< Ishaya 7 >

1 Sa’ad da Ahaz ɗan Yotam, ɗan Uzziya, yake sarkin Yahuda, Sarki Rezin na Aram da Feka ɗan Remaliya sarkin Isra’ila suka haura don su yaƙi Urushalima, amma ba su iya cinta da yaƙi ba.
Og det skete i de Dage da Akaz, Jotams Søn, Uzzijas Sønnesøn, var Konge i Juda, at Kong Rezin af Syrien og Remaljas Søn, kong Peka af Israel, drog op for at angribe Jerusalem, hvad de dog ikke var stærke nok til.
2 Sai fa aka faɗa wa gidan Dawuda cewa, “Aram ya haɗa kansa da Efraim”; saboda haka zuciyar Ahaz da ta mutanensa suka firgita, sai ka ce itatuwa a kurmin da iska ta girgiza.
Da det meldtes Davids Hus, at Syrerne havde lejret sig i Efraim, skjalv hans og hans Folks Hjerte, som Skovens Træer skælver for Vinden.
3 Sai Ubangiji ya ce wa Ishaya, “Fita, kai da ɗanka Sheyar-Yashub, don ku sadu da Ahaz a ƙarshen wuriyar da take kawo ruwa daga Tafkin Tudu, a hanyar Filin Mai Wanki.
Så sagde HERREN til Esajas: "Med din Søn Sjearjasjub" skal du gå Akaz i Møde ved Enden af Øvredammens Vandledning ved Vejen til Blegepladsen
4 Ka faɗa masa, ‘Ka yi hankali, ka natsu kada kuma ka ji tsoro ko ka damu, kada ka ji tsoron fushin sarki Rezin da na Aram da na ɗan Remaliya, ba wani abu mai hatsari ba ne, bai fi hayaƙin’yan ƙirare biyu da suke cin wuta ba.
og sige til ham: Tag dig i Vare og hold dig i Ro! Frygt ikke og lad ikke dit Hjerte ængste sig for disse to rygende Brandstumper, for Rezins og Syriens og Remaljas Søns fnysende Vrede!
5 Aram, Efraim da ɗan Remaliya sun ƙulla maƙarƙashiya, suna cewa,
Fordi Syrien, Efraim og Remaljas Søn har lagt onde Råd op imod dig og siger:
6 “Bari mu kai wa Yahuda hari; bari mu yayyage su mu rarraba su a tsakaninmu, mu naɗa Tabeyel sarki a kansu.”
Lad os drage op mod Juda og indjage det Skræk, lad os tilrive os det og gøre Tabeals Søn til Konge der!
7 Duk da haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “‘Ba zai faru ba, ba zai auku ba,
derfor, så siger den Herre HERREN: Det skal ikke lykkes; det skal ikke ske!
8 gama kan Aram shi ne Damaskus, kan Damaskus kuma kawai shi ne Rezin. Cikin shekaru sittin da biyar za a wargaje Efraim har ba za tă iya rayuwa ta zama al’umma ba.
Thi Syriens Hoved er Damaskus, og Damaskus's Hoved er Rezin, og om fem og tresindstyve År er Efraim knust og ikke længer et Folk.
9 Kan Efraim shi ne Samariya, kan Samariya kuma kawai shi ne ɗan Remaliya. In ba ku tsaya da ƙarfi cikin bangaskiyarku ba, ba za ku dawwama ba.’”
Og Efraims Hoved er Samaria, og Samarias Hoved er Remaljas Søn. Er I ikke troende, bliver I ikke boende."
10 Ubangiji ya kuma yi magana wa Ahaz ya ce,
Fremdeles sagde HERREN til Akaz:
11 “Ka roƙi Ubangiji Allahnka yă ba ka alama, ko daga zurfafa masu zurfi ko kuwa daga can cikin sama.” (Sheol h7585)
"Kræv dig et Tegn af HERREN din Gud nede i Dødsriget eller oppe i Himmelen!" (Sheol h7585)
12 Amma Ahaz ya ce, “Ba zan nema ba; ba zan gwada Ubangiji ba.”
Men Akaz svarede: "Jeg kræver intet, jeg frister ikke HERREN."
13 Sa’an nan Ishaya ya ce, “To, ku saurara, ya ku gidan Dawuda! Abin kirki kuke yi ne da kuka ƙure haƙurin jama’a? Ko haƙurin Allah ne kuma kuke so ku ƙure?
Da sagde Esajas: "Hør nu, Davids Hus! Er det eder ikke nok at trætte Mennesker, siden I også trætter min Gud?
14 Saboda haka Ubangiji kansa zai ba ku alama. Ga shi budurwa za tă yi ciki, za tă haifi ɗa, za tă kuwa kira shi Immanuwel.
Derfor vil Herren selv give eder et Tegn: Se, Jomfruen bliver frugtsommelig og føder en Søn, og hun kalder ham Immanuel".
15 In ya yi girma har ya isa yanke shawara don kansa, madara da zuma ne abincinsa.
Surmælk og Vildhonning skal være hans Føde, ved den Tid han ved at vrage det onde og vælge det gode;
16 Amma kafin yaron yă isa yanke shawara yă ƙi abin da yake mummuna, yă zaɓi abin da yake nagari, ƙasashen sarakunan nan biyu da kuke tsoro za su zama kango.
thi før Drengen ved at vrage det onde og vælge det gode, skal Landet, for hvis to Konger du gruer, være folketomt.
17 Ubangiji zai aukar maka da kwanakin wahala, kai da jama’arka, da dukan iyalin gidan sarauta, waɗanda suka fi muni tun lokacin da aka raba mulkin Efraim daga na Yahuda, zai kawo sarkin Assuriya.”
Over dig, dit Folk og din Faders Hus vil Herren bringe Dage, hvis Lige ikke har været, siden Efraim rev sig løs fra Juda: Assyrerkongen!"
18 A wannan rana Ubangiji zai yi feɗuwa yă kira ƙudaje daga rafuffuka masu nisa na Masar da kuma ƙudan zuma daga ƙasar Assuriya.
På hin Dag skal HERREN fløjte ad Fluerne ved Udløbet af Ægyptens Strømme og ad Bierne i Assyrien;
19 Za su zo su mamaye kwazazzabai da kogwanni cikin duwatsu, a kan dukan ƙayayyuwa da dukan rammukan ruwa.
og de skal komme og alle til Hobe kaste sig over Dalkløfter og Klipperevner, over hvert Tjørnekrat og hvert Vandingssted.
20 A wannan rana Ubangiji zai yi amfani da rezan da aka yi haya daga ƙetaren Kogi, sarkin Assuriya ke nan, yă aske kanku da gashin ƙafafunku, zai kuma aske gemunku.
På hin Dag afrager Herren med en hinsides Floden lejet Ragekniv, Assyrerkongen, både Hovedhåret og Kroppens Hår; ja, selv Skægget skraber den af.
21 A ranar, mutum zai bar karsana ɗaya da awaki biyu da rai.
På hin Dag kan en Mand holde sig en ung Ko og et Par Får;
22 Kuma saboda yalwa madarar da suke bayarwa, zai kasance da madarar da zai sha. Dukan waɗanda suka rage a ƙasar za su sha madara da zuma.
og på Grund af den megen Mælk, de giver, skal han spise Sur mælk; thi Surmælk og Vildhonning skal enhver, der er tilbage i Landet, spise.
23 A wannan rana, a kowane wuri inda akwai kuringa dubu da kuɗinsu ya kai shekel dubu na azurfa, ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne kawai za su kasance a can.
På hin Dag skal det ske, at hvert et Sted, hvor der nu er tusind Vinstokke, tusind Sekel Sølv værd, skal blive til Torn og Tidsel;
24 Mutane za su je can da baka da kibiyoyi, gama ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne za su rufe ƙasar.
med Pil og Bue kommer man der, thi hele Landet skal blive til Torn og Tidsel;
25 Game da dukan tuddai da dā ake nome da garemani kuwa, ba za ku ƙara je wurin ba saboda tsoron ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya; za su zama wuraren da ake kai shanu a sake su su yi ta yawo da kansu, tumaki kuma su yi ta gudu.
og alle de Bjerge, der nu dyrkes med Hakke, skal man holde sig fra af Frygt for Torn og Tidsel. Det bliver Overdrev for Okser og trædes ned af Får.

< Ishaya 7 >