< Ishaya 63 >

1 Wane ne wannan mai zuwa daga Edom, daga Bozra, saye da jajjayen rigunarsa? Wane ne wannan, sanye cikin daraja, tafe cikin girmar ƙarfinsa? “Ni ne, mai magana cikin adalci, mai ikon ceto.”
Ko je ono što ide iz Edoma, iz Vosora, u crvenijem haljinama? krasno odjeven, koraèajuæi u velièini sile svoje? Ja sam, koji govorim pravdu i vrijedan sam spasti.
2 Me ya sa rigunanka suka yi ja, sai ka ce na wanda yake tattaka’ya’yan inabi?
Zašto ti je crveno odijelo i haljine ti kao u onoga koji gazi u kaci?
3 “Na tattake’ya’yan inabi ni kaɗai; cikin al’ummai kuma babu wani tare da ni. Na tattake su cikin fushina Na matse su cikin hasalata; jininsu ya fantsamar wa rigunana, na kuma ɓata dukan tufafina.
Gazih sam u kaci, i niko izmeðu naroda ne bješe sa mnom; ali ih izgazih u gnjevu svom i potlaèih u ljutini svojoj; i krv njihova poprska mi haljine i iskaljah sve odijelo svoje.
4 Gama ranar ɗaukan fansa tana a cikin zuciyata, kuma shekarar fansata ta zo.
Jer je dan od osvete u srcu mom, i doðe godina da se moji iskupe.
5 Na duba, amma babu wanda zai taimaka, na yi mamaki cewa ba wanda ya goyi baya; saboda haka hannuna ya yi mini ceto, fushina kuma ya rayar da ni.
Pogledah, a nikoga ne bješe da pomože, i zaèudih se što nikoga ne bješe da podupre; ali me desnica moja izbavi i jarost moja poduprije me.
6 Na tattake al’ummai cikin fushina; cikin hasalata kuma na sa sun bugu na kuma zub da jininsu a ƙasa.”
I izgazih narode u gnjevu svom, i opojih ih jarošæu svojom, i prolih na zemlju krv njihovu.
7 Zan ba da labarin alherin Ubangiji, ayyukan da suka sa a yabe shi, bisa ga dukan abubuwan da Ubangiji ya yi mana, I, ayyuka masu kyan da ya yi domin gidan Isra’ila, bisa ga jinƙansa da yawan alheransa.
Pominjaæu dobrotu Gospodnju, hvalu Gospodnju za sve što nam je uèinio Gospod, i mnoštvo dobra što je uèinio domu Izrailjevu po milosti svojoj i po velikoj dobroti svojoj.
8 Ya ce, “Babu shakka su mutanena ne,’ya’ya maza waɗanda ba za su ruɗe ni ba”; ta haka ya zama Mai Cetonsu.
Jer reèe: doista su moj narod, sinovi, koji neæe iznevjeriti. I bi im spasitelj.
9 Cikin dukan damuwarsu shi ma ya damu, mala’ikan da yake gabansa ya cece su. Cikin ƙauna da jinƙai ya fanshe su; ya kuma ɗaga su ya riƙe su dukan kwanakin dā
U svakoj tuzi njihovoj on bješe tužan, i anðeo, koji je pred njim, spase ih. Ljubavi svoje radi i milosti svoje radi on ih izbavi, i podiže ih i nosi ih sve vrijeme.
10 Duk da haka suka yi tawaye suka ɓata wa Ruhu Mai Tsarki rai. Saboda haka ya juya ya kuma zama abokin gābansu shi kansa kuma ya yaƙe su.
Ali se odmetaše i žalostiše sveti duh njegov; zato im posta neprijatelj, i ratova na njih.
11 Sa’an nan mutanensa suka tuna kwanakin dā, kwanakin Musa da mutanensa, ina yake shi wanda ya fitar da su ta teku, da makiyayan garkensa? Ina shi yake wanda ya sa Ruhunsa Mai Tsarki a cikinsu,
Ali se opomenu starijeh vremena, Mojsija, naroda svojega: gdje je onaj koji ih izvede iz mora s pastirem stada svojega? gdje je onaj što metnu usred njih sveti duh svoj?
12 wanda ya aika hannu ɗaukakarsa mai iko ya kasance a hannun dama na Musa, wanda ya raba ruwaye a gabansu, don yă sami wa kansa madawwamin suna,
Koji ih vodi slavnom mišicom svojom za desnicu Mojsijevu? koji razdvoji vodu pred njima, da steèe sebi vjeèno ime?
13 wanda ya bishe su cikin zurfafa? Kamar doki a fili, ba su yi tuntuɓe ba;
Koji ih vodi preko bezdana kao konja preko pustinje, da se ne spotakoše?
14 kamar shanun da suke gangarawa zuwa kwari, haka Ruhun Ubangiji ya ba su hutu. Ga yadda ka bishe mutanenka don ka ba wa kanka suna mai ɗaukaka.
Duh Gospodnji vodi ih tiho, kao kad stoka slazi u dolinu; tako si vodio svoj narod da steèeš sebi slavno ime.
15 Ka duba daga sama ka gani daga kursiyinka da yake bisa, mai tsarki da kuma mai ɗaukaka. Ina kishinka da kuma ikonka? Ka janye juyayi da kuma tausayin da kake yi mana daga gare mu.
Pogledaj s neba, i vidi iz stana svetinje svoje i slave svoje, gdje je revnost tvoja i sila tvoja, mnoštvo milosrða tvojega i milosti tvoje? eda li æe se meni ustegnuti?
16 Amma kai Ubanmu ne, ko Ibrahim bai san mu ba Isra’ila kuma bai yarda da mu ba; kai, ya Ubangiji, kai ne Ubanmu, Mai Fansarmu tun fil azal ne sunanka.
Ti si zaista otac naš, ako i ne zna Avram za nas, i Izrailj nas ne poznaje; ti si, Gospode, otac naš, ime ti je otkako je vijeka izbavitelj naš.
17 Don me, ya Ubangiji, ka sa muna barin hanyoyinka muka kuma taurare zukatanmu don kada mu girmama ka? Ka komo domin darajar bayinka, kabilan da suke abin gādonka.
Zašto si nam dao da zaðemo, Gospode, s putova tvojih? da nam otvrdne srce da te se ne bojimo? Vrati se radi sluga svojih, radi plemena našljedstva svojega.
18 Gama a ɗan lokaci mutanenka suka mallaki wurinka mai tsarki, amma yanzu abokan gābanmu sun tattake wurinka mai tsarki.
Za malo naslijedi narod svetosti tvoje; neprijatelji naši pogaziše svetinju tvoju.
19 Mu naka tun fil azal; ba ka taɓa yin mulki a kansu ba, ba a taɓa kira su da sunanka ba.
Postasmo kao oni kojima nijesi nigda vladao niti je prizivano ime tvoje nad njima.

< Ishaya 63 >