< Ishaya 7 >
1 Sa’ad da Ahaz ɗan Yotam, ɗan Uzziya, yake sarkin Yahuda, Sarki Rezin na Aram da Feka ɗan Remaliya sarkin Isra’ila suka haura don su yaƙi Urushalima, amma ba su iya cinta da yaƙi ba.
Aahaan, Jootamin pojan, Ussian pojanpojan, Juudan kuninkaan, aikana lähtivät Resin, Aramin kuningas, ja Pekah, Remaljan poika, Israelin kuningas, sotimaan Jerusalemia vastaan, mutta he eivät voineet valloittaa sitä.
2 Sai fa aka faɗa wa gidan Dawuda cewa, “Aram ya haɗa kansa da Efraim”; saboda haka zuciyar Ahaz da ta mutanensa suka firgita, sai ka ce itatuwa a kurmin da iska ta girgiza.
Ja kun Daavidin huoneelle ilmoitettiin sanoma: "Aram on leiriytynyt Efraimiin", niin kuninkaan ja hänen kansansa sydän vapisi, niinkuin metsän puut vapisevat tuulessa.
3 Sai Ubangiji ya ce wa Ishaya, “Fita, kai da ɗanka Sheyar-Yashub, don ku sadu da Ahaz a ƙarshen wuriyar da take kawo ruwa daga Tafkin Tudu, a hanyar Filin Mai Wanki.
Silloin Herra sanoi Jesajalle: "Mene Aahasta vastaan, sinä ja sinun poikasi Sear-Jaasub, Ylälammikon vesijohdon päähän, Vanuttajankedon tielle,
4 Ka faɗa masa, ‘Ka yi hankali, ka natsu kada kuma ka ji tsoro ko ka damu, kada ka ji tsoron fushin sarki Rezin da na Aram da na ɗan Remaliya, ba wani abu mai hatsari ba ne, bai fi hayaƙin’yan ƙirare biyu da suke cin wuta ba.
ja sano hänelle: Ole varuillasi ja pysy rauhallisena, älä pelkää, älköönkä sydämesi säikkykö noita kahta savuavaa kekäleenpätkää: Resinin ja Aramin ynnä Remaljan pojan vihanvimmaa.
5 Aram, Efraim da ɗan Remaliya sun ƙulla maƙarƙashiya, suna cewa,
Koska Aram, Efraim ja Remaljan poika ovat hankkineet pahaa sinua vastaan sanoen:
6 “Bari mu kai wa Yahuda hari; bari mu yayyage su mu rarraba su a tsakaninmu, mu naɗa Tabeyel sarki a kansu.”
'Lähtekäämme Juudaa vastaan, täyttäkäämme se kauhulla, vallatkaamme se itsellemme ja asettakaamme sinne kuninkaaksi Taabalin poika',
7 Duk da haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “‘Ba zai faru ba, ba zai auku ba,
niin sanoo Herra, Herra näin: Ei se onnistu, eikä se tapahdu.
8 gama kan Aram shi ne Damaskus, kan Damaskus kuma kawai shi ne Rezin. Cikin shekaru sittin da biyar za a wargaje Efraim har ba za tă iya rayuwa ta zama al’umma ba.
Sillä Aramin pää on Damasko, ja Damaskon pää on Resin-mutta kuusikymmentä viisi vuotta vielä, ja Efraim on muserrettu eikä ole enää kansa-ja Efraimin pää on Samaria,
9 Kan Efraim shi ne Samariya, kan Samariya kuma kawai shi ne ɗan Remaliya. In ba ku tsaya da ƙarfi cikin bangaskiyarku ba, ba za ku dawwama ba.’”
ja Samarian pää on Remaljan poika. Ellette usko, niin ette kestä."
10 Ubangiji ya kuma yi magana wa Ahaz ya ce,
Ja Herra puhui jälleen Aahaalle sanoen:
11 “Ka roƙi Ubangiji Allahnka yă ba ka alama, ko daga zurfafa masu zurfi ko kuwa daga can cikin sama.” (Sheol )
"Pyydä itsellesi merkki Herralta, Jumalaltasi, pyydä alhaalta syvyydestä taikka ylhäältä korkeudesta". (Sheol )
12 Amma Ahaz ya ce, “Ba zan nema ba; ba zan gwada Ubangiji ba.”
Mutta Aahas vastasi: "En pyydä enkä kiusaa Herraa".
13 Sa’an nan Ishaya ya ce, “To, ku saurara, ya ku gidan Dawuda! Abin kirki kuke yi ne da kuka ƙure haƙurin jama’a? Ko haƙurin Allah ne kuma kuke so ku ƙure?
Siihen hän lausui: "Kuulkaa, te Daavidin suku, eikö se riitä, että te ihmiset väsytätte, kun vielä minun Jumalanikin itseenne väsytätte?
14 Saboda haka Ubangiji kansa zai ba ku alama. Ga shi budurwa za tă yi ciki, za tă haifi ɗa, za tă kuwa kira shi Immanuwel.
Sentähden Herra itse antaa teille merkin: Katso, neitsyt tulee raskaaksi ja synnyttää pojan ja antaa hänelle nimen Immanuel.
15 In ya yi girma har ya isa yanke shawara don kansa, madara da zuma ne abincinsa.
Voita ja hunajaa hän syö siinä iässä, jolloin hän oppii hylkäämään pahan ja valitsemaan hyvän;
16 Amma kafin yaron yă isa yanke shawara yă ƙi abin da yake mummuna, yă zaɓi abin da yake nagari, ƙasashen sarakunan nan biyu da kuke tsoro za su zama kango.
sillä ennenkuin poika on oppinut hylkäämään pahan ja valitsemaan hyvän, tulee autioksi maa, jonka kahta kuningasta sinä kauhistut.
17 Ubangiji zai aukar maka da kwanakin wahala, kai da jama’arka, da dukan iyalin gidan sarauta, waɗanda suka fi muni tun lokacin da aka raba mulkin Efraim daga na Yahuda, zai kawo sarkin Assuriya.”
Herra antaa tulla sinulle, sinun kansallesi ja isäsi suvulle ne päivät, joita ei ole ollut siitä asti, kun Efraim luopui Juudasta-antaa tulla Assurin kuninkaan.
18 A wannan rana Ubangiji zai yi feɗuwa yă kira ƙudaje daga rafuffuka masu nisa na Masar da kuma ƙudan zuma daga ƙasar Assuriya.
Ja sinä päivänä Herra viheltää kärpäset Egyptin virtain suulta ja mehiläiset Assurin maasta,
19 Za su zo su mamaye kwazazzabai da kogwanni cikin duwatsu, a kan dukan ƙayayyuwa da dukan rammukan ruwa.
ja ne tulevat ja laskeutuvat kaikki vuorenrotkoihin ja kallionkoloihin, kaikkiin orjantappurapensaisiin ja kaikille juottopaikoille.
20 A wannan rana Ubangiji zai yi amfani da rezan da aka yi haya daga ƙetaren Kogi, sarkin Assuriya ke nan, yă aske kanku da gashin ƙafafunku, zai kuma aske gemunku.
Sinä päivänä Herra ajattaa virran tuolta puolen palkatulla partaveitsellä, Assurin kuninkaalla, pään ja häpykarvat; viepä se vielä parrankin.
21 A ranar, mutum zai bar karsana ɗaya da awaki biyu da rai.
Siihen aikaan pitää mies lehmäsen ja pari lammasta,
22 Kuma saboda yalwa madarar da suke bayarwa, zai kasance da madarar da zai sha. Dukan waɗanda suka rage a ƙasar za su sha madara da zuma.
mutta runsaan maidon tulon tähden hän syö voita; sillä voita ja hunajaa syövät kaikki maahan jäljelle jääneet.
23 A wannan rana, a kowane wuri inda akwai kuringa dubu da kuɗinsu ya kai shekel dubu na azurfa, ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne kawai za su kasance a can.
Ja siihen aikaan jokainen paikka, jossa kasvaa tuhat viinipuuta, arvoltaan tuhat hopeasekeliä, joutuu orjantappurain ja ohdakkeiden valtaan.
24 Mutane za su je can da baka da kibiyoyi, gama ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne za su rufe ƙasar.
Sinne on mentävä nuolet ja jousi mukana, sillä koko maa on pelkkää orjantappuraa ja ohdaketta.
25 Game da dukan tuddai da dā ake nome da garemani kuwa, ba za ku ƙara je wurin ba saboda tsoron ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya; za su zama wuraren da ake kai shanu a sake su su yi ta yawo da kansu, tumaki kuma su yi ta gudu.
Ei yhdellekään niistä vuorista, joita nyt kuokalla kuokitaan, enää mennä orjantappurain ja ohdakkeiden pelosta; ne jäävät härkien laitumeksi ja lammasten tallattavaksi."