< Ishaya 65 >
1 “Na bayyana kaina ga waɗanda ba su tambaye ni ba; ina samuwa ga waɗanda ba su neme ni ba. Ga al’ummar da ba tă kira bisa sunana ba, Na ce, ‘Ga ni, ga ni.’
Jag varder sökt af dem som intet efter mig frågade; jag varder funnen af dem som intet sökte mig; och till Hedningarna, som mitt Namn intet åkallade, säger jag: Här är jag, här är jag.
2 Dukan yini ina miƙa hannuwana ga mutane masu tayarwa, waɗanda suna tafiya a hanyoyin da ba su da kyau, suna bin tunaninsu,
Ty jag uträcker mina händer hela dagen till ett ohörsamt folk, som efter sina tankar vandrar på den väg, som intet god är.
3 mutanen da suna cin gaba da tsokanata a fuskata, suna miƙa hadayu a gonaki suna ƙone turare a bagadan tubali;
Ett folk, som mig förtörnar, är alltid för mitt ansigte; offrar i örtagårdom, och röker på tegelstenar;
4 suna zama a kaburbura su kwana suna yin asirtattun ayyuka; suna cin naman aladu, tukwanensu kuma sun cika da nama marar tsabta;
Bor ibland grifter, och håller sig uti kulor; äta svinakött, och hafva förbudet såd uti deras grytor;
5 suna cewa, ‘Ku tsaya a can; kada ku yi kusa da ni, gama na fi ku tsarki!’ Irin mutanen nan hayaƙi ne a hancina, wuta kuma da take cin gaba da ci dukan yini.
Och säga: Blif hemma, och kom intet vid mig; ty jag skall helga dig. Desse skola varda en rök i mine vrede, en eld, som brinner hela dagen.
6 “Ga shi, yana nan a rubuce a gabana cewa ba zan ƙyale ba, zan yi cikakken ramuwa; zan yi ramuwa a cinyoyinsu
Si, det står skrifvet för mig: Jag vill icke tiga, utan betala; ja, jag vill betala dem i deras sköt;
7 saboda zunubanku da kuma zunuban kakanninku,” in ji Ubangiji. “Gama sun ƙone turare a kan duwatsu suka kuma ƙazantar da ni a kan tuddai, zan yi musu awo in zuba a cinyoyinsu cikakken ramuwa saboda ayyukansu na dā.”
Både deras missgerningar, och deras fäders missgerningar tillsammans, säger Herren; de som på bergen rökt, och mig på högarna försmädat hafva; jag skall mäta dem deras förra väsende uti deras sköt.
8 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kamar sa’ad da ruwan’ya’yan itace yana samuwa a cikin tarin’ya’yan inabi mutane kuma su ce, ‘Kada a lalace shi, har yanzu akwai abu mai kyau a ciki,’ haka nan zan yi a madadin bayina; ba zan hallaka su duka ba.
Så säger Herren: Likasom då man must finner uti vindrufvone, och säger: Förderfva det icke, ty der är en välsignelse uti; alltså vill jag för mina tjenares skull göra, att jag icke förderfvar det allt;
9 Zan fitar da zuriyar Yaƙub, daga Yahuda kuma waɗanda za su mallaki duwatsuna; zaɓaɓɓun mutanena za su gāje su, a can kuma bayina za su zauna.
Utan vill låta växa utaf Jacob säd, och af Juda den som mitt berg besitta skall; ty mine utkorade skola besitta det, och mine tjenare skola der bo.
10 Sharon zai zama wurin kiwo don shanu, Kwarin Akor kuma wurin hutun garkuna, domin mutanena da suke nemana.
Och Saron skall vara ett hus för hjordar, och Achors dal skall ett fälägre varda, mino folke som mig söka.
11 “Amma game da ku waɗanda kuka yashe Ubangiji kuka manta da dutsena mai tsarki kuwa, ku da kuka shimfiɗa tebur don sa’a kuka kuma cika darunan ruwan inabin da aka dama don Ƙaddara,
Men I som Herran förlåten, och mitt helga berg förgäten, och uppresen till Gad ett bord, och skänken fullt in af drickoffer för Meni;
12 zan ƙaddara ku ga kaifin takobi, dukanku kuma za ku sunkuya wa mai yanka; gama na yi kira amma ba ku amsa ba, na yi magana amma ba ku saurara ba. Kuka aikata mugunta a gabana kuka kuma zaɓi abin da ba na jin daɗi.”
Nu väl, jag vill uträkna eder till svärd, så att I alla måsten bocka eder till slagtning; derföre, att jag kallade, och I svaraden intet; jag talade, och I hörden intet, utan gjorden det mig misstyckte, och utvalden det mig intet täckt var.
13 Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “Bayin za su ci, amma ku za ku ji yunwa; bayina za su sha, amma ku za ku ji ƙishi; bayina za su yi farin ciki amma ku za ku sha kunya.
Derföre säger Herren Herren alltså: Si, mine tjenare skola äta; men I skolen hungra; Si, mine tjenare skola dricka, men I skolen törsta; si, mine tjenare skola glade vara, men I skolen till skam varda;
14 Bayina za su rera da farin cikin zukatansu, amma ku za ku yi kuka daga wahalar zuciya ku kuma yi kururuwa da karayar zuci.
Si, mine tjenare skola fröjda sig för godt mods skull; men I skolen för hjertans sorgs skull ropa, och för jämmer gråta;
15 Za ku bar sunanku ga zaɓaɓɓuna yă zama abin la’antarwa; Ubangiji Mai Iko Duka zai kashe ku, amma ga bayina zai ba su wani suna.
Och skolen låta edor namn minom utkoradom till ett svärjande: och Herren Herren skall döda dig, och nämna sina tjenare med ett annat namn;
16 Duk wanda zai roƙi albarka a cikin ƙasar zai yi haka da gaskiyar Allah; wanda zai yi rantsuwa a cikin ƙasar zai rantse da gaskiyar Allah. Gama za a manta da wahalolin baya a kuma ɓoye su daga idanuna.
Så att den som sig välsignar på jordene, han skall välsigna sig uti den rätta Guden; och den som svär på jordene, han skall svärja vid den rätta Guden; ty de förra bedröfvelser äro förgätne, och äro förskyld för min ögon.
17 “Ga shi, na halicci sabuwar sama da kuma sabuwar duniya. Abubuwa na dā za a manta da su, ba kuwa za a ƙara tuna da su ba.
Ty si, jag vill skapa en ny himmel, och ena nya jord; så att man intet mer skall komma den förra, ihåg, eller lägga dem på hjertat;
18 Amma ku yi murna ku kuma yi farin ciki har abada a abin da na halitta, gama zan halicci Urushalima ta zama abin murna mutanenta kuwa abin farin ciki.
Utan de skola fröjda sig evinnerliga, och glade vara öfver det som jag skapar; ty si, jag vill skapa Jerusalem till fröjd, och dess folk till glädje.
19 Zan yi farin ciki a kan Urushalima in kuma yi murna saboda mutanena; a can ba za a ƙara jin karar makoki da na kuka ba.
Och jag vill glad vara öfver Jerusalem, och fröjda mig öfver mitt folk; och gråtoröst eller klagoröst skall icke mer derinne hörd varda.
20 “A cikinta ba za a ƙara jin jariri ya rayu na’yan kwanaki kawai ba, ko kuwa wani tsohon da bai cika kwanakinsa ba; duk wanda ya mutu yana da shekaru ɗari za a ce ya mutu a kurciya ne kawai; duk wanda bai kai ɗari ba za a ɗauka la’antacce ne.
Der skola icke mer vara barn, som icke räcka till deras dagar, eller gamle som deras år icke uppfylla; utan hundradeåra barn skola dö, och de hundradeåra syndare skola förbannade varda.
21 Za su gina gidaje su kuma zauna a cikinsu; za su yi shuki a gonakin inabi su kuma ci’ya’yansu.
De skola bygga hus, och bo deruti; de skola plantera vingårdar, och äta fruktena af dem.
22 Ba za su ƙara gina gidaje waɗansu kuma su zauna a cikinsu ba, ko su yi shuki waɗansu kuma su ci ba. Gama kamar yadda kwanakin itace suke, haka kwanakin mutanena za su kasance; zaɓaɓɓuna za su daɗe suna jin daɗin ayyukan hannuwansu.
De skola icke bygga, att en annar bor deruti, och icke plantera, att en annar äter; ty mins folks dagar skola vara såsom ett träs dagar, och deras händers verk skall föråldras när mina utkorade.
23 Ba za su yi wahala a banza ba ko su haifi’ya’yan da aka ƙaddara da rashin sa’a; gama za su zama mutanen da Ubangiji ya yi wa albarka, su da zuriyarsu tare da su.
De skola icke arbeta fåfängt, eller föda otidiga födslo; ty de äro Herrans välsignadas säd, och deras efterkommande med dem.
24 Kafin su yi kira zan amsa; yayinda suke cikin magana zan ji.
Och skall ske, att förr än de ropa, vill jag svara; medan de ännu tala, vill jag höra.
25 Kyarketai da’yan raguna za su ci abinci tare, zaki kuma zai ci buɗu kamar yadda shanu suke yi, amma ƙura ce za tă zama abincin maciji. Ba za su ƙara cuci ko su yi ɓarna a kan dukan dutsena mai tsarki ba,” in ji Ubangiji.
Ulfven och lambet skola gå i bet tillsamman; lejonet skall äta strå, såsom ett nöt, och ormen skall äta jord; de skola ingen skada eller förderf göra på hela mitt helga berg, säger Herren.