< Ishaya 8 >
1 Ubangiji ya ce mini, “Ka ɗauki naɗaɗɗen littafi mai girma ka yi rubutu a kai da alƙalami kurum, Maher-Shalal-Hash-Baz.
Og HERREN sagde til mig: »Tag dig en stor Tavle og skriv derpaa med Menneskeskrift: Hurtigt-Bytte, Hastigt-Rov!
2 Zan kuma kira Uriya firist da Zakariya ɗan Yeberekiya su zama mini amintattun shaidu.”
Og tag mig paalidelige Vidner, Præsten Urija og Zekarja, Jeberekjahus Søn!«
3 Sa’an nan na tafi na yi jima’i da annabiya, ta kuwa yi ciki ta haifi ɗa. Ubangiji kuma ya ce mini, “Raɗa masa suna, Maher-Shalal-Hash-Baz.
Og jeg nærmede mig Profetinden, og hun blev frugtsommelig og fødte en Søn. Saa sagde HERREN til mig: »Kald ham Hurtigt-Bytte, Hastigt-Rov!
4 Kafin yaron yă san yadda zai ce ‘Babana’ ko ‘Mamana,’ sarkin Assuriya zai kwashe arzikin Damaskus da ganimar Samariya.”
Thi før Drengen kan sige Fader og Moder, skal Rigdommene fra Damaskus og Byttet fra Samaria bringes til Assyrerkongen!«
5 Ubangiji ya sāke yi mini magana ya ce,
Fremdeles sagde HERREN til mig:
6 “Domin wannan jama’a ta ƙi natsattsen ruwan rafin Shilowa suka yi ta farin ciki a kan Rezin ɗan Remaliya,
Eftersom dette Folk lader haant om Siloas sagte rindende Vande i Angst for Rezin og Remaljas Søn,
7 saboda haka Ubangiji yana shirin yă kawo musu rigyawar ruwan Kogi, wato, sarkin Assuriya da dukan sojojinsa. Zai cika dukan gaɓoɓinsa, yă kuma malala har zuwa bakin kogi.
se, saa lader Herren Flodens Vande, de vældige, store, oversvømme dem, Assyrerkongen og al hans Herlighed; over alle sine Bredder skal den gaa, trænge ud over alle sine Diger,
8 Yă yi ta malala har zuwa cikin Yahuda, yă shafe ta, yana ratsa ta ciki har yă kai kafaɗa. Fikafikansa da ya buɗe za su rufe fāɗin ƙasarka, Ya Immanuwel!”
styrte ind i Juda, skylle over, vælte frem og naa til Halsen; og dens udbredte Vinger skal fylde dit Land, saa vidt det naar — Immanuel!
9 Ku yi kururuwar yaƙi, ku ƙasashe, ku kuma ji tsoro! Ku saurara, dukanku manisantan ƙasashe. Ku shirya don yaƙi, ku kuma ji tsoro!
I Folkeslag, mærk jer det med Rædsel, lyt til, alle fjerne Lande: Rust jer, I skal ræddes, rust jer, I skal ræddes.
10 Ku ƙirƙiro dabarunku, amma ba za su yi nasara ba; ku ƙulla shirye-shiryenku, amma ba za su yi amfani ba, gama Allah yana tare da mu.
Læg Raad op, det skal dog briste, gør Aftale, det slaar dog fejl, thi — Immanuel!
11 Ubangiji ya yi mini magana da hannunsa mai ƙarfi a kaina, yana yi mini gargaɗi kada in bi hanyar waɗannan mutane. Ya ce,
Thi saa sagde HERREN til mig, da hans Haand greb mig med Vælde, og han advarede mig mod at vandre paa dette Folks Vej:
12 “Kada ka kira wani abu makirci game da kome da waɗannan mutane suke kira makirci; kada ji tsoron abin da suke tsoro, kada kuma ka firgita game da shi.
Kald ikke alt Sammensværgelse, hvad dette Folk kalder Sammensværgelse, frygt ikke, hvad det frygter, og ræddes ikke!
13 Ubangiji Maɗaukaki shi ne za ka ɗauka a matsayi mai tsarki, shi ne wanda za ka ji tsoro, shi ne za ka yi rawar jiki a gabansa,
Hærskarers HERRE, ham skal I holde hellig, han skal være eders Frygt, han skal være eders Rædsel.
14 zai kuwa kasance a wuri mai tsarki; amma ga dukan gidajen Isra’ila zai zama dutsen da zai sa mutane su yi tuntuɓe dutse kuma da zai sa su fāɗi. Ga dukan mutanen Urushalima kuma zai zama tarko da raga.
Han bliver en Helligdom, en Anstødssten og en Klippe til Fald for begge Israels Huse og en Snare og et Fangegarn for Jerusalems Indbyggere,
15 Yawancinsu za su yi tuntuɓe; za su fāɗi a kuwa ragargaza su, za a sa musu tarko a kuma kama su.”
og mange iblandt dem skal snuble, falde og kvæstes, fanges og hildes.
16 Ɗaura shaidar nan ta gargadi ka kuma yimƙe umarnin Allah a cikin almajiraina.
Bind Vidnesbyrdet til og sæt Segl for Læren i mine Disciples Sind!
17 Zan saurari Ubangiji, wanda ya ɓoye fuskarsa daga gidan Yaƙub. Zan dogara gare shi.
Jeg bier paa HERREN, han, som dølger sit Aasyn for Jakobs Hus, til ham staar mit Haab:
18 Ga ni, da yaran da Ubangiji ya ba ni. Mu alamu ne da shaidu a cikin Isra’ila daga Ubangiji Maɗaukaki, wanda yake zama a Dutsen Sihiyona.
Se, jeg og de Børn, HERREN gav mig, er Varsler og Tegn i Israel fra Hærskarers HERRE, som bor paa Zions Bjerg.
19 Sa’ad da mutane suka ce muku ku nemi shawarar’yan bori da masu sihiri, waɗanda suke shaƙe murya har ba a jin abin da suke faɗi, bai kamata mutane su nemi shawara daga Allahnsu ba? Me zai sa ku nemi shawara daga matattu a madadin masu rai?
Og siger de til eder: »Søg Genfærdene og Aanderne, som hvisker og mumler!« — skal et Folk ikke søge sin Gud, skal man søge de døde for de levende?
20 Nemi umarnin Allah da kuma shaidar jan kunne. Duk wanda bai yi magana bisa ga wannan kalma ba, ba su da amfani.
Nej! Til Læren og Vidnesbyrdet! Saaledes skal visselig de komme til at tale, som nu er uden Morgenrøde.
21 Cikin matsuwa da yunwa, za su yi ta kai komo ko’ina a ƙasar; sa’ad da suka ji yunwa, za su yi fushi su tā da idanu sama, su zagi sarkinsu da Allahnsu.
Han skal vanke om i Landet, trykket og hungrig. Og naar han hungrer, skal han blive rasende og bande sin Konge og sin Gud. Vender han sig til det høje,
22 Sa’an nan za su zura wa ƙasa idanu, abin da za su gani kawai shi ne matsuwa da duhu da kuma abin banrazana, za a kuma jefa su cikin baƙin duhu.
eller skuer han ud over Jorden, se, da er der Trængsel og Mørke, knugende Mulm; i Bælgmørke er han stødt ud.