< Ishaya 64 >
1 Da ma za ka tsage sammai ka sauko, ai, da duwatsu za su yi rawar jiki a gabanka!
Oh, da bi pretrgal nebo, da bi prišel dol, da bi gore lahko tekle ob tvoji prisotnosti,
2 Kamar sa’ad da wuta takan ci rassa ta sa ruwa ya tafasa, ka sauko ka sanar da sunanka ga abokan gābanka ka kuma sa al’ummai su yi rawan jiki a gabanka!
kakor ko topilni ogenj žge, ogenj povzroča vodam, da vrejo, da tvoje ime naredi znano tvojim nasprotnikom, da bodo narodi lahko trepetali ob tvoji prisotnosti!
3 Gama sa’ad da ka aikata abubuwan bantsoron da ba mu sa tsammani ba, ka sauko, duwatsu kuma suka yi rawar jiki a gabanka.
Ko si delal strašne stvari, ki jih nismo pričakovali, si prišel dol, gore so tekle ob tvoji prisotnosti.
4 Tun fil azal babu wanda ya taɓa ji, babu kunnen da ya gane, babu idon da ya ga wani Allah in ban da kai, wanda ya aikata waɗannan al’amura a madadin waɗanda suke sa zuciya a gare shi.
Kajti od začetka sveta ljudje niso slišali niti z ušesom zaznali niti ni oko videlo, oh Bog, razen tebe, kaj je on pripravil za tistega, ki čaka nanj.
5 Kakan taimaki waɗanda suke murnan yin abin da yake daidai, waɗanda sukan tuna da hanyoyinka. Amma sa’ad da muka ci gaba da yin zunubi, kakan yi fushi. Ta yaya za mu sami ceto ke nan?
Ti srečaš tistega, ki se razveseljuje in dela pravično, tiste, ki se te spominjajo na tvojih poteh. Glej, besen si, kajti mi smo grešili. V tistih je vztrajanje in mi bomo rešeni.
6 Dukanmu mun zama kamar wanda yake marar tsabta, kuma dukan ayyukanmu masu adalci sun zama kamar ƙazaman tsummoki; duk mun zama kamar busasshen ganye, kamar iska haka zunubanmu sukan share mu.
Toda mi vsi smo kakor nečista stvar in vse naše pravičnosti so kakor umazane cunje in mi vsi venemo kakor list in naše krivičnosti so nas kakor veter odnesle proč.
7 Babu wanda yake kira bisa sunanka ko ya yi ƙoƙarin riƙe ka; gama ka ɓoye fuskarka daga gare mu ka kuma sa muka lalace saboda zunubanmu.
Nikogar ni, ki kliče k tvojemu imenu, ki se razvnema, da bi se te oprijel. Kajti svoj obraz si skril pred nami in nas použil zaradi naših krivičnosti.
8 Duk da haka, Ubangiji, kai ne Ubanmu. Mu yumɓu ne, kai kuma mai ginin tukwane; dukanmu aikin hannunka ne.
Toda sedaj, oh Gospod, si ti naš oče. Mi smo ilo in ti naš lončar in mi vsi smo delo tvojih rok.
9 Kada ka yi fushi fiye da kima, ya Ubangiji; kada ka tuna da zunubanmu har abada. Da ma ka dube mu, muna roƙonka, gama dukanmu mutanenka ne.
Ne bodi zelo boleče ogorčen, oh Gospod niti se ne spominjaj krivičnosti na veke. Glej, preišči, rotimo te, mi vsi smo tvoje ljudstvo.
10 Biranenka masu tsarki sun zama hamada; har Sihiyona ma ta zama hamada; Urushalima ta zama kango.
Tvoja sveta mesta so divjina, Sion je divjina, Jeruzalem opustošenje.
11 Haikalinmu mai tsarki da kuma mai daraja, inda kakanninmu suka yabe ka, an ƙone da wuta, kuma dukan abubuwan da muke ƙauna sun lalace.
Naša sveta in naša krasna hiša, kjer so te naši očetje hvalili, je požgana z ognjem in vse naše prijetne stvari so opustošene.
12 Bayan dukan wannan, ya Ubangiji, ba za ka yi wani abu ba? Za ka yi shiru ka hore mu fiye da kima?
Mar se boš zadrževal zaradi teh stvari, oh Gospod? Mar boš molčal in nas zelo boleče prizadel?