< Ishaya 66 >

1 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Sama kursiyina ce, duniya kuma matashin sawuna. Ina gidan da za ku gina mini? Ina wurin hutuna zai kasance?
Так говорить Госпо́дь: Небеса́ — Мій престо́л, а земля — то підні́жок для ніг Моїх: який же то храм, що для Мене збуду́єте ви, і яке ото місце Його відпочи́нку?
2 Ba hannuna ba ne ya yi dukan waɗannan abubuwa, ta haka suka kasance?” In ji Ubangiji. “Wannan mutum ne nake jin daɗi, shi da yake mai ƙasƙanci da kuma zuciyar yin tuba, yana kuma rawar jiki ga maganata.
Таж усе це створи́ла рука Моя, і так все це ста́лось, говорить Госпо́дь! І при тому дивлюсь Я на вбо́гого та на розби́того духом, і на тремтя́чого над Моїм словом.
3 Amma duk ya miƙa hadayar bijimi yana kama da wanda ya kashe mutum, kuma duk wanda ya miƙa ɗan rago, kamar wanda ya karye wuyan kare; duk wanda ya miƙa hadaya ta gari yana kama da wanda ya yi sadakar jinin alade, kuma duk wanda ya ƙone turaren tuni, kamar wanda yake bauta gunki ne. Sun zaɓi hanyoyinsu, rayukansu kuma suna jin daɗin abubuwan banƙyamarsu;
Іна́кше хто ріже вола — одноча́сно вбиває люди́ну, прино́сить у жертву ягня́ — перело́млює шию собаці, дару́нка прино́сить — вживає свинячої крови, складає з кадила частину прига́дувальну, — одноча́сно божка́ благосло́вить. Отак як доро́ги свої вони повибира́ли, і до гидо́т тих своїх уподо́бання чує душа їхня,
4 saboda haka ni ma zan aukar musu da masifa mai zafi in kuma kawo musu abin da suke tsoro. Gama sa’ad da na yi kira, ba wanda ya amsa, sa’ad da na yi magana, ba wanda ya saurara, Sun aikata mugunta a idona suka kuma zaɓa abin da ba na jin daɗi.”
так ви́беру й Я їх на зве́дення, і предмета їхнього стра́ху на них наведу́, за те, що Я кликав — і ніхто ві́дповіді не давав, говорив Я — й не чули вони, та чинили лихе в Моїх о́чах, і ви́брали те, чого Я не жада́в!
5 Ku ji maganar Ubangiji, ku da kuke rawar jiki ga maganarsa, “’Yan’uwanku da suke ƙinku, suna kuma ware ku saboda sunana, sun ce, ‘Bari a ɗaukaka Ubangiji, don mu ga farin cikinku!’ Duk da haka za su sha kunya.
Послухайте сло́ва Господнього ті, що на слово Його тремтите́: Кажуть ваші брати, що нена́видять вас, що ва́с ради Йме́ння Мого виганяють: „Хай просла́влений буде Господь, і ми вашу радість побачимо!“Та будуть вони посоро́млені!
6 Ku ji wannan hayaniya daga birni, ku ji surutu daga haikali! Amon Ubangiji ne yana sāka wa abokan gābansa abin da ya dace da su.
Голос го́мону з міста, голос із храму, — це голос Господа, що заплату дає для Своїх ворогів!
7 “Kafin naƙuda ya fara mata, ta haihu; kafin zafi ya zo mata, ta haifi ɗa.
Поки зазна́ла дрижа́ння поро́ду, вона породила, і поки прийшов її біль, то сина леге́нько вона привела́.
8 Wa ya taɓa jin irin wannan abu? Wa ya taɓa gani irin abubuwan nan? Za a iya ƙirƙiro ƙasa a rana ɗaya ko a haifi al’umma farat ɗaya? Duk da haka da zarar Sihiyona ta fara naƙuda sai ta haifi’ya’yanta.
Хто таке́ коли чув, і хто бачив таке́? Чи зро́джена буде земля в один день, чи наро́джений буде народ за одним ра́зом? Бо як тільки зазнала Сіонська дочка́ породо́ві дрижа́ння, то синів своїх вже породила.
9 Zan kai mace har haihuwa in kuma sa ta kāsa haihu?” In ji Ubangiji. “Zan rufe mahaihuwa sa’ad da lokacin haihuwa ya yi?” In ji Allahnku.
Чи Я допрова́джу до по́роду, — і не вчиню́, щоб вона породила? говорить Господь. Чи Я, що чиню́, щоб роди́ла, — і стримаю? каже твій Бог.
10 “Ku yi farin ciki tare da Urushalima ku kuma yi murna saboda ita, dukanku waɗanda kuke ƙaunarta; ku yi farin ciki matuƙa tare da ita, dukanku waɗanda kuke makoki a kanta.
Радійте із Єрусалимом і ті́штеся всі ним, хто його покоха́в! Втішайтесь ним радістю всі, що з-за нього в жало́бі були́!
11 Gama za ku tsotsa ku kuma ƙoshi da nonon ta’aziyyarta; za ku sha sosai ku kuma ji daɗin yalwarta.”
Щоб ви сса́ли й наси́тилися з перс поті́хи його, щоб ви ссали та розкошува́ли із перс його слави!
12 Gama ga abin da Ubangiji ya faɗa, “Zan fadada salama gare ta kamar kogi, wadatar al’ummai kuma kamar rafi mai gudu; za ku tsotsa a kuma riƙe ku a hannunta ku kuma yi wasa a gwiwoyinta.
Бо Господь каже так: Ось керу́ю до нього Я мир, немов річку, і славу наро́дів, немов той потік заливни́й: і ви бу́дете ссати, і на руках вас носи́тимуть, і ба́витимуть на колі́нах!
13 Kamar yadda uwa takan ta’azantar da ɗanta haka zan ta’azantar da ku; za ku kuma ta’azantu a Urushalima.”
Як кого́сь його не́нька втіша́є, так вас Я поті́шу, і ви вті́шені бу́дете Єрусалимом.
14 Sa’ad da kuka ga wannan, zuciyarku za tă yi farin ciki za ku kuma haɓaka kamar ciyawa; za a sanar da hannun Ubangiji ga bayinsa, amma za a nuna wa maƙiyansa fushinsa.
І побачите це, й серце ваше раді́тиме, й як трава молода, розцвіту́ть ваші ко́сті! І в раба́х Його пі́знана буде Господня рука, і буде Він гні́ватися на Своїх ворогів.
15 Ga shi, Ubangiji yana zuwa da wuta, kuma kekunan yaƙinsa suna kama da guguwa; zai sauko da fushinsa da zafi, tsawatawarsa kuma da harsunan wuta.
Бо ось при́йде Господь у в огні, а Його колесни́ці — мов буря, щоб відплати́ти жаром гніву Свого́, а погро́зи Свої — полум'я́ним огнем!
16 Gama da wuta da kuma takobi Ubangiji zai yi hukunci a kan dukan mutane, kuma yawanci za su kasance waɗanda Ubangiji zai kashe.
Бо огнем та мечем Своїм буде суди́тись Госпо́дь з кожним тілом, і буде багато побитих від Го́спода.
17 “Waɗanda suka tsarkake suka kuma tsabtacce kansu don su je lambu, suna bin wannan da yake tsakiya waɗannan da suke cin naman aladu da ɓeraye da waɗansu abubuwan banƙyama, za su sadu da ƙarshensu tare,” in ji Ubangiji.
А ті, хто освя́чується й очища́є себе у пога́нських садка́х, один по одно́му, всере́дині, їдять м'ясо свиня́че й гидо́ти та мишу, — вони ра́зом загинуть, говорить Господь!
18 “Ni kuwa, saboda ayyukansu da kuma tunaninsu, ina dab da zuwa in tattara dukan al’ummai da harsuna, za su kuma zo su ga ɗaukakata.
І Я знаю їхні вчи́нки та їхні думки́, і прийду́, щоб зібрати всі наро́ди й язи́ки, — і при́йдуть вони й Мою славу побачать!
19 “Zan kafa alama a cikinsu, zan kuma aika waɗansu da suka tsira zuwa al’ummai, zuwa Tarshish, zuwa Libiya da Lidiya (sanannun’yan aika), zuwa Tubal da kuma Girka, da kuma zuwa manisantan tsibirai da ba su taɓa jin labarin sunana ba ko su ga ɗaukakata. Za su yi shelar ɗaukakata a cikin al’ummai.
І зна́ка на них покладу́, і пошлю́ урято́ваних з них до наро́дів, у Тарші́ш, Пул, і Лул, в Мешех і Кос, у Тувал та Яван, в острови́ предале́кі, що зві́стки про Мене не чули й не бачили слави Моєї, — і звістя́ть мою славу вони між наро́дами!
20 Za su kuma dawo da dukan’yan’uwanku, daga dukan al’ummai, zuwa dutsena mai tsarki a Urushalima kamar hadaya ga Ubangiji, a kan dawakai, a kekunan yaƙi da wagonu, da kuma a kan alfadarai da kuma raƙuma,” in ji Ubangiji. “Za su kawo su, kamar yadda Isra’ilawa suke kawo hadayun hatsi, zuwa haikalin Ubangiji a cikin tsabtatattun kore.
І вони приведу́ть усіх ваших братів із наро́дів усіх у дару́нок для Господа на ко́нях та на колесницях, і на фурах та мулах, та на верблю́дах, на го́ру святу Мою, до Єрусалиму, говорить Госпо́дь, як прино́сять сино́ве Ізраїлеві дару́нка в посу́дині чистій до дому Господнього.
21 Zan kuwa zaɓa waɗansunsu kuma su zama firistoci da Lawiyawa,” in ji Ubangiji.
І візьму́ Я із них за священиків та за Левитів, говорить Господь.
22 “Kamar yadda sabuwar duniya da sabuwar sama za su tabbata a gabana,” in ji Ubangiji, “haka sunanku da zuriyarku za su tabbata.
Бо як небо нове́ та нова́ та земля, що вчиню́, стануть перед обличчям Моїм, говорить Господь, так стоятимуть ваші наща́дки та ваше ім'я́!
23 Daga wannan sabon wata zuwa wancan, kuma daga wannan Asabbaci zuwa wancan, dukan mutane za su zo su rusuna a gabana,” in ji Ubangiji.
І станеться, кожного новомі́сяччя в ча́сі його, і щосуботи за ча́су її кожне тіло прихо́дитиме, щоб вклоня́тися перед обличчям Моїм, говорить Господь.
24 “Za su kuma fita su ga gawawwakin mutanen da suka yi mini tayarwa; tsutsotsin da suke cinsu ba za su taɓa mutuwa ba, balle wutar da take ƙona su ta mutu, za su kuma zama abin ƙyama ga dukan mutane.”
І ви́йдуть вони та й побачать ті трупи людей, що відпа́ли від Мене, бо їхня черва́ не помре й не пога́сне огонь їхній, — і стануть вони за ги́доту для кожного тіла!

< Ishaya 66 >