< Ishaya 64 >
1 Da ma za ka tsage sammai ka sauko, ai, da duwatsu za su yi rawar jiki a gabanka!
Oh that thou mightest rend the heavens, come down: at thy presence would mountains [then] melt away.
2 Kamar sa’ad da wuta takan ci rassa ta sa ruwa ya tafasa, ka sauko ka sanar da sunanka ga abokan gābanka ka kuma sa al’ummai su yi rawan jiki a gabanka!
As fire is kindled on brushwood, as water is made to bubble up by fire—to make thy name known to thy adversaries, that at thy presence nations might tremble!
3 Gama sa’ad da ka aikata abubuwan bantsoron da ba mu sa tsammani ba, ka sauko, duwatsu kuma suka yi rawar jiki a gabanka.
[As] when thou didst fearful deeds which we had not looked for, thou camest down, [while] at thy presence mountains melted away;
4 Tun fil azal babu wanda ya taɓa ji, babu kunnen da ya gane, babu idon da ya ga wani Allah in ban da kai, wanda ya aikata waɗannan al’amura a madadin waɗanda suke sa zuciya a gare shi.
Yea! what from the beginning of the world men had not heard, not perceived by their hearing; no eye [also] had seen a god beside thee, who could do [the like] for the one that waiteth for him.
5 Kakan taimaki waɗanda suke murnan yin abin da yake daidai, waɗanda sukan tuna da hanyoyinka. Amma sa’ad da muka ci gaba da yin zunubi, kakan yi fushi. Ta yaya za mu sami ceto ke nan?
Thou acceptest him that rejoiceth and worketh righteousness, those that remember thee in thy ways: behold, thou wast wroth, for we had sinned on them continually; and can we thus be saved?
6 Dukanmu mun zama kamar wanda yake marar tsabta, kuma dukan ayyukanmu masu adalci sun zama kamar ƙazaman tsummoki; duk mun zama kamar busasshen ganye, kamar iska haka zunubanmu sukan share mu.
And we are become like an unclean man all of us, and like a soiled garment, all our righteousness; and we wither like a leaf all of us; and our iniquities, like the wind, will bear us away.
7 Babu wanda yake kira bisa sunanka ko ya yi ƙoƙarin riƙe ka; gama ka ɓoye fuskarka daga gare mu ka kuma sa muka lalace saboda zunubanmu.
And there is none that calleth upon thy name, that stirreth himself up to lay hold of thee; for thou hast hidden thy face from us, and hast let us melt away, through the force of our iniquities.
8 Duk da haka, Ubangiji, kai ne Ubanmu. Mu yumɓu ne, kai kuma mai ginin tukwane; dukanmu aikin hannunka ne.
But now, O Lord, our father art thou; we are the clay, and thou our fashioner; and the work of thy hand are we all.
9 Kada ka yi fushi fiye da kima, ya Ubangiji; kada ka tuna da zunubanmu har abada. Da ma ka dube mu, muna roƙonka, gama dukanmu mutanenka ne.
Be not wroth, O Lord, so very greatly, and do not for ever remember [our] iniquity: behold, look, we beseech thee, thy people are we all.
10 Biranenka masu tsarki sun zama hamada; har Sihiyona ma ta zama hamada; Urushalima ta zama kango.
Thy holy cities are become a wilderness, Zion is become a wilderness, Jerusalem, a desolate place.
11 Haikalinmu mai tsarki da kuma mai daraja, inda kakanninmu suka yabe ka, an ƙone da wuta, kuma dukan abubuwan da muke ƙauna sun lalace.
Our holy and beautiful house where our fathers praised thee, is burnt up with fire; and all our costly things are become ruins.
12 Bayan dukan wannan, ya Ubangiji, ba za ka yi wani abu ba? Za ka yi shiru ka hore mu fiye da kima?
Wilt thou for these things refrain thyself, O Lord? wilt thou be silent, and afflict us so very greatly?