< Ishaya 64 >

1 Da ma za ka tsage sammai ka sauko, ai, da duwatsu za su yi rawar jiki a gabanka!
if you tore [the] heavens you came down from before you mountains they shook.
2 Kamar sa’ad da wuta takan ci rassa ta sa ruwa ya tafasa, ka sauko ka sanar da sunanka ga abokan gābanka ka kuma sa al’ummai su yi rawan jiki a gabanka!
As kindles fire brushwood water it boils fire to make known name your to opponents your from before you nations they will quake.
3 Gama sa’ad da ka aikata abubuwan bantsoron da ba mu sa tsammani ba, ka sauko, duwatsu kuma suka yi rawar jiki a gabanka.
When doing you awesome [deeds] [which] not we were looking for you came down from before you mountains they shook.
4 Tun fil azal babu wanda ya taɓa ji, babu kunnen da ya gane, babu idon da ya ga wani Allah in ban da kai, wanda ya aikata waɗannan al’amura a madadin waɗanda suke sa zuciya a gare shi.
And from long ago not people have heard not people have given ear eye not it has seen a God besides you [who] he acts for [one who] waits for him.
5 Kakan taimaki waɗanda suke murnan yin abin da yake daidai, waɗanda sukan tuna da hanyoyinka. Amma sa’ad da muka ci gaba da yin zunubi, kakan yi fushi. Ta yaya za mu sami ceto ke nan?
You meet [one who] rejoices and [one who] does righteousness in ways your they remember you there! you you were angry and we sinned in them long duration so we may be saved?
6 Dukanmu mun zama kamar wanda yake marar tsabta, kuma dukan ayyukanmu masu adalci sun zama kamar ƙazaman tsummoki; duk mun zama kamar busasshen ganye, kamar iska haka zunubanmu sukan share mu.
And we have become like unclean [person] all of us and [are] like a garment of menstruation all righteousness our and we have withered like leafage all of us and iniquities our like the wind they carry off us.
7 Babu wanda yake kira bisa sunanka ko ya yi ƙoƙarin riƙe ka; gama ka ɓoye fuskarka daga gare mu ka kuma sa muka lalace saboda zunubanmu.
And there not [is one who] calls on name your [one who] rouses himself to take hold on you for you have hidden face your from us and you have melted us in [the] hand of iniquity our.
8 Duk da haka, Ubangiji, kai ne Ubanmu. Mu yumɓu ne, kai kuma mai ginin tukwane; dukanmu aikin hannunka ne.
And now O Yahweh [are] father our you we [are] the clay and you [are] [the] [one who] formed us and [are] [the] work of hand your all of us.
9 Kada ka yi fushi fiye da kima, ya Ubangiji; kada ka tuna da zunubanmu har abada. Da ma ka dube mu, muna roƙonka, gama dukanmu mutanenka ne.
May not you be angry O Yahweh up to muchness and may not for ever you remember iniquity here! look please [are] people your all of us.
10 Biranenka masu tsarki sun zama hamada; har Sihiyona ma ta zama hamada; Urushalima ta zama kango.
[the] cities of Holiness your they have been a wilderness Zion a wilderness it has been Jerusalem [is] a desolation.
11 Haikalinmu mai tsarki da kuma mai daraja, inda kakanninmu suka yabe ka, an ƙone da wuta, kuma dukan abubuwan da muke ƙauna sun lalace.
[the] house of Holiness our and splendor our where they praised you ancestors our it has become a burning of fire and all pleasant things our it has become a ruin.
12 Bayan dukan wannan, ya Ubangiji, ba za ka yi wani abu ba? Za ka yi shiru ka hore mu fiye da kima?
¿ On these [things] will you restrain yourself O Yahweh will you be silent? and will you afflict? us up to muchness.

< Ishaya 64 >