< Ishaya 64 >

1 Da ma za ka tsage sammai ka sauko, ai, da duwatsu za su yi rawar jiki a gabanka!
Oh que você rasgaria os céus, que você desceria, que as montanhas podem tremer com sua presença.
2 Kamar sa’ad da wuta takan ci rassa ta sa ruwa ya tafasa, ka sauko ka sanar da sunanka ga abokan gābanka ka kuma sa al’ummai su yi rawan jiki a gabanka!
como quando o fogo acende a lenha, e o fogo faz com que a água ferva. Dê a conhecer seu nome a seus adversários, que as nações possam tremer com sua presença!
3 Gama sa’ad da ka aikata abubuwan bantsoron da ba mu sa tsammani ba, ka sauko, duwatsu kuma suka yi rawar jiki a gabanka.
Quando você fez coisas incríveis que nós não procuramos, você desceu, e as montanhas tremeram com sua presença.
4 Tun fil azal babu wanda ya taɓa ji, babu kunnen da ya gane, babu idon da ya ga wani Allah in ban da kai, wanda ya aikata waɗannan al’amura a madadin waɗanda suke sa zuciya a gare shi.
Pois de homens velhos não ouviram falar, nem percebido pelo ouvido, nem o olho viu um Deus além de você, que trabalha para aquele que espera por ele.
5 Kakan taimaki waɗanda suke murnan yin abin da yake daidai, waɗanda sukan tuna da hanyoyinka. Amma sa’ad da muka ci gaba da yin zunubi, kakan yi fushi. Ta yaya za mu sami ceto ke nan?
Você encontra aquele que se alegra e faz a justiça, aqueles que se lembram de você em seus caminhos. Eis que você estava com raiva, e nós pecamos. Estamos em pecado há muito tempo. Devemos ser salvos?
6 Dukanmu mun zama kamar wanda yake marar tsabta, kuma dukan ayyukanmu masu adalci sun zama kamar ƙazaman tsummoki; duk mun zama kamar busasshen ganye, kamar iska haka zunubanmu sukan share mu.
Pois todos nós nos tornamos como alguém que está impuro, e toda nossa retidão é como uma peça de vestuário poluída. Todos nós desbotamos como uma folha; e nossas iniqüidades, como o vento, nos levam embora.
7 Babu wanda yake kira bisa sunanka ko ya yi ƙoƙarin riƙe ka; gama ka ɓoye fuskarka daga gare mu ka kuma sa muka lalace saboda zunubanmu.
Não há ninguém que invoque seu nome, que se agita para se apoderar de você; pois você escondeu seu rosto de nós, e nos consumiram por meio de nossas iniqüidades.
8 Duk da haka, Ubangiji, kai ne Ubanmu. Mu yumɓu ne, kai kuma mai ginin tukwane; dukanmu aikin hannunka ne.
Mas agora, Yahweh, você é nosso Pai. Nós somos o barro e você nosso oleiro. Todos nós somos o trabalho de sua mão.
9 Kada ka yi fushi fiye da kima, ya Ubangiji; kada ka tuna da zunubanmu har abada. Da ma ka dube mu, muna roƙonka, gama dukanmu mutanenka ne.
Don não fique furioso, Yahweh. Não se lembre da iniqüidade para sempre. Olhe e veja, nós lhe imploramos, somos todos seu povo.
10 Biranenka masu tsarki sun zama hamada; har Sihiyona ma ta zama hamada; Urushalima ta zama kango.
Suas cidades sagradas se tornaram uma região selvagem. Zion se tornou uma região selvagem, Jerusalém, uma desolação.
11 Haikalinmu mai tsarki da kuma mai daraja, inda kakanninmu suka yabe ka, an ƙone da wuta, kuma dukan abubuwan da muke ƙauna sun lalace.
Nossa santa e nossa bela casa onde nossos pais o elogiaram é queimado com fogo. Todos os nossos lugares agradáveis são resíduos.
12 Bayan dukan wannan, ya Ubangiji, ba za ka yi wani abu ba? Za ka yi shiru ka hore mu fiye da kima?
Will, você se retrai por estas coisas, Yahweh? Você vai ficar calado e nos castigar muito severamente?

< Ishaya 64 >