< Ishaya 8 >
1 Ubangiji ya ce mini, “Ka ɗauki naɗaɗɗen littafi mai girma ka yi rubutu a kai da alƙalami kurum, Maher-Shalal-Hash-Baz.
UThixo wathi kimi, “Thatha isibhebhedu selitshe esikhulu ulobe kuso ngolimi olujwayelekileyo ukuthi: Maheri-Shalali-Hashi-Bhazi (okutsho ukuthi: abaphanga ukuhuquluza okuphangiweyo).
2 Zan kuma kira Uriya firist da Zakariya ɗan Yeberekiya su zama mini amintattun shaidu.”
Ngizabiza u-Uriya umphristi loZakhariya indodana kaJebherekhiya njengabofakazi bami abathembekileyo.”
3 Sa’an nan na tafi na yi jima’i da annabiya, ta kuwa yi ciki ta haifi ɗa. Ubangiji kuma ya ce mini, “Raɗa masa suna, Maher-Shalal-Hash-Baz.
Ngemva kwalokho ngaya kumphrofethikazi, wathatha isisu, wazala indodana. UThixo wasesithi kimi, “Mbize ngokuthi nguMaheri-Shalali-Hashi-Bhazi.
4 Kafin yaron yă san yadda zai ce ‘Babana’ ko ‘Mamana,’ sarkin Assuriya zai kwashe arzikin Damaskus da ganimar Samariya.”
Kuzakuthi umfana engakakwazi ukuthi ‘Ubaba’ loba ‘Umama,’ inotho yaseDamaseko lempahla ethunjwe eSamariya kuzathathwa yinkosi yase-Asiriya.”
5 Ubangiji ya sāke yi mini magana ya ce,
UThixo wakhuluma kimi futhi wathi:
6 “Domin wannan jama’a ta ƙi natsattsen ruwan rafin Shilowa suka yi ta farin ciki a kan Rezin ɗan Remaliya,
“Ngenxa yokuthi abantu laba sebewalile amanzi ageleza kuhle aseShilowa bethokozela uRezini lendodana kaRemaliya,
7 saboda haka Ubangiji yana shirin yă kawo musu rigyawar ruwan Kogi, wato, sarkin Assuriya da dukan sojojinsa. Zai cika dukan gaɓoɓinsa, yă kuma malala har zuwa bakin kogi.
ngakho-ke iNkosi isiseduze ukubalethela izikhukhula zamanzi ezilamandla, eziyinkosi yase-Asiriya lobukhosi bayo bonke, zivela eYufrathe. Azachithekela ngaphandle kwayo yonke imigelo yawo, ageleze phezu kwamakhumbi ayo wonke,
8 Yă yi ta malala har zuwa cikin Yahuda, yă shafe ta, yana ratsa ta ciki har yă kai kafaɗa. Fikafikansa da ya buɗe za su rufe fāɗin ƙasarka, Ya Immanuwel!”
afohlele koJuda, agcwale kulo, adlule phakathi kwalo efika entanyeni. Impiko zawo ezeluliweyo zizakwembesa ububanzi belizwe lakho, Awu, Emanuweli!”
9 Ku yi kururuwar yaƙi, ku ƙasashe, ku kuma ji tsoro! Ku saurara, dukanku manisantan ƙasashe. Ku shirya don yaƙi, ku kuma ji tsoro!
Hlabani umkhosi wempi lina zizwe, lichithwe! Lalelani lonke lina mazwe akude. Lungiselani impi, lichithwe! Lungiselani impi lichithwe!
10 Ku ƙirƙiro dabarunku, amma ba za su yi nasara ba; ku ƙulla shirye-shiryenku, amma ba za su yi amfani ba, gama Allah yana tare da mu.
Lungisani icebo lenu, kodwa kalisoze liphumelele: bumbani isu lenu, kodwa kaliyikuma, ngoba uNkulunkulu ulathi.
11 Ubangiji ya yi mini magana da hannunsa mai ƙarfi a kaina, yana yi mini gargaɗi kada in bi hanyar waɗannan mutane. Ya ce,
UThixo wakhuluma kimi isandla sakhe esilamandla siphezu kwami, engixwayisa ukuba ngingalandeli indlela yalababantu. Wathi:
12 “Kada ka kira wani abu makirci game da kome da waɗannan mutane suke kira makirci; kada ji tsoron abin da suke tsoro, kada kuma ka firgita game da shi.
“Ungabokuthi kungamacebo amabi konke abantu laba abathi kungamacebo amabi; ungakwesabi abakwesabayo njalo ungakuqhuqhi.
13 Ubangiji Maɗaukaki shi ne za ka ɗauka a matsayi mai tsarki, shi ne wanda za ka ji tsoro, shi ne za ka yi rawar jiki a gabansa,
UThixo uSomandla nguye okumele limazi engongcwele, nguye okumele limesabe, nguye okumele limqhuqhe.
14 zai kuwa kasance a wuri mai tsarki; amma ga dukan gidajen Isra’ila zai zama dutsen da zai sa mutane su yi tuntuɓe dutse kuma da zai sa su fāɗi. Ga dukan mutanen Urushalima kuma zai zama tarko da raga.
Uzakuba yisiphephelo; kodwa kuzo zombili izindlu zako-Israyeli uzakuba yilitshe elikhubekisa abantu ledwala elibenza bawe. Ebantwini baseJerusalema uzakuba yisifu lomjibila.
15 Yawancinsu za su yi tuntuɓe; za su fāɗi a kuwa ragargaza su, za a sa musu tarko a kuma kama su.”
Inengi labo lizakhubeka; bazakuwa bephuke, bazathiywa bathunjwe.”
16 Ɗaura shaidar nan ta gargadi ka kuma yimƙe umarnin Allah a cikin almajiraina.
Bopha ubufakazi besixwayiso, uqinise umthetho phakathi kwabafundi bakaNkulunkulu.
17 Zan saurari Ubangiji, wanda ya ɓoye fuskarsa daga gidan Yaƙub. Zan dogara gare shi.
Ngizamlindela uThixo, ofihlela indlu kaJakhobe ubuso bakhe. Ngizabeka ithemba lami kuye.
18 Ga ni, da yaran da Ubangiji ya ba ni. Mu alamu ne da shaidu a cikin Isra’ila daga Ubangiji Maɗaukaki, wanda yake zama a Dutsen Sihiyona.
Mina ngilapha, kanye labantwana uThixo angiphe bona. Siyizibonakaliso lempawu ku-Israyeli ezivela kuThixo uSomandla, ohlala entabeni iZiyoni.
19 Sa’ad da mutane suka ce muku ku nemi shawarar’yan bori da masu sihiri, waɗanda suke shaƙe murya har ba a jin abin da suke faɗi, bai kamata mutane su nemi shawara daga Allahnsu ba? Me zai sa ku nemi shawara daga matattu a madadin masu rai?
Nxa abantu bekutshela ukuthi buza abalamadlozi labalemimoya yobuthakathi, labanyenyezayo bengunguza, kambe abantu akumelanga babuzisise uNkulunkulu wabo na? Kungani abaphilayo libabuzela kwabafayo na?
20 Nemi umarnin Allah da kuma shaidar jan kunne. Duk wanda bai yi magana bisa ga wannan kalma ba, ba su da amfani.
Emthethweni lakubo ubufakazi! Nxa bengakhulumi ngokumayelana lelizwi leli, kabalakho ukukhanya kokusa.
21 Cikin matsuwa da yunwa, za su yi ta kai komo ko’ina a ƙasar; sa’ad da suka ji yunwa, za su yi fushi su tā da idanu sama, su zagi sarkinsu da Allahnsu.
Bazazula lelizwe behlulukelwe, belambile. Lapho sebephalwe yindlala, bazathukuthela, bathuke inkosi yabo loNkulunkulu wabo bekhangele phezulu.
22 Sa’an nan za su zura wa ƙasa idanu, abin da za su gani kawai shi ne matsuwa da duhu da kuma abin banrazana, za a kuma jefa su cikin baƙin duhu.
Emva kwalokho bazakhangela emhlabeni babone usizi kuphela, lomnyama owesabekayo, njalo bazaphoselwa emnyameni opheleleyo.