< Ishaya 66 >
1 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Sama kursiyina ce, duniya kuma matashin sawuna. Ina gidan da za ku gina mini? Ina wurin hutuna zai kasance?
BAWIPA ni hettelah a dei, kalvan teh ka tahungnae bawitungkhung lah ao teh, talai teh ka khoktoungnae lah ao. Namaw im na sak pouh awh han. Namaw ka kâhatnae hmuen ao han.
2 Ba hannuna ba ne ya yi dukan waɗannan abubuwa, ta haka suka kasance?” In ji Ubangiji. “Wannan mutum ne nake jin daɗi, shi da yake mai ƙasƙanci da kuma zuciyar yin tuba, yana kuma rawar jiki ga maganata.
Bangkongtetpawiteh, hete hnocawngca pueng teh, ka kut hoi ka sak teh, kaawmnaw doeh telah BAWIPA ni ati. Hateiteh, ka roedeng naw hoi muitha hoi pankângai e tami, ka lawk dawk ka pâyaw e tami hah ka khet han.
3 Amma duk ya miƙa hadayar bijimi yana kama da wanda ya kashe mutum, kuma duk wanda ya miƙa ɗan rago, kamar wanda ya karye wuyan kare; duk wanda ya miƙa hadaya ta gari yana kama da wanda ya yi sadakar jinin alade, kuma duk wanda ya ƙone turaren tuni, kamar wanda yake bauta gunki ne. Sun zaɓi hanyoyinsu, rayukansu kuma suna jin daɗin abubuwan banƙyamarsu;
Maitotan ka thet e tami teh, tami ka thet e patetlah ao han. Tuca hoi thuengnae ka sak e tami teh, ui lahuen ka khoe e patetlah ao han. Tavai ka poe e tami teh, vok thi ka poe e patetlah ao han. Hmuitui ka thueng e tami teh, meikaphawk yawhawi ka poe e patetlah ao han. Mahoima lamthung ka kârawi e tami teh, panuettho e hno dawk a lungkahawi e patetlah ao han.
4 saboda haka ni ma zan aukar musu da masifa mai zafi in kuma kawo musu abin da suke tsoro. Gama sa’ad da na yi kira, ba wanda ya amsa, sa’ad da na yi magana, ba wanda ya saurara, Sun aikata mugunta a idona suka kuma zaɓa abin da ba na jin daɗi.”
Hottelah amahoima ka kâdum e hah ka rawi han. A taki e hno hah ahnimae lathueng ka pha sak han. Bangkongtetpawiteh, ka kaw nah apinihai na pato hoeh. Lawk ka dei teh thai awh hoeh. Hateiteh, ka mithmu vah, yonnae a sak awh teh, ka lunghawihoehnae hno hah a kârawi awh.
5 Ku ji maganar Ubangiji, ku da kuke rawar jiki ga maganarsa, “’Yan’uwanku da suke ƙinku, suna kuma ware ku saboda sunana, sun ce, ‘Bari a ɗaukaka Ubangiji, don mu ga farin cikinku!’ Duk da haka za su sha kunya.
A lawk dawk ka pâyaw e naw, BAWIPA lawk thai awh haw. Nang ka hmuhma e na hmaunawngha, ka min kecu dawk nangmouh kahreknaw ni, na lunghawinae ka hmu thai awh nahanelah, BAWIPA teh pholennae awm seh telah ati awh, hateiteh a kaya awh han.
6 Ku ji wannan hayaniya daga birni, ku ji surutu daga haikali! Amon Ubangiji ne yana sāka wa abokan gābansa abin da ya dace da su.
Khopui dawk hoi ruengruengtinae, Bawkim dawk hoi hramnae pawlawk, BAWIPA hramnae pawlawk, a tarannaw kakueplah moi a pathungnae pawlawk teh thai awh haw.
7 “Kafin naƙuda ya fara mata, ta haihu; kafin zafi ya zo mata, ta haifi ɗa.
A pataw hoehnahlan a khe teh, von a pataw hoehnahlan camo a khe.
8 Wa ya taɓa jin irin wannan abu? Wa ya taɓa gani irin abubuwan nan? Za a iya ƙirƙiro ƙasa a rana ɗaya ko a haifi al’umma farat ɗaya? Duk da haka da zarar Sihiyona ta fara naƙuda sai ta haifi’ya’yanta.
Hot patet e teh apinimaw a thai boi. Hot patet e teh apinimaw a hmu boi. Hnin touh dawk hoi ram hah khe thai han na maw. Vaitalahoi miphun a tâco thai han na maw. Bangkongtetpawiteh, Zion ni a pataw tahma nah camo tang a khe.
9 Zan kai mace har haihuwa in kuma sa ta kāsa haihu?” In ji Ubangiji. “Zan rufe mahaihuwa sa’ad da lokacin haihuwa ya yi?” In ji Allahnku.
Khenae tueng dawk tâcawt sak laipalah, ka o han na maw, telah BAWIPA ni ati. Ca khesakkung ni ca tawn sak hanelah pasoung laipalah ka o han maw, telah Cathut ni a ti.
10 “Ku yi farin ciki tare da Urushalima ku kuma yi murna saboda ita, dukanku waɗanda kuke ƙaunarta; ku yi farin ciki matuƙa tare da ita, dukanku waɗanda kuke makoki a kanta.
Jerusalem ka lungpataw pueng, Jerusalem teh konawm khai awh. Ama kakhuinaw a ma lunghawikhai nateh konawm awh.
11 Gama za ku tsotsa ku kuma ƙoshi da nonon ta’aziyyarta; za ku sha sosai ku kuma ji daɗin yalwarta.”
Hottelah na teh awh pawiteh, ahnie sanu na net awh vaiteh na boum awh han. Ahnie tawnta e thung hoi rasat vaiteh, na nawm awh han.
12 Gama ga abin da Ubangiji ya faɗa, “Zan fadada salama gare ta kamar kogi, wadatar al’ummai kuma kamar rafi mai gudu; za ku tsotsa a kuma riƙe ku a hannunta ku kuma yi wasa a gwiwoyinta.
BAWIPA ni a dei e teh, roumnae palang patetlah thoseh, Jentelnaw e tawnta e teh ka lawng e tuiphuek tui patetlah thoseh, Jerusalem vah ka pha sak han. Nangmouh teh sanutui na net awh vaiteh, keng dawk tawmnae, khokpakhu dawk tawmnae hah na coe awh han.
13 Kamar yadda uwa takan ta’azantar da ɗanta haka zan ta’azantar da ku; za ku kuma ta’azantu a Urushalima.”
A manu ni a ca lung a mawng sak e patetlah nangmouh lung ka mawng sak han. Jerusalem khopui dawk lung na mawng sak awh han.
14 Sa’ad da kuka ga wannan, zuciyarku za tă yi farin ciki za ku kuma haɓaka kamar ciyawa; za a sanar da hannun Ubangiji ga bayinsa, amma za a nuna wa maƙiyansa fushinsa.
Hote na hmu awh toteh, na lung ahawi awh han. Na hrunaw hah ka hringsuep e thingkung patetlah a thao awh han. BAWIPA e a kut hnotithainae teh sannaw koe thoseh, a lungkhueknae teh a tarannaw koe a kamnue han.
15 Ga shi, Ubangiji yana zuwa da wuta, kuma kekunan yaƙinsa suna kama da guguwa; zai sauko da fushinsa da zafi, tsawatawarsa kuma da harsunan wuta.
Khenhaw! a lungphuennae ka patawpoung lah a kamnue nahane hoi, na yuenae hmaisaan patetlah a kamnue nahanelah, BAWIPA teh hmai rangleng hoi bongparui patetlah a tho han.
16 Gama da wuta da kuma takobi Ubangiji zai yi hukunci a kan dukan mutane, kuma yawanci za su kasance waɗanda Ubangiji zai kashe.
Bangkongtetpawiteh, hmai hoi tahloi hoi, BAWIPA ni takthai hoi kahringnaw pueng lawk a ceng han. BAWIPA ni a thei e teh a pap poung han.
17 “Waɗanda suka tsarkake suka kuma tsabtacce kansu don su je lambu, suna bin wannan da yake tsakiya waɗannan da suke cin naman aladu da ɓeraye da waɗansu abubuwan banƙyama, za su sadu da ƙarshensu tare,” in ji Ubangiji.
Mahoima kâthoung sak hane hoi, mahoima kâkapek hanelah, takha koe kacetnaw, meikaphawknaw rahak vah, pou ka cet e, vokmoi hoi panuettho e moihnam moi ka cat e naw pueng cungtalah he a kahma awh han telah BAWIPA ni a ti.
18 “Ni kuwa, saboda ayyukansu da kuma tunaninsu, ina dab da zuwa in tattara dukan al’ummai da harsuna, za su kuma zo su ga ɗaukakata.
Bangkongtetpawiteh, a sak awh e hoi a pouk awh e ka panue, miphun tangkuem hoi lawk phunkuep tangkuem hah, ka pâkhuengnae tueng a pha han. Tho awh vaiteh ka bawilennae hah a hmu awh han.
19 “Zan kafa alama a cikinsu, zan kuma aika waɗansu da suka tsira zuwa al’ummai, zuwa Tarshish, zuwa Libiya da Lidiya (sanannun’yan aika), zuwa Tubal da kuma Girka, da kuma zuwa manisantan tsibirai da ba su taɓa jin labarin sunana ba ko su ga ɗaukakata. Za su yi shelar ɗaukakata a cikin al’ummai.
Ahnimouh koe kamnuenae hah ka o sak han. Hahoi teh, ahnimouh rahak vah, rektapnae koehoi ka hlout e ka miphun tangkuem koe, Tarshish, Pul, licung longkawi e Lud, Tubal hoi Javan, ka min kamthangnae ka panuek boihoeh e naw koe, tuipui namran ahlanae koe ka thak han. Hottelah, Jentelnaw koe ka bawilennae a pâpho awh han.
20 Za su kuma dawo da dukan’yan’uwanku, daga dukan al’ummai, zuwa dutsena mai tsarki a Urushalima kamar hadaya ga Ubangiji, a kan dawakai, a kekunan yaƙi da wagonu, da kuma a kan alfadarai da kuma raƙuma,” in ji Ubangiji. “Za su kawo su, kamar yadda Isra’ilawa suke kawo hadayun hatsi, zuwa haikalin Ubangiji a cikin tsabtatattun kore.
Hahoi Isarelnaw ni, kathounge hlaam hah thueng e hno lah BAWIPA e im dawk ouk a thokhai e patetlah miphunnaw pueng thung dawk hai na hmaunawnghanaw hah marang dawk hoi thoseh, leng dawk hoi thoseh, kâkayawt e van hoi thoseh, la dawk hoi thoseh, kalauk dawk hoi thoseh, Jerusalem mon kathoung dawk BAWIPA koe ouk a thueng awh e patetlah a thokhai awh han telah BAWIPA ni a ti.
21 Zan kuwa zaɓa waɗansunsu kuma su zama firistoci da Lawiyawa,” in ji Ubangiji.
Hotnaw thung dawk hoi tami tangawn vaihma hoi Levihnaw hanelah ka la han telah BAWIPA ni a ti.
22 “Kamar yadda sabuwar duniya da sabuwar sama za su tabbata a gabana,” in ji Ubangiji, “haka sunanku da zuriyarku za su tabbata.
Bangkongtetpawiteh, kalvan katha hoi talai katha ka sak hane teh, ka hmalah ka kangning hane patetlah, na catounnaw hoi na min a kangning han telah BAWIPA ni a ti.
23 Daga wannan sabon wata zuwa wancan, kuma daga wannan Asabbaci zuwa wancan, dukan mutane za su zo su rusuna a gabana,” in ji Ubangiji.
Hahoi teh, hettelah han. Thapa a reinae koehoi bout a rei katha totouh, sabbath hnin hoi alouke sabbath hnin totouh moithangnaw pueng Kai bawk hanelah ka hmalah a tho awh han telah BAWIPA ni a ti.
24 “Za su kuma fita su ga gawawwakin mutanen da suka yi mini tayarwa; tsutsotsin da suke cinsu ba za su taɓa mutuwa ba, balle wutar da take ƙona su ta mutu, za su kuma zama abin ƙyama ga dukan mutane.”
Tâcawt awh vaiteh, kai taranlahoi kâ kaeknaw e ro hah a khet awh han. Bangkongtetpawiteh, pâri hai dout thai hoeh ni teh hmai hai roum thai mahoeh. Tami pueng hanelah teh panuet a tho han.