< Ishaya 66 >
1 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Sama kursiyina ce, duniya kuma matashin sawuna. Ina gidan da za ku gina mini? Ina wurin hutuna zai kasance?
Thus said YHWH: “The heavens [are] My throne, And the earth My footstool, Where [is] this—the house that you build for Me? And where [is] this—the place—My rest?
2 Ba hannuna ba ne ya yi dukan waɗannan abubuwa, ta haka suka kasance?” In ji Ubangiji. “Wannan mutum ne nake jin daɗi, shi da yake mai ƙasƙanci da kuma zuciyar yin tuba, yana kuma rawar jiki ga maganata.
And My hand has made all these, And all these things are,” A declaration of YHWH! “And to this one I look attentively, To the humble and bruised in spirit, And who is trembling at My word.
3 Amma duk ya miƙa hadayar bijimi yana kama da wanda ya kashe mutum, kuma duk wanda ya miƙa ɗan rago, kamar wanda ya karye wuyan kare; duk wanda ya miƙa hadaya ta gari yana kama da wanda ya yi sadakar jinin alade, kuma duk wanda ya ƙone turaren tuni, kamar wanda yake bauta gunki ne. Sun zaɓi hanyoyinsu, rayukansu kuma suna jin daɗin abubuwan banƙyamarsu;
Whoever slaughters the ox strikes a man, Whoever sacrifices the lamb beheads a dog, Whoever is bringing up a present—The blood of a sow, Whoever is making mention of frankincense, Is blessing iniquity. Indeed, they have fixed on their own ways, And their soul has delighted in their abominations.
4 saboda haka ni ma zan aukar musu da masifa mai zafi in kuma kawo musu abin da suke tsoro. Gama sa’ad da na yi kira, ba wanda ya amsa, sa’ad da na yi magana, ba wanda ya saurara, Sun aikata mugunta a idona suka kuma zaɓa abin da ba na jin daɗi.”
I also—I fix on their distress, And I bring in their fears to them, Because I have called, and there is none answering, I spoke, and they have not listened, And they do evil in My eyes, And on that which I did not desire—fixed.”
5 Ku ji maganar Ubangiji, ku da kuke rawar jiki ga maganarsa, “’Yan’uwanku da suke ƙinku, suna kuma ware ku saboda sunana, sun ce, ‘Bari a ɗaukaka Ubangiji, don mu ga farin cikinku!’ Duk da haka za su sha kunya.
Hear a word of YHWH, You who are trembling at His word: “Your brothers who are hating you, Who are driving you out for My Name’s sake, have said, YHWH is honored, and we look on your joy, But they are ashamed.”
6 Ku ji wannan hayaniya daga birni, ku ji surutu daga haikali! Amon Ubangiji ne yana sāka wa abokan gābansa abin da ya dace da su.
A voice of noise from the city, A voice from the temple, The voice of YHWH, Giving repayment to His enemies.
7 “Kafin naƙuda ya fara mata, ta haihu; kafin zafi ya zo mata, ta haifi ɗa.
“Before she is pained she has brought forth, Before a pang comes to her, She has delivered a male.
8 Wa ya taɓa jin irin wannan abu? Wa ya taɓa gani irin abubuwan nan? Za a iya ƙirƙiro ƙasa a rana ɗaya ko a haifi al’umma farat ɗaya? Duk da haka da zarar Sihiyona ta fara naƙuda sai ta haifi’ya’yanta.
Who has heard anything like this? Who has seen anything like these? Is earth caused to bring forth in one day? Is a nation born at once? For she has been pained, Zion has also borne her sons.
9 Zan kai mace har haihuwa in kuma sa ta kāsa haihu?” In ji Ubangiji. “Zan rufe mahaihuwa sa’ad da lokacin haihuwa ya yi?” In ji Allahnku.
Do I bring to the birth, And not cause to bring forth?” says YHWH, “Am I not He who is causing to beget? I have also restrained,” said your God.
10 “Ku yi farin ciki tare da Urushalima ku kuma yi murna saboda ita, dukanku waɗanda kuke ƙaunarta; ku yi farin ciki matuƙa tare da ita, dukanku waɗanda kuke makoki a kanta.
“Rejoice with Jerusalem, And be glad in her, all you loving her, Rejoice with her for joy, All you who are mourning for her,
11 Gama za ku tsotsa ku kuma ƙoshi da nonon ta’aziyyarta; za ku sha sosai ku kuma ji daɗin yalwarta.”
So that you suckle, and have been satisfied, From the breast of her consolations, So that you wring out, and have delighted yourselves From the abundance of her glory.”
12 Gama ga abin da Ubangiji ya faɗa, “Zan fadada salama gare ta kamar kogi, wadatar al’ummai kuma kamar rafi mai gudu; za ku tsotsa a kuma riƙe ku a hannunta ku kuma yi wasa a gwiwoyinta.
For thus said YHWH: “Behold, I am stretching out to her peace as a river, And the glory of nations as an overflowing stream, And you have sucked, You are carried on the side, And you are dandled on the knees.
13 Kamar yadda uwa takan ta’azantar da ɗanta haka zan ta’azantar da ku; za ku kuma ta’azantu a Urushalima.”
As one whom his mother comforts, so do I comfort you, Indeed, you are comforted in Jerusalem.”
14 Sa’ad da kuka ga wannan, zuciyarku za tă yi farin ciki za ku kuma haɓaka kamar ciyawa; za a sanar da hannun Ubangiji ga bayinsa, amma za a nuna wa maƙiyansa fushinsa.
And you have seen, and your heart has rejoiced, And your bones flourish as tender grass, And the hand of YHWH has been known to His servants, And He has been indignant with His enemies.
15 Ga shi, Ubangiji yana zuwa da wuta, kuma kekunan yaƙinsa suna kama da guguwa; zai sauko da fushinsa da zafi, tsawatawarsa kuma da harsunan wuta.
For behold, YHWH comes in fire, And His chariots as a windstorm, To refresh His anger in fury, And His rebuke in flames of fire.
16 Gama da wuta da kuma takobi Ubangiji zai yi hukunci a kan dukan mutane, kuma yawanci za su kasance waɗanda Ubangiji zai kashe.
For by fire and by His sword, YHWH does judgment with all flesh. And many have been YHWH’s pierced ones.
17 “Waɗanda suka tsarkake suka kuma tsabtacce kansu don su je lambu, suna bin wannan da yake tsakiya waɗannan da suke cin naman aladu da ɓeraye da waɗansu abubuwan banƙyama, za su sadu da ƙarshensu tare,” in ji Ubangiji.
“Those sanctifying and cleansing themselves [to go] to the gardens, One after another in the midst, Eating flesh of the sow, And of the abomination, and of the muroid, Are consumed together,” A declaration of YHWH.
18 “Ni kuwa, saboda ayyukansu da kuma tunaninsu, ina dab da zuwa in tattara dukan al’ummai da harsuna, za su kuma zo su ga ɗaukakata.
“And I—their works and their thoughts, I come to gather all the nations and tongues, And they have come and seen My glory.
19 “Zan kafa alama a cikinsu, zan kuma aika waɗansu da suka tsira zuwa al’ummai, zuwa Tarshish, zuwa Libiya da Lidiya (sanannun’yan aika), zuwa Tubal da kuma Girka, da kuma zuwa manisantan tsibirai da ba su taɓa jin labarin sunana ba ko su ga ɗaukakata. Za su yi shelar ɗaukakata a cikin al’ummai.
And I have set a sign among them, And have sent out of them those escaping to the nations (Tarshish, Pul, and Lud, drawing bow, Tubal and Javan, the islands that are far off), Who have not heard My fame, nor seen My glory, And they have declared My glory among nations.
20 Za su kuma dawo da dukan’yan’uwanku, daga dukan al’ummai, zuwa dutsena mai tsarki a Urushalima kamar hadaya ga Ubangiji, a kan dawakai, a kekunan yaƙi da wagonu, da kuma a kan alfadarai da kuma raƙuma,” in ji Ubangiji. “Za su kawo su, kamar yadda Isra’ilawa suke kawo hadayun hatsi, zuwa haikalin Ubangiji a cikin tsabtatattun kore.
And they have brought all your brothers out of all the nations, A present to YHWH, On horses, and on chariot, and on litters, And on mules, and on dromedaries, To My holy mountain Jerusalem,” said YHWH, “As the sons of Israel bring the present in a clean vessel, Into the house of YHWH.
21 Zan kuwa zaɓa waɗansunsu kuma su zama firistoci da Lawiyawa,” in ji Ubangiji.
And I also take of them for priests, For Levites,” said YHWH.
22 “Kamar yadda sabuwar duniya da sabuwar sama za su tabbata a gabana,” in ji Ubangiji, “haka sunanku da zuriyarku za su tabbata.
“For as the new heavens and the new earth that I am making, Are standing before Me,” A declaration of YHWH, “So your seed and your name remain.
23 Daga wannan sabon wata zuwa wancan, kuma daga wannan Asabbaci zuwa wancan, dukan mutane za su zo su rusuna a gabana,” in ji Ubangiji.
And it has been from month to month, And from Sabbath to Sabbath, All flesh come to bow themselves before Me,” said YHWH.
24 “Za su kuma fita su ga gawawwakin mutanen da suka yi mini tayarwa; tsutsotsin da suke cinsu ba za su taɓa mutuwa ba, balle wutar da take ƙona su ta mutu, za su kuma zama abin ƙyama ga dukan mutane.”
“And they have gone forth, And looked on the carcasses of the men Who are transgressing against Me, For their worm does not die, And their fire is not quenched, And they have been an abhorrence to all flesh!”