< Ishaya 65 >

1 “Na bayyana kaina ga waɗanda ba su tambaye ni ba; ina samuwa ga waɗanda ba su neme ni ba. Ga al’ummar da ba tă kira bisa sunana ba, Na ce, ‘Ga ni, ga ni.’
I allowed myself to be sought by those that asked not; I let myself be found by those that sought me not: I said, Here am I, here am I, unto a nation that called itself not by my name.
2 Dukan yini ina miƙa hannuwana ga mutane masu tayarwa, waɗanda suna tafiya a hanyoyin da ba su da kyau, suna bin tunaninsu,
I spread out my hands all the time unto a rebellious people, that walk in the way which is not good, after their own thoughts;
3 mutanen da suna cin gaba da tsokanata a fuskata, suna miƙa hadayu a gonaki suna ƙone turare a bagadan tubali;
[To] the people that provoke me to anger to my face continually; that sacrifice in gardens and burn incense upon [altars of] brick,
4 suna zama a kaburbura su kwana suna yin asirtattun ayyuka; suna cin naman aladu, tukwanensu kuma sun cika da nama marar tsabta;
That sit about among the graves, and lodge in the vaults, that eat the flesh of the swine, and [have] broth of abominations [in] their vessels;
5 suna cewa, ‘Ku tsaya a can; kada ku yi kusa da ni, gama na fi ku tsarki!’ Irin mutanen nan hayaƙi ne a hancina, wuta kuma da take cin gaba da ci dukan yini.
That say, Stand by thyself, come not near to me; for I am holier than thou. These are a smoke in my nose, a fire that burneth all the time.
6 “Ga shi, yana nan a rubuce a gabana cewa ba zan ƙyale ba, zan yi cikakken ramuwa; zan yi ramuwa a cinyoyinsu
Behold, it is written before me; I will not keep silence, till I have recompensed, yea, recompensed into their bosom.—
7 saboda zunubanku da kuma zunuban kakanninku,” in ji Ubangiji. “Gama sun ƙone turare a kan duwatsu suka kuma ƙazantar da ni a kan tuddai, zan yi musu awo in zuba a cinyoyinsu cikakken ramuwa saboda ayyukansu na dā.”
Your iniquities and the iniquities of your fathers together, saith the Lord, who have burnt incense upon the mountains, and upon the hills have blasphemed me: and I will measure out their work at first into their bosom.
8 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kamar sa’ad da ruwan’ya’yan itace yana samuwa a cikin tarin’ya’yan inabi mutane kuma su ce, ‘Kada a lalace shi, har yanzu akwai abu mai kyau a ciki,’ haka nan zan yi a madadin bayina; ba zan hallaka su duka ba.
Thus hath said the Lord, As the new wine is found in the cluster of grapes, and one saith, Destroy it not, for a blessing is in it; so will I do for the sake of my servants, that I will not destroy the whole;
9 Zan fitar da zuriyar Yaƙub, daga Yahuda kuma waɗanda za su mallaki duwatsuna; zaɓaɓɓun mutanena za su gāje su, a can kuma bayina za su zauna.
And I let come forth out of Jacob a seed, and out of Judah an inheritor of my mountains; and my elect shall inherit it, and my servants shall dwell there.
10 Sharon zai zama wurin kiwo don shanu, Kwarin Akor kuma wurin hutun garkuna, domin mutanena da suke nemana.
And Sharon shall become a fold of flocks, and the valley of 'Achor a resting-place for herds, for my people that have sought me.
11 “Amma game da ku waɗanda kuka yashe Ubangiji kuka manta da dutsena mai tsarki kuwa, ku da kuka shimfiɗa tebur don sa’a kuka kuma cika darunan ruwan inabin da aka dama don Ƙaddara,
But ye who forsake the Lord, who forget my holy mountain, that set out a table for the god of Fortune, and that fill for Destiny the drink-offering.—
12 zan ƙaddara ku ga kaifin takobi, dukanku kuma za ku sunkuya wa mai yanka; gama na yi kira amma ba ku amsa ba, na yi magana amma ba ku saurara ba. Kuka aikata mugunta a gabana kuka kuma zaɓi abin da ba na jin daɗi.”
Yea, I will destine you to the sword, and all of you shall kneel down to the slaughter; because when I called, ye did not answer; when I spoke, ye did not hear; but ye did what is evil in my eyes, and that wherein I had no delight did ye choose.
13 Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “Bayin za su ci, amma ku za ku ji yunwa; bayina za su sha, amma ku za ku ji ƙishi; bayina za su yi farin ciki amma ku za ku sha kunya.
Therefore thus hath said the Lord Eternal, Behold, my servants shall eat, but ye shall be hungry; behold, my servants shall drink, but ye shall be thirsty; behold, my servants shall rejoice, but ye shall be made ashamed;
14 Bayina za su rera da farin cikin zukatansu, amma ku za ku yi kuka daga wahalar zuciya ku kuma yi kururuwa da karayar zuci.
Behold, my servants shall sing for joy of heart, but ye shall cry out from pain of heart, and from a broken spirit shall ye howl;
15 Za ku bar sunanku ga zaɓaɓɓuna yă zama abin la’antarwa; Ubangiji Mai Iko Duka zai kashe ku, amma ga bayina zai ba su wani suna.
And ye shall leave behind your name for an oath unto my elect ones, when the Lord Eternal will slay thee; but his servants will he call by another name.
16 Duk wanda zai roƙi albarka a cikin ƙasar zai yi haka da gaskiyar Allah; wanda zai yi rantsuwa a cikin ƙasar zai rantse da gaskiyar Allah. Gama za a manta da wahalolin baya a kuma ɓoye su daga idanuna.
Whoever there be that blesseth himself on the earth shall bless himself by the true God; and that sweareth on the earth shall swear by the true God; because the former troubles are forgotten, and because they are hidden from my eyes.
17 “Ga shi, na halicci sabuwar sama da kuma sabuwar duniya. Abubuwa na dā za a manta da su, ba kuwa za a ƙara tuna da su ba.
For, behold, I will create new heavens and a new earth; and the former shall not be remembered, nor come into mind;
18 Amma ku yi murna ku kuma yi farin ciki har abada a abin da na halitta, gama zan halicci Urushalima ta zama abin murna mutanenta kuwa abin farin ciki.
But be ye glad and rejoice unto all eternity in what I create; for, behold, I will create Jerusalem for rejoicing, and her people for gladness.
19 Zan yi farin ciki a kan Urushalima in kuma yi murna saboda mutanena; a can ba za a ƙara jin karar makoki da na kuka ba.
And I will rejoice over Jerusalem, and be glad in my people: and there shall not be heard in her any more the voice of weeping, nor the voice of complaint.
20 “A cikinta ba za a ƙara jin jariri ya rayu na’yan kwanaki kawai ba, ko kuwa wani tsohon da bai cika kwanakinsa ba; duk wanda ya mutu yana da shekaru ɗari za a ce ya mutu a kurciya ne kawai; duk wanda bai kai ɗari ba za a ɗauka la’antacce ne.
There shall no more come thence an infant of few days, nor an old man that shall not have the full length of his days; for as a lad shall one die a hundred years old; and as a sinner shall be accursed he who [dieth] at a hundred years old.
21 Za su gina gidaje su kuma zauna a cikinsu; za su yi shuki a gonakin inabi su kuma ci’ya’yansu.
And they shall build houses, and inhabit them; and they shall plant vineyards, and eat their fruit.
22 Ba za su ƙara gina gidaje waɗansu kuma su zauna a cikinsu ba, ko su yi shuki waɗansu kuma su ci ba. Gama kamar yadda kwanakin itace suke, haka kwanakin mutanena za su kasance; zaɓaɓɓuna za su daɗe suna jin daɗin ayyukan hannuwansu.
They shall not build, and another inhabit; they shall not plant, and another eat; for as the days of a tree are the days of my people, and the work of their hands shall my elect wear out.
23 Ba za su yi wahala a banza ba ko su haifi’ya’yan da aka ƙaddara da rashin sa’a; gama za su zama mutanen da Ubangiji ya yi wa albarka, su da zuriyarsu tare da su.
They shall not toil in vain, nor bring forth unto an early death; for the seed of the blessed of the Lord are they, and their offspring with them.
24 Kafin su yi kira zan amsa; yayinda suke cikin magana zan ji.
And it shall come to pass, that before yet they call will I answer; and while they are still speaking will I hear.
25 Kyarketai da’yan raguna za su ci abinci tare, zaki kuma zai ci buɗu kamar yadda shanu suke yi, amma ƙura ce za tă zama abincin maciji. Ba za su ƙara cuci ko su yi ɓarna a kan dukan dutsena mai tsarki ba,” in ji Ubangiji.
The wolf and the lamb shall feed together, and the lion shall like the bullock eat straw: and the serpent—dust shall be his food. They shall not hurt nor destroy in all my holy mountain, saith the Lord.

< Ishaya 65 >