< Ishaya 66 >
1 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Sama kursiyina ce, duniya kuma matashin sawuna. Ina gidan da za ku gina mini? Ina wurin hutuna zai kasance?
Thus hath said the Lord, The heaven is my throne, and the earth is my footstool: where is there a house that ye can build unto me? and where is the place of my rest?
2 Ba hannuna ba ne ya yi dukan waɗannan abubuwa, ta haka suka kasance?” In ji Ubangiji. “Wannan mutum ne nake jin daɗi, shi da yake mai ƙasƙanci da kuma zuciyar yin tuba, yana kuma rawar jiki ga maganata.
For all these things hath my hand made, that all these things came into being, saith the Lord; but upon such a one will I look, upon the poor, and him who is of a contrite spirit, and who trembleth at my word.
3 Amma duk ya miƙa hadayar bijimi yana kama da wanda ya kashe mutum, kuma duk wanda ya miƙa ɗan rago, kamar wanda ya karye wuyan kare; duk wanda ya miƙa hadaya ta gari yana kama da wanda ya yi sadakar jinin alade, kuma duk wanda ya ƙone turaren tuni, kamar wanda yake bauta gunki ne. Sun zaɓi hanyoyinsu, rayukansu kuma suna jin daɗin abubuwan banƙyamarsu;
He that slaughtereth the ox, slayeth a man; he that sacrificeth a lamb, breaketh the neck of a dog; he that offereth a meat-offering, [offereth] swine's blood; he that burneth incense, blesseth an idol: yea, they have made choice of their own ways, and in their abominations doth their soul delight.
4 saboda haka ni ma zan aukar musu da masifa mai zafi in kuma kawo musu abin da suke tsoro. Gama sa’ad da na yi kira, ba wanda ya amsa, sa’ad da na yi magana, ba wanda ya saurara, Sun aikata mugunta a idona suka kuma zaɓa abin da ba na jin daɗi.”
So will I also make choice of their misfortune, and what they dread will I bring upon them; because I called, and none did answer; I spoke, and they did not hear; and they did what is evil in my eyes, and that in which I delighted not did they choose.
5 Ku ji maganar Ubangiji, ku da kuke rawar jiki ga maganarsa, “’Yan’uwanku da suke ƙinku, suna kuma ware ku saboda sunana, sun ce, ‘Bari a ɗaukaka Ubangiji, don mu ga farin cikinku!’ Duk da haka za su sha kunya.
Hear the word of the Lord, ye that tremble at his word: Your brethren that hated you, that cast you out for the sake of my name, said, “Let the Lord be glorified;” but he will appear to your joy, and they shall be made ashamed.
6 Ku ji wannan hayaniya daga birni, ku ji surutu daga haikali! Amon Ubangiji ne yana sāka wa abokan gābansa abin da ya dace da su.
[There is] a voice of tumult from the city, a voice from the temple, the voice of the Lord who rendereth recompense to his enemies.
7 “Kafin naƙuda ya fara mata, ta haihu; kafin zafi ya zo mata, ta haifi ɗa.
Before she had travailed she brought forth; before yet her pain was come, she was delivered of a man-child.
8 Wa ya taɓa jin irin wannan abu? Wa ya taɓa gani irin abubuwan nan? Za a iya ƙirƙiro ƙasa a rana ɗaya ko a haifi al’umma farat ɗaya? Duk da haka da zarar Sihiyona ta fara naƙuda sai ta haifi’ya’yanta.
Who hath heard the like? who hath seen such things? shall a land be made to travail in one day? or shall a nation be born at once? that Zion hath travailed, also brought forth her children?
9 Zan kai mace har haihuwa in kuma sa ta kāsa haihu?” In ji Ubangiji. “Zan rufe mahaihuwa sa’ad da lokacin haihuwa ya yi?” In ji Allahnku.
Shall I bring to the birth, and not cause to bring forth? saith the Lord; or shall I who cause to bring forth, now prevent it? saith thy God.
10 “Ku yi farin ciki tare da Urushalima ku kuma yi murna saboda ita, dukanku waɗanda kuke ƙaunarta; ku yi farin ciki matuƙa tare da ita, dukanku waɗanda kuke makoki a kanta.
Rejoice ye with Jerusalem, and be delighted over her, all ye that love her; be highly glad with her, all ye that mourn for her.
11 Gama za ku tsotsa ku kuma ƙoshi da nonon ta’aziyyarta; za ku sha sosai ku kuma ji daɗin yalwarta.”
In order that ye may suck, and be satisfied with the breast of her consolations; in order that ye may sip, and find pleasure from the abundance of her glory.
12 Gama ga abin da Ubangiji ya faɗa, “Zan fadada salama gare ta kamar kogi, wadatar al’ummai kuma kamar rafi mai gudu; za ku tsotsa a kuma riƙe ku a hannunta ku kuma yi wasa a gwiwoyinta.
For thus hath said the Lord, Behold, I will extend to her peace like a river, and like a rapid stream the glory of nations, that ye may suck: upon the arm shall ye be borne, and upon knees shall ye be dandled.
13 Kamar yadda uwa takan ta’azantar da ɗanta haka zan ta’azantar da ku; za ku kuma ta’azantu a Urushalima.”
As one whom his mother comforteth, so will I comfort you; and in Jerusalem shall ye be comforted.
14 Sa’ad da kuka ga wannan, zuciyarku za tă yi farin ciki za ku kuma haɓaka kamar ciyawa; za a sanar da hannun Ubangiji ga bayinsa, amma za a nuna wa maƙiyansa fushinsa.
And ye shall see this, and your heart shall be glad, and your bones shall flourish like the grass; and then will be known the hand of the Lord on his servants, and he will be indignant toward his enemies.
15 Ga shi, Ubangiji yana zuwa da wuta, kuma kekunan yaƙinsa suna kama da guguwa; zai sauko da fushinsa da zafi, tsawatawarsa kuma da harsunan wuta.
For, behold, the Lord will come with fire, and his chariots will be like the storm-wind, to send forth his anger with fury, and his threatening with flames of fire.
16 Gama da wuta da kuma takobi Ubangiji zai yi hukunci a kan dukan mutane, kuma yawanci za su kasance waɗanda Ubangiji zai kashe.
For by fire will the Lord judge, and by his sword against all flesh: and many shall be the slain of the Lord.
17 “Waɗanda suka tsarkake suka kuma tsabtacce kansu don su je lambu, suna bin wannan da yake tsakiya waɗannan da suke cin naman aladu da ɓeraye da waɗansu abubuwan banƙyama, za su sadu da ƙarshensu tare,” in ji Ubangiji.
They that sanctify themselves, and purify themselves for the gardens, behind one tree in the midst, they who eat the flesh of the swine, and the abomination, and the mouse, together shall they perish, saith the Lord.
18 “Ni kuwa, saboda ayyukansu da kuma tunaninsu, ina dab da zuwa in tattara dukan al’ummai da harsuna, za su kuma zo su ga ɗaukakata.
And I, because of their works and their thoughts, will let it come to pass to gather all the nations and tongues; and they shall come, and shall see my glory.
19 “Zan kafa alama a cikinsu, zan kuma aika waɗansu da suka tsira zuwa al’ummai, zuwa Tarshish, zuwa Libiya da Lidiya (sanannun’yan aika), zuwa Tubal da kuma Girka, da kuma zuwa manisantan tsibirai da ba su taɓa jin labarin sunana ba ko su ga ɗaukakata. Za su yi shelar ɗaukakata a cikin al’ummai.
And I will display a sign on them, and I will send from them those that escape unto the nations, Tharshish, Pul, and Lud, that draw the bow, Thubal, and Javan, the isles afar off, that have not heard my fame, and have not seen my glory; and they shall proclaim my glory among the nations.
20 Za su kuma dawo da dukan’yan’uwanku, daga dukan al’ummai, zuwa dutsena mai tsarki a Urushalima kamar hadaya ga Ubangiji, a kan dawakai, a kekunan yaƙi da wagonu, da kuma a kan alfadarai da kuma raƙuma,” in ji Ubangiji. “Za su kawo su, kamar yadda Isra’ilawa suke kawo hadayun hatsi, zuwa haikalin Ubangiji a cikin tsabtatattun kore.
And they shall bring all your brethren out of all nations as an offering unto the Lord, upon horses, and in chariots, and in litters, and upon mules, and upon dromedaries, to my holy mountain Jerusalem, saith the Lord, as the children of Israel bring the offering in a clean vessel into the house of the Lord.
21 Zan kuwa zaɓa waɗansunsu kuma su zama firistoci da Lawiyawa,” in ji Ubangiji.
And of them also will I take for priests and for Levites, saith the Lord.
22 “Kamar yadda sabuwar duniya da sabuwar sama za su tabbata a gabana,” in ji Ubangiji, “haka sunanku da zuriyarku za su tabbata.
For as the new heavens and the new earth, which I will make, shall have permanence before me, saith the Lord, so shall exist permanently your seed and your name.
23 Daga wannan sabon wata zuwa wancan, kuma daga wannan Asabbaci zuwa wancan, dukan mutane za su zo su rusuna a gabana,” in ji Ubangiji.
And it shall come to pass, that from one new moon to the other new moon, and from one sabbath to the other sabbath, shall all flesh come to prostrate themselves before me, saith the Lord.
24 “Za su kuma fita su ga gawawwakin mutanen da suka yi mini tayarwa; tsutsotsin da suke cinsu ba za su taɓa mutuwa ba, balle wutar da take ƙona su ta mutu, za su kuma zama abin ƙyama ga dukan mutane.”
And they shall go forth, and look upon the carcasses of the men that have transgressed against me; for their worm shall not die, nor shall their fire be quenched; and they shall be an abhorrence unto all flesh.