< Ishaya 65 >
1 “Na bayyana kaina ga waɗanda ba su tambaye ni ba; ina samuwa ga waɗanda ba su neme ni ba. Ga al’ummar da ba tă kira bisa sunana ba, Na ce, ‘Ga ni, ga ni.’
從未求問我的,我要讓他尋求我;從未尋找我的,我要讓他找到我;我對那從未稱呼我名的民族說:「看,我在這裏!我在這裏!」
2 Dukan yini ina miƙa hannuwana ga mutane masu tayarwa, waɗanda suna tafiya a hanyoyin da ba su da kyau, suna bin tunaninsu,
我整天向悖逆的民族,即隨自己的思念走邪辟路的人,伸出我的手。
3 mutanen da suna cin gaba da tsokanata a fuskata, suna miƙa hadayu a gonaki suna ƙone turare a bagadan tubali;
這民族時常在我面前惹我發怒,在園中獻祭,在磚台上焚香;
4 suna zama a kaburbura su kwana suna yin asirtattun ayyuka; suna cin naman aladu, tukwanensu kuma sun cika da nama marar tsabta;
他們住在墳墓內,宿在隱密處,吃豬肉,在他們的器皿中都是些不潔之物,
5 suna cewa, ‘Ku tsaya a can; kada ku yi kusa da ni, gama na fi ku tsarki!’ Irin mutanen nan hayaƙi ne a hancina, wuta kuma da take cin gaba da ci dukan yini.
他們還對人說:「站遠點,別靠近我,怕我聖潔了你。」這些事真叫我鼻子冒煙,整日冒火。
6 “Ga shi, yana nan a rubuce a gabana cewa ba zan ƙyale ba, zan yi cikakken ramuwa; zan yi ramuwa a cinyoyinsu
看哪!這一切已在我面前寫定;我決不緘默,我非報復不可。
7 saboda zunubanku da kuma zunuban kakanninku,” in ji Ubangiji. “Gama sun ƙone turare a kan duwatsu suka kuma ƙazantar da ni a kan tuddai, zan yi musu awo in zuba a cinyoyinsu cikakken ramuwa saboda ayyukansu na dā.”
我要一起報復他們的罪惡和他們祖先的罪惡:上主說。因為他們在山上燒過香,在丘陵上褻謾過我,所以我要量好他們應得的報酬,報應到他們的懷中。
8 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kamar sa’ad da ruwan’ya’yan itace yana samuwa a cikin tarin’ya’yan inabi mutane kuma su ce, ‘Kada a lalace shi, har yanzu akwai abu mai kyau a ciki,’ haka nan zan yi a madadin bayina; ba zan hallaka su duka ba.
上主這樣說:「就如當人發現葡萄內尚有酒汁時,就說:不要破壞它,因為裏面還有祝福;我為了我的僕人也要這樣作,不將他們完全消滅。
9 Zan fitar da zuriyar Yaƙub, daga Yahuda kuma waɗanda za su mallaki duwatsuna; zaɓaɓɓun mutanena za su gāje su, a can kuma bayina za su zauna.
我要使雅各伯生出苗裔,使猶大生出繼承我山的人;我的選民要以她為業,我的僕人要住在那裏。
10 Sharon zai zama wurin kiwo don shanu, Kwarin Akor kuma wurin hutun garkuna, domin mutanena da suke nemana.
為那尋求我的百姓,沙龍將成為羊群的牧場,阿苛爾山谷為那尋求我的百姓,要成為牛群的棲所。」「
11 “Amma game da ku waɗanda kuka yashe Ubangiji kuka manta da dutsena mai tsarki kuwa, ku da kuka shimfiɗa tebur don sa’a kuka kuma cika darunan ruwan inabin da aka dama don Ƙaddara,
至於你們這些離棄上主,忘記我的聖山,為加得神設宴,給默尼神注滿調和的酒的人,
12 zan ƙaddara ku ga kaifin takobi, dukanku kuma za ku sunkuya wa mai yanka; gama na yi kira amma ba ku amsa ba, na yi magana amma ba ku saurara ba. Kuka aikata mugunta a gabana kuka kuma zaɓi abin da ba na jin daɗi.”
我注定了你們歸於刀下,你們要屈身受戮;因為我喊叫你們,你們沒有回答;我說話,你們不肯聽,反而去行我視為惡的事,揀選我所不喜歡的事。」
13 Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “Bayin za su ci, amma ku za ku ji yunwa; bayina za su sha, amma ku za ku ji ƙishi; bayina za su yi farin ciki amma ku za ku sha kunya.
因此吾主上主這樣說:「你們要看見我的僕人有得吃,你們卻要飢餓;你們看見我的僕人有得喝,你們卻要口渴;你們看見我的僕人喜樂,你們卻要哭泣;
14 Bayina za su rera da farin cikin zukatansu, amma ku za ku yi kuka daga wahalar zuciya ku kuma yi kururuwa da karayar zuci.
你們看見我的僕人因心中快樂而歡慶,你們卻要因心中憂苦而悲號,因喪氣而哀傷。
15 Za ku bar sunanku ga zaɓaɓɓuna yă zama abin la’antarwa; Ubangiji Mai Iko Duka zai kashe ku, amma ga bayina zai ba su wani suna.
你們將留下你們的名給我的選民作咒詞:『吾主上主將如此叫你死!』但是我的僕人要有另一個名字作稱呼。」
16 Duk wanda zai roƙi albarka a cikin ƙasar zai yi haka da gaskiyar Allah; wanda zai yi rantsuwa a cikin ƙasar zai rantse da gaskiyar Allah. Gama za a manta da wahalolin baya a kuma ɓoye su daga idanuna.
所以那在地上為自己求福的,要向真實的天主求福;那在地上起誓的,要指著真實的天主起誓,因為先前的苦難都已忘記,從我的眼前隱匿了。
17 “Ga shi, na halicci sabuwar sama da kuma sabuwar duniya. Abubuwa na dā za a manta da su, ba kuwa za a ƙara tuna da su ba.
因為,看,我要創造新天新地,先前的不再被記憶,不再被關心。
18 Amma ku yi murna ku kuma yi farin ciki har abada a abin da na halitta, gama zan halicci Urushalima ta zama abin murna mutanenta kuwa abin farin ciki.
人們都要因我所造的而永遠喜悅快樂;因為,看,我要造一座令人喜悅的耶路撒冷,一個令人歡樂的百姓。
19 Zan yi farin ciki a kan Urushalima in kuma yi murna saboda mutanena; a can ba za a ƙara jin karar makoki da na kuka ba.
我要因耶路撒冷而喜悅,因我的百姓而歡欣,其中再聽不到哭泣和哀號的聲音。
20 “A cikinta ba za a ƙara jin jariri ya rayu na’yan kwanaki kawai ba, ko kuwa wani tsohon da bai cika kwanakinsa ba; duk wanda ya mutu yana da shekaru ɗari za a ce ya mutu a kurciya ne kawai; duk wanda bai kai ɗari ba za a ɗauka la’antacce ne.
那裏再沒有夭折的嬰兒和不滿壽數的老人;百歲死去的人算是青年,凡活不到百歲的人算是被詛咒的。
21 Za su gina gidaje su kuma zauna a cikinsu; za su yi shuki a gonakin inabi su kuma ci’ya’yansu.
他們要建築房舍,自居其中;種植葡萄,自食其果;
22 Ba za su ƙara gina gidaje waɗansu kuma su zauna a cikinsu ba, ko su yi shuki waɗansu kuma su ci ba. Gama kamar yadda kwanakin itace suke, haka kwanakin mutanena za su kasance; zaɓaɓɓuna za su daɗe suna jin daɗin ayyukan hannuwansu.
並不是他們建築而別人來住,他們種植而別人來吃,因為我百姓的壽數有如樹木的年數,我的選民要享用她自己的勞作。
23 Ba za su yi wahala a banza ba ko su haifi’ya’yan da aka ƙaddara da rashin sa’a; gama za su zama mutanen da Ubangiji ya yi wa albarka, su da zuriyarsu tare da su.
他們不再徒然勤勞,生子不再受驚,因為他們是上主祝福的苗裔,他們的子孫亦將如此。
24 Kafin su yi kira zan amsa; yayinda suke cikin magana zan ji.
那時,他們還未呼求,我已答應了;他們還在祈禱,我已俯允了。
25 Kyarketai da’yan raguna za su ci abinci tare, zaki kuma zai ci buɗu kamar yadda shanu suke yi, amma ƙura ce za tă zama abincin maciji. Ba za su ƙara cuci ko su yi ɓarna a kan dukan dutsena mai tsarki ba,” in ji Ubangiji.
豺狼和羔羊將要一齊牧放,獅子要如牛犢一般吃草,塵土將是大蛇的食物;在我的整個聖山上,再沒有誰作惡,也沒有誰害人:上主說。