< Ishaya 7 >

1 Sa’ad da Ahaz ɗan Yotam, ɗan Uzziya, yake sarkin Yahuda, Sarki Rezin na Aram da Feka ɗan Remaliya sarkin Isra’ila suka haura don su yaƙi Urushalima, amma ba su iya cinta da yaƙi ba.
II arriva, du temps d’Achaz, fils de Jotham, fils d’Ouzia, roi de Juda, que Recîn, roi de Syrie, de concert avec Pékah, fils de Remaliahou, roi d’Israël, marcha sur Jérusalem pour l’attaquer, mais ne put triompher d’elle.
2 Sai fa aka faɗa wa gidan Dawuda cewa, “Aram ya haɗa kansa da Efraim”; saboda haka zuciyar Ahaz da ta mutanensa suka firgita, sai ka ce itatuwa a kurmin da iska ta girgiza.
Quand la maison de David apprit cette nouvelle: "Le Syrien est venu camper avec Ephraïm," son cœur et le cœur de son peuple en frissonnèrent, comme les arbres d’une forêt frissonnent sous le vent.
3 Sai Ubangiji ya ce wa Ishaya, “Fita, kai da ɗanka Sheyar-Yashub, don ku sadu da Ahaz a ƙarshen wuriyar da take kawo ruwa daga Tafkin Tudu, a hanyar Filin Mai Wanki.
L’Eternel dit alors à Isaïe: "Rends-toi au-devant d’Achaz, toi et Chear-Yachoub, ton fils, vers l’extrémité du canal de la Piscine supérieure, sur la chaussée qui conduit au champ du Foulon.
4 Ka faɗa masa, ‘Ka yi hankali, ka natsu kada kuma ka ji tsoro ko ka damu, kada ka ji tsoron fushin sarki Rezin da na Aram da na ɗan Remaliya, ba wani abu mai hatsari ba ne, bai fi hayaƙin’yan ƙirare biyu da suke cin wuta ba.
Et tu lui diras: N’Aie garde de perdre ton calme, sois sans crainte et ne laisse pas défaillir ton cœur devant ces deux bouts de tisons fumeux devant la colère de Recin et d’Aram, et du fils de Remaliahou.
5 Aram, Efraim da ɗan Remaliya sun ƙulla maƙarƙashiya, suna cewa,
Puisque Aram a formé contre toi de mauvais desseins, ainsi qu’Ephraïm et le fils de Remaliahou, et qu’ils ont dit:
6 “Bari mu kai wa Yahuda hari; bari mu yayyage su mu rarraba su a tsakaninmu, mu naɗa Tabeyel sarki a kansu.”
"Marchons contre Juda, réduisons-le à l’extrémité, forçons-le de se rendre à nous, puis nous lui imposerons comme roi le fils de Tabeal,"
7 Duk da haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “‘Ba zai faru ba, ba zai auku ba,
ainsi a parlé le Seigneur-Elohim: Cela ne s’accomplira ni ne sera!"
8 gama kan Aram shi ne Damaskus, kan Damaskus kuma kawai shi ne Rezin. Cikin shekaru sittin da biyar za a wargaje Efraim har ba za tă iya rayuwa ta zama al’umma ba.
Car la tête d’Aram, c’est Damas, et la tète de Damas, c’est Recin; (or dans soixante-cinq ans, Ephraïrn, déchu, cessera d’être une nation).
9 Kan Efraim shi ne Samariya, kan Samariya kuma kawai shi ne ɗan Remaliya. In ba ku tsaya da ƙarfi cikin bangaskiyarku ba, ba za ku dawwama ba.’”
Et la tête d’Ephraïm, c’est Samarie, et la tête de Samarie, c’est le fils de Remaliahou. Si vous manquez de confiance, vous manquerez d’avenir."
10 Ubangiji ya kuma yi magana wa Ahaz ya ce,
L’Eternel, continuant de parler à Achaz, lui dit:
11 “Ka roƙi Ubangiji Allahnka yă ba ka alama, ko daga zurfafa masu zurfi ko kuwa daga can cikin sama.” (Sheol h7585)
"Demande un signe de la part de l’Eternel, ton Dieu, que ta demande s’applique aux régions d’en bas ou aux sphères supérieures. (Sheol h7585)
12 Amma Ahaz ya ce, “Ba zan nema ba; ba zan gwada Ubangiji ba.”
Je n’en demanderai pas, répliqua Achaz: je ne veux pas mettre l’Eternel à l’épreuve."
13 Sa’an nan Ishaya ya ce, “To, ku saurara, ya ku gidan Dawuda! Abin kirki kuke yi ne da kuka ƙure haƙurin jama’a? Ko haƙurin Allah ne kuma kuke so ku ƙure?
Alors le prophète reprit: "Ecoutez-donc, maison de David! Est-ce trop peu pour vous de lasser les hommes que vous vouliez encore lasser mon Dieu?
14 Saboda haka Ubangiji kansa zai ba ku alama. Ga shi budurwa za tă yi ciki, za tă haifi ɗa, za tă kuwa kira shi Immanuwel.
Ah certes! Le Seigneur vous donne de lui-même un signe: Voici, la jeune femme est devenue enceinte, elle va mettre au monde un fils, qu’elle appellera Immanouel.
15 In ya yi girma har ya isa yanke shawara don kansa, madara da zuma ne abincinsa.
Il se nourrira de crème et de miel, jusqu’à ce qu’il ait du discernement pour repousser le mal et choisir le bien.
16 Amma kafin yaron yă isa yanke shawara yă ƙi abin da yake mummuna, yă zaɓi abin da yake nagari, ƙasashen sarakunan nan biyu da kuke tsoro za su zama kango.
Or, avant même que l’enfant sache repousser le mal et choisir le bien, la région dont les deux rois te causent des angoisses sera devenue une solitude,
17 Ubangiji zai aukar maka da kwanakin wahala, kai da jama’arka, da dukan iyalin gidan sarauta, waɗanda suka fi muni tun lokacin da aka raba mulkin Efraim daga na Yahuda, zai kawo sarkin Assuriya.”
le Seigneur suscitera contre toi, contre ton peuple et la maison de ton père des jours tels qu’il n’y en a pas eu depuis qu’Ephraïm s’est séparé de Juda et cela grâce au roi d’Assyrie.
18 A wannan rana Ubangiji zai yi feɗuwa yă kira ƙudaje daga rafuffuka masu nisa na Masar da kuma ƙudan zuma daga ƙasar Assuriya.
En ce temps, le Seigneur appellera, par un sifflement, les moustiques qui sont sur les bords des canaux de l’Egypte et les frelons qui vivent en Assyrie;
19 Za su zo su mamaye kwazazzabai da kogwanni cikin duwatsu, a kan dukan ƙayayyuwa da dukan rammukan ruwa.
ils viendront s’abattre tous ensemble sur les vallons incultes, dans les fissures des rochers, dans tous les buissons et toutes les broussailles.
20 A wannan rana Ubangiji zai yi amfani da rezan da aka yi haya daga ƙetaren Kogi, sarkin Assuriya ke nan, yă aske kanku da gashin ƙafafunku, zai kuma aske gemunku.
En ce jour, le Seigneur, au moyen du rasoir pris en location sur les bords du fleuve par l’entremise du roi d’Assyrie coupera les cheveux de la tête et les poils des jambes; il fera tomber la barbe elle-même.
21 A ranar, mutum zai bar karsana ɗaya da awaki biyu da rai.
En ces temps, chaque individu pourra entretenir une génisse et deux brebis,
22 Kuma saboda yalwa madarar da suke bayarwa, zai kasance da madarar da zai sha. Dukan waɗanda suka rage a ƙasar za su sha madara da zuma.
et il en recueillera une telle quantité de lait qu’il se nourrira de crème. Oui, quiconque aura eu la vie sauve dans le pays pourra se nourrir de crème et de miel.
23 A wannan rana, a kowane wuri inda akwai kuringa dubu da kuɗinsu ya kai shekel dubu na azurfa, ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne kawai za su kasance a can.
Il arrivera encore, à la même époque, que tout terrain portant mille pieds de vigne d’une valeur de mille sicles, sera envahi par les ronces et les épines.
24 Mutane za su je can da baka da kibiyoyi, gama ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne za su rufe ƙasar.
On ne s’y rendra qu’armé de flèches et de carquois, tant le sol tout entier sera devenu la proie des ronces et des chardons.
25 Game da dukan tuddai da dā ake nome da garemani kuwa, ba za ku ƙara je wurin ba saboda tsoron ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya; za su zama wuraren da ake kai shanu a sake su su yi ta yawo da kansu, tumaki kuma su yi ta gudu.
Quant aux montagnes qu’on laboure au moyen de la bêche, on ne les abordera même pas, par crainte des ronces et des chardons; on y lâchera les bœufs, et elles seront foulées par les brebis.

< Ishaya 7 >