< Ishaya 66 >

1 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Sama kursiyina ce, duniya kuma matashin sawuna. Ina gidan da za ku gina mini? Ina wurin hutuna zai kasance?
Thus saith the Lord: Heaven is my throne, and the earth my footstool: what is this house that you will build to me? and what is this place of my rest?
2 Ba hannuna ba ne ya yi dukan waɗannan abubuwa, ta haka suka kasance?” In ji Ubangiji. “Wannan mutum ne nake jin daɗi, shi da yake mai ƙasƙanci da kuma zuciyar yin tuba, yana kuma rawar jiki ga maganata.
My hand made all these things, and all these things were made, saith the Lord. But to whom shall I have respect, but to him that is poor and little, and of a contrite spirit, and that trembleth at my words?
3 Amma duk ya miƙa hadayar bijimi yana kama da wanda ya kashe mutum, kuma duk wanda ya miƙa ɗan rago, kamar wanda ya karye wuyan kare; duk wanda ya miƙa hadaya ta gari yana kama da wanda ya yi sadakar jinin alade, kuma duk wanda ya ƙone turaren tuni, kamar wanda yake bauta gunki ne. Sun zaɓi hanyoyinsu, rayukansu kuma suna jin daɗin abubuwan banƙyamarsu;
He that sacrificeth an ox, is as if he slew a man: he that killeth a sheep in sacrifice, as if he should brain a dog: he that offereth an oblation, as if he should offer swine’s blood; he that remembereth incense, as if he should bless an idol. All these things have they chosen in their ways, and their soul is delighted in their abominations.
4 saboda haka ni ma zan aukar musu da masifa mai zafi in kuma kawo musu abin da suke tsoro. Gama sa’ad da na yi kira, ba wanda ya amsa, sa’ad da na yi magana, ba wanda ya saurara, Sun aikata mugunta a idona suka kuma zaɓa abin da ba na jin daɗi.”
Wherefore I also will choose their mockeries, and will bring upon them the things they feared: because I called, and there was none that would answer; I have spoken, and they heard not; and they have done evil in my eyes, and have chosen the things that displease me.
5 Ku ji maganar Ubangiji, ku da kuke rawar jiki ga maganarsa, “’Yan’uwanku da suke ƙinku, suna kuma ware ku saboda sunana, sun ce, ‘Bari a ɗaukaka Ubangiji, don mu ga farin cikinku!’ Duk da haka za su sha kunya.
Hear the word of the Lord, you that tremble at his word: Your brethren that hate you, and cast you out for my name’s sake, have said: Let the Lord be glorified, and we shall see in your joy: but they shall be confounded.
6 Ku ji wannan hayaniya daga birni, ku ji surutu daga haikali! Amon Ubangiji ne yana sāka wa abokan gābansa abin da ya dace da su.
A voice of the people from the city, a voice from the temple, the voice of the Lord that rendereth recompense to his enemies.
7 “Kafin naƙuda ya fara mata, ta haihu; kafin zafi ya zo mata, ta haifi ɗa.
Before she was in labour, she brought forth; before her time came to be delivered, she brought forth a man child.
8 Wa ya taɓa jin irin wannan abu? Wa ya taɓa gani irin abubuwan nan? Za a iya ƙirƙiro ƙasa a rana ɗaya ko a haifi al’umma farat ɗaya? Duk da haka da zarar Sihiyona ta fara naƙuda sai ta haifi’ya’yanta.
Who hath ever heard such a thing? and who hath seen the like to this? shall the earth bring forth in one day? or shall a nation be brought forth at once, because Sion hath been in labour, and hath brought forth her children?
9 Zan kai mace har haihuwa in kuma sa ta kāsa haihu?” In ji Ubangiji. “Zan rufe mahaihuwa sa’ad da lokacin haihuwa ya yi?” In ji Allahnku.
Shall not I that make others to bring forth children, myself bring forth, saith the Lord? shall I, that give generation to others, be barren, saith the Lord thy God?
10 “Ku yi farin ciki tare da Urushalima ku kuma yi murna saboda ita, dukanku waɗanda kuke ƙaunarta; ku yi farin ciki matuƙa tare da ita, dukanku waɗanda kuke makoki a kanta.
Rejoice with Jerusalem, and be glad with her, all you that love her: rejoice for joy with her, all you that mourn for her.
11 Gama za ku tsotsa ku kuma ƙoshi da nonon ta’aziyyarta; za ku sha sosai ku kuma ji daɗin yalwarta.”
That you may suck, and be filled with the breasts of her consolations: that you may milk out, and flow with delights, from the abundance of her glory.
12 Gama ga abin da Ubangiji ya faɗa, “Zan fadada salama gare ta kamar kogi, wadatar al’ummai kuma kamar rafi mai gudu; za ku tsotsa a kuma riƙe ku a hannunta ku kuma yi wasa a gwiwoyinta.
For thus saith the Lord: Behold I will bring upon her as it were a river of peace, and as an overflowing torrent the glory of the Gentiles, which you shall suck; you shall be carried at the breasts, and upon the knees they shall caress you.
13 Kamar yadda uwa takan ta’azantar da ɗanta haka zan ta’azantar da ku; za ku kuma ta’azantu a Urushalima.”
As one whom the mother caresseth, so will I comfort you, and you shall be comforted in Jerusalem.
14 Sa’ad da kuka ga wannan, zuciyarku za tă yi farin ciki za ku kuma haɓaka kamar ciyawa; za a sanar da hannun Ubangiji ga bayinsa, amma za a nuna wa maƙiyansa fushinsa.
You shall see and your heart shall rejoice, and your bones shall flourish like an herb, and the hand of the Lord shall be known to his servants, and he shall be angry with his enemies.
15 Ga shi, Ubangiji yana zuwa da wuta, kuma kekunan yaƙinsa suna kama da guguwa; zai sauko da fushinsa da zafi, tsawatawarsa kuma da harsunan wuta.
For behold the Lord will come with fire, and his chariots are like a whirlwind, to render his wrath in indignation, and his rebuke with flames of fire.
16 Gama da wuta da kuma takobi Ubangiji zai yi hukunci a kan dukan mutane, kuma yawanci za su kasance waɗanda Ubangiji zai kashe.
For the Lord shall judge by fire, and by his sword unto all flesh, and the slain of the Lord shall be many.
17 “Waɗanda suka tsarkake suka kuma tsabtacce kansu don su je lambu, suna bin wannan da yake tsakiya waɗannan da suke cin naman aladu da ɓeraye da waɗansu abubuwan banƙyama, za su sadu da ƙarshensu tare,” in ji Ubangiji.
They that were sanctified, and thought themselves clean in the gardens behind the gate within, they that did eat swine’s flesh, and the abomination, and the mouse: they shall be consumed together, saith the Lord.
18 “Ni kuwa, saboda ayyukansu da kuma tunaninsu, ina dab da zuwa in tattara dukan al’ummai da harsuna, za su kuma zo su ga ɗaukakata.
But I know their works, and their thoughts: I come that I may gather them together with all nations and tongues: and they shall come and shall see my glory.
19 “Zan kafa alama a cikinsu, zan kuma aika waɗansu da suka tsira zuwa al’ummai, zuwa Tarshish, zuwa Libiya da Lidiya (sanannun’yan aika), zuwa Tubal da kuma Girka, da kuma zuwa manisantan tsibirai da ba su taɓa jin labarin sunana ba ko su ga ɗaukakata. Za su yi shelar ɗaukakata a cikin al’ummai.
And I will set a sign among them, and I will send of them that shall be saved, to the Gentiles into the sea, into Africa, and Lydia them that draw the bow: into Italy, and Greece, to the islands afar off, to them that have not heard of me, and have not seen my glory. And they shall declare my glory to the Gentiles:
20 Za su kuma dawo da dukan’yan’uwanku, daga dukan al’ummai, zuwa dutsena mai tsarki a Urushalima kamar hadaya ga Ubangiji, a kan dawakai, a kekunan yaƙi da wagonu, da kuma a kan alfadarai da kuma raƙuma,” in ji Ubangiji. “Za su kawo su, kamar yadda Isra’ilawa suke kawo hadayun hatsi, zuwa haikalin Ubangiji a cikin tsabtatattun kore.
And they shall bring all your brethren out of all nations for a gift to the Lord, upon horses, and in chariots, and in litters, and on mules, and in coaches, to my holy mountain Jerusalem, saith the Lord, as if the children of Israel should bring an offering in a clean vessel into the house of the Lord.
21 Zan kuwa zaɓa waɗansunsu kuma su zama firistoci da Lawiyawa,” in ji Ubangiji.
And I will take of them to be priests, and Levites, saith the Lord.
22 “Kamar yadda sabuwar duniya da sabuwar sama za su tabbata a gabana,” in ji Ubangiji, “haka sunanku da zuriyarku za su tabbata.
For as the new heavens, and the new earth, which I will make to stand before me, saith the Lord: so shall your seed stand, and your name.
23 Daga wannan sabon wata zuwa wancan, kuma daga wannan Asabbaci zuwa wancan, dukan mutane za su zo su rusuna a gabana,” in ji Ubangiji.
And there shall be month after month, and sabbath after sabbath: and all flesh shall come to adore before my face, saith the Lord.
24 “Za su kuma fita su ga gawawwakin mutanen da suka yi mini tayarwa; tsutsotsin da suke cinsu ba za su taɓa mutuwa ba, balle wutar da take ƙona su ta mutu, za su kuma zama abin ƙyama ga dukan mutane.”
And they shall go out, and see the carcasses of the men that have transgressed against me: their worm shall not die, and their fire shall not be quenched: and they shall be a loathsome sight to all flesh.

< Ishaya 66 >