< Ishaya 63 >

1 Wane ne wannan mai zuwa daga Edom, daga Bozra, saye da jajjayen rigunarsa? Wane ne wannan, sanye cikin daraja, tafe cikin girmar ƙarfinsa? “Ni ne, mai magana cikin adalci, mai ikon ceto.”
این کیست که از ادوم با لباس سرخ ازبصره می‌آید؟ یعنی‌این که به لباس جلیل خود ملبس است و در کثرت قوت خویش می‌خرامد؟ من که به عدالت تکلم می‌کنم و برای نجات، زورآور می‌باشم.۱
2 Me ya sa rigunanka suka yi ja, sai ka ce na wanda yake tattaka’ya’yan inabi?
چرا لباس تو سرخ است و جامه تو مثل کسی‌که چرخشت را پایمال کند؟۲
3 “Na tattake’ya’yan inabi ni kaɗai; cikin al’ummai kuma babu wani tare da ni. Na tattake su cikin fushina Na matse su cikin hasalata; jininsu ya fantsamar wa rigunana, na kuma ɓata dukan tufafina.
من چرخشت را تنها پایمال نمودم واحدی از قوم‌ها با من نبود و ایشان را بغضب خودپایمال کردم و بحدت خشم خویش لگد کوب نمودم و خون ایشان به لباس من پاشیده شده، تمامی جامه خود را آلوده ساختم.۳
4 Gama ranar ɗaukan fansa tana a cikin zuciyata, kuma shekarar fansata ta zo.
زیرا که یوم انتقام در دل من بود و سال فدیه شدگانم رسیده بود.۴
5 Na duba, amma babu wanda zai taimaka, na yi mamaki cewa ba wanda ya goyi baya; saboda haka hannuna ya yi mini ceto, fushina kuma ya rayar da ni.
و نگریستم و اعانت کننده‌ای نبود و تعجب نمودم زیرا دستگیری نبود. لهذا بازوی من مرانجات داد و حدت خشم من مرا دستگیری نمود.۵
6 Na tattake al’ummai cikin fushina; cikin hasalata kuma na sa sun bugu na kuma zub da jininsu a ƙasa.”
و قوم‌ها را به غضب خود پایمال نموده، ایشان را از حدت خشم خویش مست ساختم. و خون ایشان را بر زمین ریختم.۶
7 Zan ba da labarin alherin Ubangiji, ayyukan da suka sa a yabe shi, bisa ga dukan abubuwan da Ubangiji ya yi mana, I, ayyuka masu kyan da ya yi domin gidan Isra’ila, bisa ga jinƙansa da yawan alheransa.
احسانهای خداوند و تسبیحات خداوند راذکر خواهم نمود برحسب هر‌آنچه خداوند برای ما عمل نموده است و به موجب کثرت احسانی که برای خاندان اسرائیل موافق رحمت‌ها و وفوررافت خود بجا آورده است.۷
8 Ya ce, “Babu shakka su mutanena ne,’ya’ya maza waɗanda ba za su ruɗe ni ba”; ta haka ya zama Mai Cetonsu.
زیرا گفته است: ایشان قوم من و پسرانی که خیانت نخواهند کردمی باشند، پس نجات‌دهنده ایشان شده است.۸
9 Cikin dukan damuwarsu shi ma ya damu, mala’ikan da yake gabansa ya cece su. Cikin ƙauna da jinƙai ya fanshe su; ya kuma ɗaga su ya riƙe su dukan kwanakin dā
او در همه تنگیهای ایشان به تنگ آورده شد وفرشته حضور وی ایشان را نجات داد. در محبت و حلم خود ایشان را فدیه داد و در جمیع ایام قدیم، متحمل ایشان شده، ایشان را برداشت.۹
10 Duk da haka suka yi tawaye suka ɓata wa Ruhu Mai Tsarki rai. Saboda haka ya juya ya kuma zama abokin gābansu shi kansa kuma ya yaƙe su.
اما ایشان عاصی شده، روح قدوس او رامحزون ساختند، پس برگشته، دشمن ایشان شد واو خود با ایشان جنگ نمود.۱۰
11 Sa’an nan mutanensa suka tuna kwanakin dā, kwanakin Musa da mutanensa, ina yake shi wanda ya fitar da su ta teku, da makiyayan garkensa? Ina shi yake wanda ya sa Ruhunsa Mai Tsarki a cikinsu,
آنگاه ایام قدیم و موسی و قوم خویش رابیاد آورد (و گفت ) کجاست آنکه ایشان را با شبان گله خود از دریا برآورد و کجا است آنکه روح قدوس خود را در میان ایشان نهاد؟۱۱
12 wanda ya aika hannu ɗaukakarsa mai iko ya kasance a hannun dama na Musa, wanda ya raba ruwaye a gabansu, don yă sami wa kansa madawwamin suna,
که بازوی جلیل خود را به‌دست راست موسی خرامان ساخت و آبها را پیش روی ایشان منشق گردانیدتا اسم جاودانی برای خویش پیدا کند؟۱۲
13 wanda ya bishe su cikin zurfafa? Kamar doki a fili, ba su yi tuntuɓe ba;
آنکه ایشان را در لجه‌ها مثل اسب در بیابان رهبری نمود که لغزش نخورند.۱۳
14 kamar shanun da suke gangarawa zuwa kwari, haka Ruhun Ubangiji ya ba su hutu. Ga yadda ka bishe mutanenka don ka ba wa kanka suna mai ɗaukaka.
مثل بهایمی که به وادی فرود می‌روند روح خداوند ایشان را آرامی بخشید. هم چنان قوم خود را رهبری نمودی تابرای خود اسم مجید پیدا نمایی.۱۴
15 Ka duba daga sama ka gani daga kursiyinka da yake bisa, mai tsarki da kuma mai ɗaukaka. Ina kishinka da kuma ikonka? Ka janye juyayi da kuma tausayin da kake yi mana daga gare mu.
از آسمان بنگر و از مسکن قدوسیت وجلال خویش نظر افکن. غیرت جبروت تو کجااست؟ جوشش دل و رحمت های تو که به من نمودی بازداشته شده است.۱۵
16 Amma kai Ubanmu ne, ko Ibrahim bai san mu ba Isra’ila kuma bai yarda da mu ba; kai, ya Ubangiji, kai ne Ubanmu, Mai Fansarmu tun fil azal ne sunanka.
به درستی که توپدر ما هستی اگر‌چه ابراهیم ما را نشناسد واسرائیل ما را بجا نیاورد، اما تو‌ای یهوه، پدر ما وولی ما هستی و نام تو از ازل می‌باشد.۱۶
17 Don me, ya Ubangiji, ka sa muna barin hanyoyinka muka kuma taurare zukatanmu don kada mu girmama ka? Ka komo domin darajar bayinka, kabilan da suke abin gādonka.
پس‌ای خداوند ما را از طریق های خود چرا گمراه ساختی و دلهای ما را سخت گردانیدی تا از تونترسیم. به‌خاطر بندگانت و اسباط میراث خودرجعت نما.۱۷
18 Gama a ɗan lokaci mutanenka suka mallaki wurinka mai tsarki, amma yanzu abokan gābanmu sun tattake wurinka mai tsarki.
قوم مقدس تو اندک زمانی آن رامتصرف بودند و دشمنان ما مکان قدس تو راپایمال نمودند.۱۸
19 Mu naka tun fil azal; ba ka taɓa yin mulki a kansu ba, ba a taɓa kira su da sunanka ba.
و ما مثل کسانی که تو هرگز برایشان حکمرانی نکرده باشی و به نام تو نامیده نشده باشند گردیده‌ایم.۱۹

< Ishaya 63 >