< Ishaya 65 >
1 “Na bayyana kaina ga waɗanda ba su tambaye ni ba; ina samuwa ga waɗanda ba su neme ni ba. Ga al’ummar da ba tă kira bisa sunana ba, Na ce, ‘Ga ni, ga ni.’
Ils m’ont cherché, ceux qui auparavant ne m’interrogeaient pas; ils m’ont trouvé, ceux qui ne m’ont pas cherché; j’ai dit: Me voici, me voici, à une nation qui n’invoquait pas mon nom.
2 Dukan yini ina miƙa hannuwana ga mutane masu tayarwa, waɗanda suna tafiya a hanyoyin da ba su da kyau, suna bin tunaninsu,
J’ai étendu mes mains tout le jour à un peuple incrédule, qui marche dans une voie qui n’est pas bonne, à la suite de ses pensées.
3 mutanen da suna cin gaba da tsokanata a fuskata, suna miƙa hadayu a gonaki suna ƙone turare a bagadan tubali;
C’est un peuple qui me provoque au courroux devant ma face sans cesse; qui immolent dans les jardins, et sacrifient sur les briques;
4 suna zama a kaburbura su kwana suna yin asirtattun ayyuka; suna cin naman aladu, tukwanensu kuma sun cika da nama marar tsabta;
Qui habitent dans les sépulcres, qui dorment dans les temples des idoles; qui mangent de la chair de porc, et mettent du jus profane dans leurs vases;
5 suna cewa, ‘Ku tsaya a can; kada ku yi kusa da ni, gama na fi ku tsarki!’ Irin mutanen nan hayaƙi ne a hancina, wuta kuma da take cin gaba da ci dukan yini.
Qui disent: Retire-toi de moi, ne m’approche pas, parce que tu es impur; ceux-là seront une fumée dans ma fureur, un feu brûlant tout le jour.
6 “Ga shi, yana nan a rubuce a gabana cewa ba zan ƙyale ba, zan yi cikakken ramuwa; zan yi ramuwa a cinyoyinsu
Voilà que c’est écrit devant moi; je ne me tairai pas, mais je rendrai, et je verserai dans leur sein
7 saboda zunubanku da kuma zunuban kakanninku,” in ji Ubangiji. “Gama sun ƙone turare a kan duwatsu suka kuma ƙazantar da ni a kan tuddai, zan yi musu awo in zuba a cinyoyinsu cikakken ramuwa saboda ayyukansu na dā.”
Vos iniquités, dit le Seigneur, en même temps que les iniquités de vos pères, qui ont sacrifié sur les montagnes, et m’ont outragé sur les collines, et je verserai leurs premières œuvres à égale mesure dans leur sein.
8 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kamar sa’ad da ruwan’ya’yan itace yana samuwa a cikin tarin’ya’yan inabi mutane kuma su ce, ‘Kada a lalace shi, har yanzu akwai abu mai kyau a ciki,’ haka nan zan yi a madadin bayina; ba zan hallaka su duka ba.
Voici ce que dit le Seigneur: De même que si on trouve un grain dans une grappe de raisin, et Sion dit: Ne le perds pas, parce que c’est une bénédiction, de même aussi je ferai en sorte, à cause de mes serviteurs, que je ne perde pas entièrement tout Israël.
9 Zan fitar da zuriyar Yaƙub, daga Yahuda kuma waɗanda za su mallaki duwatsuna; zaɓaɓɓun mutanena za su gāje su, a can kuma bayina za su zauna.
Je ferai sortir de Jacob une postérité, et de Juda celui qui possédera mes montagnes; mes élus hériteront de cette terre et mes serviteurs y habiteront.
10 Sharon zai zama wurin kiwo don shanu, Kwarin Akor kuma wurin hutun garkuna, domin mutanena da suke nemana.
Et les campagnes serviront de parcs aux troupeaux de menu bétail, et la vallée d’Achor, de retraite aux troupeaux de gros bétail, en faveur de ceux de mon peuple qui m’ont recherché.
11 “Amma game da ku waɗanda kuka yashe Ubangiji kuka manta da dutsena mai tsarki kuwa, ku da kuka shimfiɗa tebur don sa’a kuka kuma cika darunan ruwan inabin da aka dama don Ƙaddara,
Mais vous qui avez abandonné le Seigneur, qui avez oublié ma montagne sainte, qui dressez une table à la Fortune, et y faites des libations,
12 zan ƙaddara ku ga kaifin takobi, dukanku kuma za ku sunkuya wa mai yanka; gama na yi kira amma ba ku amsa ba, na yi magana amma ba ku saurara ba. Kuka aikata mugunta a gabana kuka kuma zaɓi abin da ba na jin daɗi.”
Je vous compterai avec le glaive, et tous vous tomberez dans ce carnage, parce que j’ai appelé, et vous n’avez pas répondu; j’ai parlé, et vous n’avez pas écouté; vous faisiez le mal à mes yeux, et tout ce que je n’ai pas voulu, vous l’avez choisi.
13 Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “Bayin za su ci, amma ku za ku ji yunwa; bayina za su sha, amma ku za ku ji ƙishi; bayina za su yi farin ciki amma ku za ku sha kunya.
À cause de cela voici ce que dit le Seigneur Dieu: Voilà que mes serviteurs mangeront, et vous, vous aurez faim; voilà que mes serviteurs boiront, et vous, vous aurez soif;
14 Bayina za su rera da farin cikin zukatansu, amma ku za ku yi kuka daga wahalar zuciya ku kuma yi kururuwa da karayar zuci.
Voilà que mes serviteurs se réjouiront, et vous, vous serez confus; voilà que mes serviteurs chanteront des louanges dans l’exultation de leur cœur, et vous, vous jetterez des cris dans la douleur de votre cœur, et dans le brisement de votre esprit vous pousserez des hurlements.
15 Za ku bar sunanku ga zaɓaɓɓuna yă zama abin la’antarwa; Ubangiji Mai Iko Duka zai kashe ku, amma ga bayina zai ba su wani suna.
Et vous laisserez votre nom à mes serviteurs comme un objet d’imprécation; et le Seigneur Dieu te détruira, et il appellera ses serviteurs d’un autre nom,
16 Duk wanda zai roƙi albarka a cikin ƙasar zai yi haka da gaskiyar Allah; wanda zai yi rantsuwa a cikin ƙasar zai rantse da gaskiyar Allah. Gama za a manta da wahalolin baya a kuma ɓoye su daga idanuna.
Dans lequel celui qui est béni sur la terre sera béni dans le Dieu de vérité, et celui qui jure sur la terre jurera par le Dieu de vérité; parce qu’à l’oubli ont été livrées les premières angoisses, et qu’elles ont été cachées à ma face.
17 “Ga shi, na halicci sabuwar sama da kuma sabuwar duniya. Abubuwa na dā za a manta da su, ba kuwa za a ƙara tuna da su ba.
Car voici que je crée des cieux nouveaux et une terre nouvelle; les choses passées ne seront pas dans la mémoire, et elles ne monteront pas sur le cœur.
18 Amma ku yi murna ku kuma yi farin ciki har abada a abin da na halitta, gama zan halicci Urushalima ta zama abin murna mutanenta kuwa abin farin ciki.
Mais vous vous réjouirez, vous exulterez à jamais dans les choses que je crée; parce que voici que je crée Jérusalem exultation, et son peuple joie.
19 Zan yi farin ciki a kan Urushalima in kuma yi murna saboda mutanena; a can ba za a ƙara jin karar makoki da na kuka ba.
Et j’exulterai en Jérusalem, et je me réjouirai en mon peuple; et on n’y entendra plus la voix du pleur et la voix du cri.
20 “A cikinta ba za a ƙara jin jariri ya rayu na’yan kwanaki kawai ba, ko kuwa wani tsohon da bai cika kwanakinsa ba; duk wanda ya mutu yana da shekaru ɗari za a ce ya mutu a kurciya ne kawai; duk wanda bai kai ɗari ba za a ɗauka la’antacce ne.
Il n’y aura plus là d’enfants de peu de jours, et de vieillard qui ne remplisse ses jours; parce que l’enfant mourra à cent ans, et que le pécheur de cent ans sera maudit.
21 Za su gina gidaje su kuma zauna a cikinsu; za su yi shuki a gonakin inabi su kuma ci’ya’yansu.
Et ils bâtiront des maisons et ils les habiteront; ils planteront des vignes et ils en mangeront les fruits.
22 Ba za su ƙara gina gidaje waɗansu kuma su zauna a cikinsu ba, ko su yi shuki waɗansu kuma su ci ba. Gama kamar yadda kwanakin itace suke, haka kwanakin mutanena za su kasance; zaɓaɓɓuna za su daɗe suna jin daɗin ayyukan hannuwansu.
Ils ne bâtiront pas pour qu’un autre habite; ils ne planteront pas pour qu’un autre mange; car à l’égal des jours de l’arbre, seront les jours de mon peuple; et les ouvrages de leurs mains auront une longue durée;
23 Ba za su yi wahala a banza ba ko su haifi’ya’yan da aka ƙaddara da rashin sa’a; gama za su zama mutanen da Ubangiji ya yi wa albarka, su da zuriyarsu tare da su.
Mes élus ne travailleront pas en vain, et ils n’engendreront pas dans le trouble; parce qu’ils sont la race des bénis du Seigneur, et que leurs descendants seront bénis avec eux.
24 Kafin su yi kira zan amsa; yayinda suke cikin magana zan ji.
Et il arrivera qu’avant qu’ils crient, moi je les exaucerai; eux parlant encore, j’écouterai.
25 Kyarketai da’yan raguna za su ci abinci tare, zaki kuma zai ci buɗu kamar yadda shanu suke yi, amma ƙura ce za tă zama abincin maciji. Ba za su ƙara cuci ko su yi ɓarna a kan dukan dutsena mai tsarki ba,” in ji Ubangiji.
Le loup et l’agneau paîtront ensemble; le lion et le bœuf mangeront la paille, et pour le serpent, la poussière sera son pain; ils ne nuiront point, et ils ne tueront point sur toute ma montagne sainte, dit le Seigneur.