< Ishaya 7 >

1 Sa’ad da Ahaz ɗan Yotam, ɗan Uzziya, yake sarkin Yahuda, Sarki Rezin na Aram da Feka ɗan Remaliya sarkin Isra’ila suka haura don su yaƙi Urushalima, amma ba su iya cinta da yaƙi ba.
And it comes to pass in the days of Ahaz, son of Jotham, son of Uzziah, king of Judah, [that] Rezin king of Aram, and Pekah, son of Remaliah, king of Israel, have gone up to Jerusalem, to battle against it, and he is not able to fight against it.
2 Sai fa aka faɗa wa gidan Dawuda cewa, “Aram ya haɗa kansa da Efraim”; saboda haka zuciyar Ahaz da ta mutanensa suka firgita, sai ka ce itatuwa a kurmin da iska ta girgiza.
And it is declared to the house of David, saying, “Aram has been led toward Ephraim,” and his heart and the heart of his people is moved, like the moving of trees of a forest by the presence of wind.
3 Sai Ubangiji ya ce wa Ishaya, “Fita, kai da ɗanka Sheyar-Yashub, don ku sadu da Ahaz a ƙarshen wuriyar da take kawo ruwa daga Tafkin Tudu, a hanyar Filin Mai Wanki.
And YHWH says to Isaiah, “Now go forth to meet Ahaz, you and your son Shear-Jashub, to the end of the conduit of the upper pool, to the highway of the fuller’s field,
4 Ka faɗa masa, ‘Ka yi hankali, ka natsu kada kuma ka ji tsoro ko ka damu, kada ka ji tsoron fushin sarki Rezin da na Aram da na ɗan Remaliya, ba wani abu mai hatsari ba ne, bai fi hayaƙin’yan ƙirare biyu da suke cin wuta ba.
and you have said to him: Take heed, and be quiet, do not fear, And do not let your heart be timid, Because of these two tails of smoking brands, For the fierceness of the anger of Rezin and Aram, And the son of Remaliah.
5 Aram, Efraim da ɗan Remaliya sun ƙulla maƙarƙashiya, suna cewa,
Because that Aram counseled evil against you, Ephraim and the son of Remaliah, saying,
6 “Bari mu kai wa Yahuda hari; bari mu yayyage su mu rarraba su a tsakaninmu, mu naɗa Tabeyel sarki a kansu.”
We go up into Judah, and we distress it, And we divide it to ourselves, And we cause a king to reign in its midst—The son of Tabeal.
7 Duk da haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “‘Ba zai faru ba, ba zai auku ba,
Thus said Lord YHWH: It does not stand, nor will it be!
8 gama kan Aram shi ne Damaskus, kan Damaskus kuma kawai shi ne Rezin. Cikin shekaru sittin da biyar za a wargaje Efraim har ba za tă iya rayuwa ta zama al’umma ba.
For the head of Aram [is] Damascus, And the head of Damascus [is] Rezin, And within sixty-five years Is Ephraim broken from [being] a people.
9 Kan Efraim shi ne Samariya, kan Samariya kuma kawai shi ne ɗan Remaliya. In ba ku tsaya da ƙarfi cikin bangaskiyarku ba, ba za ku dawwama ba.’”
And the head of Ephraim [is] Samaria, And the head of Samaria [is] the son of Remaliah. If you do not give credence, Surely you are not steadfast.”
10 Ubangiji ya kuma yi magana wa Ahaz ya ce,
And YHWH adds to speak to Ahaz, saying,
11 “Ka roƙi Ubangiji Allahnka yă ba ka alama, ko daga zurfafa masu zurfi ko kuwa daga can cikin sama.” (Sheol h7585)
“Ask for a sign from your God YHWH, Make the request deep, or make [it] high upwards.” (Sheol h7585)
12 Amma Ahaz ya ce, “Ba zan nema ba; ba zan gwada Ubangiji ba.”
And Ahaz says, “I do not ask nor try YHWH.”
13 Sa’an nan Ishaya ya ce, “To, ku saurara, ya ku gidan Dawuda! Abin kirki kuke yi ne da kuka ƙure haƙurin jama’a? Ko haƙurin Allah ne kuma kuke so ku ƙure?
And he says, “Now hear, O house of David, Is it a little thing for you to weary men, That you also weary my God?
14 Saboda haka Ubangiji kansa zai ba ku alama. Ga shi budurwa za tă yi ciki, za tă haifi ɗa, za tă kuwa kira shi Immanuwel.
Therefore the Lord Himself gives a sign to you, Behold, the virgin is conceiving, And is bringing forth a Son, And has called His Name Immanuel,
15 In ya yi girma har ya isa yanke shawara don kansa, madara da zuma ne abincinsa.
He eats butter and honey, When He knows to refuse evil, and to fix on good.
16 Amma kafin yaron yă isa yanke shawara yă ƙi abin da yake mummuna, yă zaɓi abin da yake nagari, ƙasashen sarakunan nan biyu da kuke tsoro za su zama kango.
For before the youth knows To refuse evil, and to fix on good, The land you are distressed with is forsaken, because of her two kings.
17 Ubangiji zai aukar maka da kwanakin wahala, kai da jama’arka, da dukan iyalin gidan sarauta, waɗanda suka fi muni tun lokacin da aka raba mulkin Efraim daga na Yahuda, zai kawo sarkin Assuriya.”
YHWH brings on you, and on your people, And on the house of your father, Days that have not come, Even from the day of the turning aside of Ephraim from Judah, By the king of Asshur.”
18 A wannan rana Ubangiji zai yi feɗuwa yă kira ƙudaje daga rafuffuka masu nisa na Masar da kuma ƙudan zuma daga ƙasar Assuriya.
And it has come to pass in that day, YHWH hisses for a fly that [is] in the extremity of the brooks of Egypt, And for a bee that [is] in the land of Asshur.
19 Za su zo su mamaye kwazazzabai da kogwanni cikin duwatsu, a kan dukan ƙayayyuwa da dukan rammukan ruwa.
And they have come, and all of them rested in the desolate valleys, And in holes of the rocks, and on all the thorns, And on all the commendable things.
20 A wannan rana Ubangiji zai yi amfani da rezan da aka yi haya daga ƙetaren Kogi, sarkin Assuriya ke nan, yă aske kanku da gashin ƙafafunku, zai kuma aske gemunku.
In that day the Lord shaves, By a razor that is hired beyond the river, By the king of Asshur, The head, and the hair of the feet, Indeed, it also consumes the beard.
21 A ranar, mutum zai bar karsana ɗaya da awaki biyu da rai.
And it has come to pass in that day, A man keeps alive a heifer of the herd, And two of the flock,
22 Kuma saboda yalwa madarar da suke bayarwa, zai kasance da madarar da zai sha. Dukan waɗanda suka rage a ƙasar za su sha madara da zuma.
And it has come to pass, He eats butter from the abundance of the yielding of milk, For everyone who is left in the heart of the land eats butter and honey.
23 A wannan rana, a kowane wuri inda akwai kuringa dubu da kuɗinsu ya kai shekel dubu na azurfa, ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne kawai za su kasance a can.
And it has come to pass in that day, Every place where there are one thousand vines, At one thousand pieces of silver, Is for briers and for thorns.
24 Mutane za su je can da baka da kibiyoyi, gama ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne za su rufe ƙasar.
He comes there with arrows and with bow, Because all the land is brier and thorn.
25 Game da dukan tuddai da dā ake nome da garemani kuwa, ba za ku ƙara je wurin ba saboda tsoron ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya; za su zama wuraren da ake kai shanu a sake su su yi ta yawo da kansu, tumaki kuma su yi ta gudu.
And all the hills that are kept in order with a mattock, There does not come [for] fear of brier and thorn, And it has been for the sending forth of ox, And for the treading of sheep!

< Ishaya 7 >