< Ishaya 8 >
1 Ubangiji ya ce mini, “Ka ɗauki naɗaɗɗen littafi mai girma ka yi rubutu a kai da alƙalami kurum, Maher-Shalal-Hash-Baz.
И рече ми Господ: Узми књигу велику и напиши у њој писмом човечјим: Брз на плен, хитар на грабеж.
2 Zan kuma kira Uriya firist da Zakariya ɗan Yeberekiya su zama mini amintattun shaidu.”
И узех верне сведоке, Урију свештеника и Захарију сина Јеверехијиног.
3 Sa’an nan na tafi na yi jima’i da annabiya, ta kuwa yi ciki ta haifi ɗa. Ubangiji kuma ya ce mini, “Raɗa masa suna, Maher-Shalal-Hash-Baz.
Потом приступих к пророчици, и она затрудне и роди сина. А Господ ми рече: Надени му име: Брз на плен, хитар на грабеж.
4 Kafin yaron yă san yadda zai ce ‘Babana’ ko ‘Mamana,’ sarkin Assuriya zai kwashe arzikin Damaskus da ganimar Samariya.”
Јер пре него дете научи викати: Оче мој и мајко моја, однеће се благо дамаштанско и плен самаријски пред царем асирским.
5 Ubangiji ya sāke yi mini magana ya ce,
И још ми рече Господ говорећи:
6 “Domin wannan jama’a ta ƙi natsattsen ruwan rafin Shilowa suka yi ta farin ciki a kan Rezin ɗan Remaliya,
Што овај народ не мари за воду силоамску која тече тихо, и радује се Ресину и сину Ремалијином,
7 saboda haka Ubangiji yana shirin yă kawo musu rigyawar ruwan Kogi, wato, sarkin Assuriya da dukan sojojinsa. Zai cika dukan gaɓoɓinsa, yă kuma malala har zuwa bakin kogi.
Зато, ево, Господ ће навести на њих воду из реке силну и велику, цара асирског и сву славу његову, те ће изаћи из свих потока својих, и тећи ће поврх свих брегова својих,
8 Yă yi ta malala har zuwa cikin Yahuda, yă shafe ta, yana ratsa ta ciki har yă kai kafaɗa. Fikafikansa da ya buɗe za su rufe fāɗin ƙasarka, Ya Immanuwel!”
И навалиће преко Јуде, плавиће и разливаће се и доћи до грла, и крила ће јој се раширити преко свеколике земље твоје, Емануило!
9 Ku yi kururuwar yaƙi, ku ƙasashe, ku kuma ji tsoro! Ku saurara, dukanku manisantan ƙasashe. Ku shirya don yaƙi, ku kuma ji tsoro!
Здружујте се, народи, али ћете се потрти; чујте сви који сте у далекој земљи: оружајте се, али ћете се потрти; оружајте се, али ћете се потрти.
10 Ku ƙirƙiro dabarunku, amma ba za su yi nasara ba; ku ƙulla shirye-shiryenku, amma ba za su yi amfani ba, gama Allah yana tare da mu.
Договарајте се, договор ће вам се разбити: реците реч, неће бити од ње ништа, јер је с нама Бог.
11 Ubangiji ya yi mini magana da hannunsa mai ƙarfi a kaina, yana yi mini gargaɗi kada in bi hanyar waɗannan mutane. Ya ce,
Јер ми овако рече Господ ухвативши ме за руку и опоменувши ме да не идем путем овог народа, говорећи:
12 “Kada ka kira wani abu makirci game da kome da waɗannan mutane suke kira makirci; kada ji tsoron abin da suke tsoro, kada kuma ka firgita game da shi.
Не говорите "Буна" кад год овај народ каже "Буна", и не бојте се чега се он боји, и не плашите се.
13 Ubangiji Maɗaukaki shi ne za ka ɗauka a matsayi mai tsarki, shi ne wanda za ka ji tsoro, shi ne za ka yi rawar jiki a gabansa,
Господа над војскама светите; и Он нека вам је страх и бојазан.
14 zai kuwa kasance a wuri mai tsarki; amma ga dukan gidajen Isra’ila zai zama dutsen da zai sa mutane su yi tuntuɓe dutse kuma da zai sa su fāɗi. Ga dukan mutanen Urushalima kuma zai zama tarko da raga.
И биће вам светиња, а камен за спотицање и стена за саблазан обема домовима Израиљевим, замка и мрежа становницима јерусалимским.
15 Yawancinsu za su yi tuntuɓe; za su fāɗi a kuwa ragargaza su, za a sa musu tarko a kuma kama su.”
И спотакнуће се многи и пашће и сатрће се, заплешће се и ухватиће се.
16 Ɗaura shaidar nan ta gargadi ka kuma yimƙe umarnin Allah a cikin almajiraina.
Свежи сведочанство, запечати закон мојим ученицима.
17 Zan saurari Ubangiji, wanda ya ɓoye fuskarsa daga gidan Yaƙub. Zan dogara gare shi.
Чекаћу дакле Господа, који је сакрио лице своје од дома Јаковљевог, и уздаћу се у Њ.
18 Ga ni, da yaran da Ubangiji ya ba ni. Mu alamu ne da shaidu a cikin Isra’ila daga Ubangiji Maɗaukaki, wanda yake zama a Dutsen Sihiyona.
Ево ја и деца коју ми је дао Господ јесмо знак и чудо Израиљу од Господа над војскама, који настава на гори Сиону.
19 Sa’ad da mutane suka ce muku ku nemi shawarar’yan bori da masu sihiri, waɗanda suke shaƙe murya har ba a jin abin da suke faɗi, bai kamata mutane su nemi shawara daga Allahnsu ba? Me zai sa ku nemi shawara daga matattu a madadin masu rai?
И ако вам кажу: Питајте враче и гатаре, који шапћу и мрмљају, реците: Не треба ли народ да пита Бога свог? Или ће питати мртве место живих?
20 Nemi umarnin Allah da kuma shaidar jan kunne. Duk wanda bai yi magana bisa ga wannan kalma ba, ba su da amfani.
Закон и сведочанство тражите. Ако ли ко не говори тако, њему нема зоре.
21 Cikin matsuwa da yunwa, za su yi ta kai komo ko’ina a ƙasar; sa’ad da suka ji yunwa, za su yi fushi su tā da idanu sama, su zagi sarkinsu da Allahnsu.
И ходиће по земљи потуцајући се и гладујући; и кад буде гладан, љутиће се и псовати цара свог и Бога свог горе.
22 Sa’an nan za su zura wa ƙasa idanu, abin da za su gani kawai shi ne matsuwa da duhu da kuma abin banrazana, za a kuma jefa su cikin baƙin duhu.
А кад погледа на земљу, а то невоља и мрак и тешка мука, и он загнан у таму.