawa, don yă yi murtuke hayaƙi har zuwa sama.
Nebo roznícena jsouc jako oheň bezbožnost, bodláčí a trní pálí, potom zapálí i houště lesu; pročež rozptýleni budou jako dým u povětří.
19 Ta wurin fushin Ubangiji Maɗaukaki ƙasar za tă ci wuta mutane kuma za su zama abin hura wutar, babu wanda zai ji tausayin ɗan’uwansa.
Pro hněv Hospodina zástupů zatmí se země, a ten lid bude jako pokrm ohně. Žádný ani bratra svého šanovati nebude,
20 A dama za su ci, amma su ci gaba da jin yunwa; a hagu za su ci, amma ba za su ƙoshi ba. Kowa zai mai da naman’ya’yansa abinci.
Ale krájeje sobě po pravé straně, však lačněti bude, a zžíraje po levé, však nenasytí se. Jeden každý maso ramene svého žráti bude,
21 Manasse zai mai da Efraim abinci, Efraim kuma yă cinye Manasse; tare za su yi gāba da Yahuda. Duk da haka, fushinsa bai huce ba, hannunsa har yanzu yana a miƙe.
Manasses Efraima a Efraim Manessesa, oba pak spolu proti Judovi budou. Ve všem tom však neodvrátí se prchlivost jeho, ale předce ruka jeho bude vztažená.

< Ishaya 9 >