< Ishaya 63 >

1 Wane ne wannan mai zuwa daga Edom, daga Bozra, saye da jajjayen rigunarsa? Wane ne wannan, sanye cikin daraja, tafe cikin girmar ƙarfinsa? “Ni ne, mai magana cikin adalci, mai ikon ceto.”
Quel est celui qui vient d’Edom, de Bosra, les vêtements teints? il est beau dans sa robe, il marche dans la grandeur de sa puissance. C’est moi qui parle justice, et qui combats pour sauver.
2 Me ya sa rigunanka suka yi ja, sai ka ce na wanda yake tattaka’ya’yan inabi?
Pourquoi donc rouge est votre robe, et vos vêtements comme les vêtements de ceux qui foulent dans un pressoir?
3 “Na tattake’ya’yan inabi ni kaɗai; cikin al’ummai kuma babu wani tare da ni. Na tattake su cikin fushina Na matse su cikin hasalata; jininsu ya fantsamar wa rigunana, na kuma ɓata dukan tufafina.
J’ai foulé le pressoir tout seul, et d’entre les nations il n’y a pas un homme avec moi; je les ai foulés aux pieds dans ma fureur, et je les ai foulés aux pieds dans ma colère; leur sang s’est répandu sur mes vêtements, il a souillé tous mes habits.
4 Gama ranar ɗaukan fansa tana a cikin zuciyata, kuma shekarar fansata ta zo.
Car le jour de la vengeance est dans mon cœur, l’année de ma rédemption est venue.
5 Na duba, amma babu wanda zai taimaka, na yi mamaki cewa ba wanda ya goyi baya; saboda haka hannuna ya yi mini ceto, fushina kuma ya rayar da ni.
J’ai regardé autour de moi, et il n’y avait pas d’auxiliaire; j’ai cherché, et il n’y a eu personne qui m’aidât; ainsi mon bras m’a sauvé, et mon indignation elle-même m’a secouru.
6 Na tattake al’ummai cikin fushina; cikin hasalata kuma na sa sun bugu na kuma zub da jininsu a ƙasa.”
Et j’ai foulé aux pieds les peuples dans ma fureur, je les ai enivrés de mon indignation, et j’ai renversé par terre leur force.
7 Zan ba da labarin alherin Ubangiji, ayyukan da suka sa a yabe shi, bisa ga dukan abubuwan da Ubangiji ya yi mana, I, ayyuka masu kyan da ya yi domin gidan Isra’ila, bisa ga jinƙansa da yawan alheransa.
Je me souviendrai des miséricordes du Seigneur, je chanterai louange du Seigneur, à cause de tout ce qu’il a fait pour nous, et à cause de la multitude des biens accordés à la maison d’Israël, et qu’il leur a prodigués selon sa bonté et selon la multitude de ses miséricordes.
8 Ya ce, “Babu shakka su mutanena ne,’ya’ya maza waɗanda ba za su ruɗe ni ba”; ta haka ya zama Mai Cetonsu.
Et il a dit: Mais pourtant c’est mon peuple; ce sont des fils qui ne renoncent pas leur père; et il est devenu pour eux un sauveur.
9 Cikin dukan damuwarsu shi ma ya damu, mala’ikan da yake gabansa ya cece su. Cikin ƙauna da jinƙai ya fanshe su; ya kuma ɗaga su ya riƙe su dukan kwanakin dā
Dans toute leur tribulation il n’a pas été tourmenté, car l’ange de sa face les a sauvés; dans son amour et dans sa bonté il les a lui-même rachetés; il les a portés, il les a élevés dans tous les jours des siècles passés.
10 Duk da haka suka yi tawaye suka ɓata wa Ruhu Mai Tsarki rai. Saboda haka ya juya ya kuma zama abokin gābansu shi kansa kuma ya yaƙe su.
Mais eux-mêmes l’ont provoqué au courroux, ils ont affligé l’esprit de son saint; il est devenu pour eux un ennemi, et il les a lui-même complètement défaits.
11 Sa’an nan mutanensa suka tuna kwanakin dā, kwanakin Musa da mutanensa, ina yake shi wanda ya fitar da su ta teku, da makiyayan garkensa? Ina shi yake wanda ya sa Ruhunsa Mai Tsarki a cikinsu,
Et il s’est souvenu des jours du siècle de Moïse et de son peuple: Où est celui qui les a retirés de la mer avec les pasteurs de son troupeau? où est celui qui a mis au milieu de lui l’esprit de son saint;
12 wanda ya aika hannu ɗaukakarsa mai iko ya kasance a hannun dama na Musa, wanda ya raba ruwaye a gabansu, don yă sami wa kansa madawwamin suna,
Qui a conduit à droite Moïse par le bras de sa majesté, qui a divisé les eaux devant eux, afin de se faire un nom éternel;
13 wanda ya bishe su cikin zurfafa? Kamar doki a fili, ba su yi tuntuɓe ba;
Qui les a conduits à travers les abîmes, comme le cheval qui dans le désert ne se heurte pas?
14 kamar shanun da suke gangarawa zuwa kwari, haka Ruhun Ubangiji ya ba su hutu. Ga yadda ka bishe mutanenka don ka ba wa kanka suna mai ɗaukaka.
Comme l’animal qui descend dans la campagne, l’esprit du Seigneur a été son guide; ainsi vous avez conduit votre peuple, afin de vous faire un nom glorieux.
15 Ka duba daga sama ka gani daga kursiyinka da yake bisa, mai tsarki da kuma mai ɗaukaka. Ina kishinka da kuma ikonka? Ka janye juyayi da kuma tausayin da kake yi mana daga gare mu.
Soyez attentifs du haut du ciel, et voyez de l’habitacle de votre sainteté et de votre gloire: où est votre zélé et votre puissance, la multitude de vos entrailles et de vos miséricordes? elles se sont resserrées à mon égard.
16 Amma kai Ubanmu ne, ko Ibrahim bai san mu ba Isra’ila kuma bai yarda da mu ba; kai, ya Ubangiji, kai ne Ubanmu, Mai Fansarmu tun fil azal ne sunanka.
Car vous êtes notre père; Abraham ne nous a pas connus, et Israël nous a ignorés; vous. Seigneur, êtes notre père; notre rédempteur, dès les temps anciens, est votre nom.
17 Don me, ya Ubangiji, ka sa muna barin hanyoyinka muka kuma taurare zukatanmu don kada mu girmama ka? Ka komo domin darajar bayinka, kabilan da suke abin gādonka.
Seigneur, pourquoi nous avez-vous laissés errer loin de vos voies, et avez-vous laissé endurcir nos cœurs jusqu’à ne plus vous craindre? revenez à cause de vos serviteurs, tribus de votre héritage.
18 Gama a ɗan lokaci mutanenka suka mallaki wurinka mai tsarki, amma yanzu abokan gābanmu sun tattake wurinka mai tsarki.
Comme un rien ils ont possédé votre peuple saint, nos ennemis; ils ont foulé aux pieds votre sanctification.
19 Mu naka tun fil azal; ba ka taɓa yin mulki a kansu ba, ba a taɓa kira su da sunanka ba.
Nous sommes devenus comme dans le principe, lorsque vous ne dominiez pas sur nous, et que votre nom n’était pas invoqué sur nous.

< Ishaya 63 >